< Salme 109 >

1 Min Lovsangs Gud, ti ikke!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
2 Thi de have opladt Ugudeligheds Mund og Falskheds Mund imod mig; de have talt imod mig med Løgnens Tunge,
gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
3 og de have omringet mig med hadefulde Ord og stridt imod mig uden Aarsag.
Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
4 Til Løn for min Kærlighed staa de mig imod, men jeg er stedse i Bøn.
A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
5 Og de beviste mig ondt for godt, og Had for min Kærlighed.
Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
6 Sæt en ugudelig over ham og lad en Anklager staa ved hans højre Haand!
Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
7 Naar han dømmes, da lad ham gaa ud som skyldig, og lad hans Bøn blive tir Synd!
Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
8 Hans Dage vorde faa, en anden annamme hans Embede!
Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
9 Hans Børn vorde faderløse og hans Hustru Enke!
Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
10 Og lad hans Børn vanke hid og did og tigge, og lad dem fra deres øde Hjem søge om Føde!
Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
11 Lad Aagerkarlen kaste Garn ud efter alt det, han har, og fremmede røve Frugten af hans Arbejde.
Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
12 Lad ham ikke finde nogen, som bevarer Miskundhed imod ham, og ingen forbarme sig over hans faderløse!
Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
13 Hans Fremtid vorde afskaaren, deres Navn vorde udslettet i andet Led!
Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
14 Hans Fædres Misgerning vorde ihukommet hos Herren og hans Moders Synd ikke udslettet!
Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
15 De være Herren altid for Øje, og han udrydde deres Ihukommelse af Jorden;
Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
16 fordi han ikke kom i Hu at gøre Miskundhed, men forfulgte en elendig og en fattig Mand og den, som var bedrøvet i Hjertet, for at dræbe ham.
Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
17 Han elskede Forbandelse, den kom ogsaa over ham, og han havde ikke Lyst til Velsignelse, og den blev ogsaa langt fra ham.
Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
18 Og han iførte sig Forbandelse som sit Klædebon, og den kom ind i ham som Vand og som Olie i hans Ben.
Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
19 Den vorde ham som et Klædebon, hvilket han ifører sig, og som et Bælte, hvilket han altid ombinder sig med.
Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
20 Dette er Lønnen fra Herren til dem, som staa mig imod, og som tale ondt imod min Sjæl!
Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
21 Men du, Herre, Herre! gøre vel imod mig for dit Navns Skyld; red mig, fordi din Miskundhed er god.
Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
22 Thi jeg er elendig og fattig, og mit Hjerte er saaret inden i mig.
Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
23 Jeg svinder bort som en Skygge, naar den hælder, jeg bliver jaget bort som en Græshoppe.
Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
24 Mine Knæ rave af Faste, og mit Kød er magert og har ingen Fedme.
Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
25 Og jeg maa være deres Spot; de se mig, de ryste med deres Hoved.
Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
26 Hjælp mig, Herre, min Gud! frels mig efter din Miskundhed,
Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
27 at de maa kende, at dette er din Haand; du, Herre! du har gjort det.
Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
28 Forbande de, saa velsigner du, de rejse sig, men blive til Skamme, og din Tjener glædes.
Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
29 Lad mine Modstandere iføres Forsmædelse og klædes med deres Skam som med en Kappe.
Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
30 Jeg vil takke Herren højlig med min Mund, og jeg vil love ham midt iblandt mange;
Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
31 thi han staar ved den fattiges højre Haand for at frelse ham fra dem, som dømme hans Sjæl.
Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.

< Salme 109 >