< Salme 25 >

1 En Psalme af David. Til dig, Herre! opløfter jeg min Sjæl.
Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
2 Jeg forlader mig paa dig, min Gud! lad mig ikke beskæmmes, at mine Fjender ikke skulle fryde sig over mig.
A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
3 Ja, ingen, som bier efter dig, skal beskæmmes; beskæmmes skulle de, som handle troløst uden Aarsag.
Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
4 Herre! lad mig kende dine Veje, lær mig dine Stier.
Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
5 Gør, at jeg gaar frem i din Sandhed, og lær mig den; thi du er min Frelses Gud, jeg bier efter dig den ganske Dag.
ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
6 Herre! kom din Barmhjertighed og din Miskundhed i Hu; thi de have været fra Evighed.
Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
7 Kom ikke mine Ungdoms Synder eller mine Overtrædelser i Hu; men kom du mig i Hu efter din Miskundhed for din Godheds Skyld, Herre!
Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
8 Herren er god og oprigtig, derfor underviser han Syndere om Vejen.
Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
9 Han skal gøre, at de ydmygede komme til Ret, og han skal lære de ydmygede sin Vej.
Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
10 Alle Herrens Stier ere Miskundhed og Sandhed for dem, som bevare hans Pagt og hans Vidnesbyrd.
Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
11 For dit Navns Skyld, Herre, forlad mig dog min Misgerning; thi den er stor.
Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
12 Hvo er den Mand, som frygter Herren? han skal undervise ham om den Vej, som han skal udvælge.
To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
13 Hans Sjæl skal bo i Lyksalighed, og hans Sæd skal arve Landet.
Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
14 Herrens Omgang er med dem, som frygte ham, og hans Pagt er med dem, til at lade dem kende den.
Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
15 Mine Øjne ere stedse til Herren; thi han skal drage mine Fødder ud af Garnet.
Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
16 Vend dit Ansigt til mig og vær mig naadig; thi jeg er enlig og elendig.
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
17 Mit Hjertes Ængstelser have vidt udbredt sig; før mig ud af mine Trængsler!
Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
18 Se hen til min Elendighed og min Møje, og forlad mig alle mine Synder!
Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
19 Se hen til mine Fjender, thi de ere mange; og de hade mig med uretfærdigt Had.
Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
20 Bevar min Sjæl og red mig, at jeg ikke beskæmmes, thi jeg tror paa dig.
Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
21 Lad Retsindighed og Oprigtighed bevare mig; thi jeg bier efter dig.
Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
22 Forløs, o Gud, Israel af al dets Nød!
Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!

< Salme 25 >