< Salme 132 >
1 Herre! kom David i Hu for alle hans Lidelser,
Waƙar haurawa. Ya Ubangiji, ka tuna da Dawuda da kuma dukan irin wuyan da ya jimre.
2 ham, som tilsvor Herren og lovede Jakobs mægtige:
Ya yi rantsuwa ga Ubangiji ya kuma yi alkawari ga Maɗaukaki na Yaƙub cewa,
3 „Jeg vil ikke gaa ind i mit Hus's Telt, jeg vil ikke opstige paa min Sengs Leje;
“Ba zan shiga gidana ko in kwanta a gado ba,
4 jeg vil ikke lade mine Øjne sove, eller mine Øjenlaage blunde,
ba zan ba wa idanuna barci ba, ba gyangyaɗi wa idanuna,
5 førend jeg finder et Sted for Herren, en Bolig for Jakobs mægtige.”
sai na sami wuri wa Ubangiji, mazauni domin Maɗaukaki na Yaƙub.”
6 Se, vi hørte om den i Efrata; vi fandt den paa Jaars Mark.
Mun ji haka a Efrata, muka yi ƙaro da shi a filayen Ya’ar,
7 Vi ville gaa ind i hans Bolig, vi ville tilbede for hans Fødders Fodskammel.
“Bari mu tafi wurin zamansa; bari mu yi sujada a wurin sa ƙafafunsa,
8 Herre! staa op til din Hvile, du og din Magts Ark.
ka tashi, ya Ubangiji, ka kuma zo wurin hutunka, kai da akwatin alkawarin ƙarfinka.
9 Lad dine Præster klæde sig med Retfærdighed og dine hellige synge med Fryd.
Bari a suturta firistocinka da adalci; bari tsarkakanka su rera don farin ciki.”
10 For David, din Tjeners Skyld, forskyd ikke din Salvedes Ansigt!
Saboda Dawuda bawanka, kada ka ƙi shafaffenka.
11 Herren tilsvor David den Sandhed, fra hvilken han ikke vilde vige: „Af dit Livs Frugt vil jeg sætte en Mand paa din Trone.”
Ubangiji ya rantse wa Dawuda tabbataccen rantsuwa cewa ba zai janye ba cewa, “Ɗaya daga cikin zuriyarka zan sa a kan kursiyinka,
12 Dersom dine Børn holde min Pagt og mine Vidnesbyrd, som jeg vil lære dem, da skulle og deres Børn altid sidde paa din Trone.
in’ya’yanka maza za su kiyaye alkawari da farillan da na koya musu, to’ya’yansu maza za su zauna a kan kursiyinka har abada abadin.”
13 Thi Herren har udvalgt Zion, han har begæret sig den til Bolig:
Gama Ubangiji ya zaɓi Sihiyona, ya so ta zama mazauninsa,
14 „Den er min Hvile altid, her vil jeg bo; thi jeg har begæret den.
“Wannan shi ne wurin hutuna har abada abadin; a nan zan zauna ina mulki gama ina son ta,
15 Jeg vil velsigne Spisen der, jeg vil mætte de fattige der med Brød.
zan albarkace ta da tanade-tanade masu yawa; matalautanta za su ƙoshi da abinci.
16 Og jeg vil klæde dens Præster med Salighed, og dens hellige skulle synge med Fryd.
Zan suturta firistocinta da ceto, tsarkakanta kuma kullum za su rera don farin ciki.
17 Der vil jeg lade et Horn opvokse for David; jeg har beredt en Lampe for min Salvede.
“A nan zan sa ƙaho ya yi girma wa Dawuda in kuma kafa fitila saboda shafaffena.
18 Hans Fjender vil jeg klæde i Skam, men paa ham skal hans Krone blomstre.
Zan suturta abokan gābansa da kunya, amma rawanin da yake a kansa zai yi ta walƙiya.”