< Salme 27 >

1 Af David. Herren er mit Lys og min Frelse, for hvem skal jeg frygte? Herren er mit Livs Værn, for hvem skal jeg ræddes?
Ta Dawuda. Ubangiji ne haskena da cetona, wa zan ji tsoro? Ubangiji ne mafakar raina, wane ne zan ji tsoro?
2 Der de onde kom frem imod mig for at æde mit Kød, mine Modstandere og mine Fjender, da snublede de og faldt.
Sa’ad da mugaye suka tasar mini don su cinye ni, sa’ad da abokan gābana da maƙiyina suka kawo mini hari, sun yi tuntuɓe suka fāɗi.
3 Dersom en Hær vilde lejre sig imod mig, da skal mit Hjerte ikke frygte; dersom en Krig rejses imod mig, da er jeg dog trøstig.
Ko da yake mayaƙa sun kewaye ni, zuciyata ba za tă ji tsoro ba; ko da yake ya ɓarke a kaina, duk da haka zan ƙarfafa.
4 Een Ting har jeg begæret af Herren, den vil jeg søge efter; at jeg maa bo i Herrens Hus alle mine Livsdage for at beskue Herrens Livsalighed og at grunde i hans Tempel.
Abu guda na roƙi Ubangiji, wannan shi ne na nema, cewa in zauna a gidan Ubangiji dukan kwanakin raina, in dubi kyan Ubangiji in kuma neme shi a cikin haikalinsa.
5 Thi han skal gemme mig i sin Hytte paa den onde Dag; han skal skjule mig i sit Pauluns Skjul, han skal ophøje mig paa en Klippe.
Gama a lokacin wahala, zai kiyaye ni lafiya a wurin zamansa; zai ɓoye ni cikin inuwar tabanakul nasa ya kuma sa ni can a bisa dutse.
6 Og nu hæver mit Hoved sig over mine Fjender, som ere trindt omkring mig, og jeg vil ofre ham Ofre med Frydeklang i hans Paulun; jeg vil synge og lege for Herren.
Sa’an nan kaina zai ɗaukaka a bisa abokan gābana waɗanda suka kewaye ni; a tabanakul nasa zan miƙa hadaya da sowa ta farin ciki; zan rera in kuma yi kiɗi ga Ubangiji.
7 Herre! hør min Røst, naar jeg raaber, og vær mig naadig og bønhør mig!
Ka ji muryata sa’ad da na yi kira, ya Ubangiji; ka yi mini jinƙai ka kuma amsa mini.
8 Til dig sagde mit Hjerte, der du sagde: „Søger mit Ansigt”, jeg søger dit Ansigt, Herre!
Zuciyata kan faɗa game da kai, “Nemi fuskarsa!” Fuskarka, Ubangiji, zan nema.
9 Skjul ikke dit Ansigt for mig, forskyd ikke din Tjener i Vrede; du har været min Hjælp, opgiv mig ikke og forlad mig ikke, min Frelses Gud!
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni, kada ka kore bawanka daga gare ka cikin fushi; kai ne ka kasance mai taimakona. Kada ka ƙi ni ko ka yashe ni, Ya Allah Mai cetona.
10 Thi min Fader og min Moder forlode mig; men Herren tager mig op.
Ko da mahaifina da mahaifiyata sun yashe ni, Ubangiji zai karɓe ni.
11 Herre! lær mig din Vej og led mig paa den jævne Sti, for mine Fjenders Skyld.
Ka koya mini hanyarka, ya Ubangiji; ka bi da ni a miƙaƙƙiyar hanya saboda masu danne ni.
12 Giv mig ikke i mine Fjenders Vold; thi falske Vidner og de, som aande Uretfærdighed, opstode imod mig.
Kada ka ba da ni da sha’awar maƙiyina, gama masu shaidar ƙarya sun taso a kaina, suna numfasa tashin hankali.
13 Havde jeg ikke troet, at jeg skulde se Herrens Godhed i de levendes Land —!
Har yanzu ina da ƙarfin gwiwa a wannan cewa zan ga alherin Ubangiji; a ƙasar masu rai.
14 Bi efter Herren, vær frimodig, og han skal styrke dit Hjerte; ja, bi efter Herren!
Ka dogara ga Ubangiji, ka yi ƙarfin hali ka yi ƙarfin zuciya ka kuma dogara ga Ubangiji.

< Salme 27 >