< Salme 130 >

1 Af det dybe raaber jeg til dig, Herre!
Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
2 Herre! hør paa min Røst; lad dine Øren mærke paa mine ydmyge Begæringers Røst.
Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
3 Dersom du, Herre, vil tage Vare paa Misgerninger, Herre! hvo kan da bestaa?
In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
4 Men hos dig er Forladelse, paa det du maa frygtes.
Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
5 Jeg biede efter Herren, min Sjæl biede, og jeg haabede paa hans Ord.
Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
6 Min Sjæl længes efter Herren mere end Vægtere efter Morgenen, Vægtere efter Morgenen.
Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
7 Israel! haab paa Herren; thi hos Herren er Miskundhed, og megen Forløsning er hos ham.
Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
8 Og han skal forløse Israel af alle dets Misgerninger.
Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.

< Salme 130 >