< 4 Mosebog 9 >
1 Og Herren talede til Mose i Sinai Ørk, i det andet Aar, efter at de vare udgangne af Ægyptens Land, i den første Maaned, og sagde,
Ubangiji ya yi magana da Musa a Hamadar Sinai, a watan farko na shekara ta biyu bayan fitarsu daga ƙasar Masar. Ya ce,
2 at Israels Børn skulle holde Paaske paa dens bestemte Tid.
“Ka sa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa a ƙayyadadden lokaci.
3 Paa den fjortende Dag i denne Maaned, imellem de tvende Aftener skulle I holde den paa dens bestemte Tid; efter alle dens Skikke og efter alle dens Bestemmelser skulle I holde den.
A yi wannan bikin ƙayyadadden lokaci da yamma, a rana ta goma sha huɗu ga wannan wata, a yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa.”
4 Og Mose sagde til Israels Børn, at de skulde holde Paaske.
Saboda haka sai Musa ya gaya wa Isra’ilawa su yi Bikin Ƙetarewa,
5 Og de holdt Paaske i den første Maaned, paa den fjortende Dag i Maaneden, imellem de tvende Aftener, i Sinai Ørk; efter alt det, som Herren havde befalet Mose, saaledes gjorde Israels Børn.
suka kuwa yi haka a Hamadar Sinai da yamma, a rana ta sha huɗu ga watan farko. Isra’ilawa suka yi dukan abubuwa yadda Ubangiji ya umarci Musa.
6 Og det skete, at der var nogle Mænd, som vare blevne urene ved et Menneskes Lig, og de kunde ikke holde Paasken paa den samme Dag; og de gik frem for Mose Ansigt og for Arons Ansigt den samme Dag.
Amma waɗansunsu ba su iya yin Bikin Ƙetarewa a ranar ba gama sun ƙazantu ta wurin taɓa gawa. Saboda haka suka zo wurin Musa da Haruna a wannan rana
7 Og disse Mænd sagde til ham: Vi ere blevne urene ved et Menneskes Lig; hvi skulle vi derfor udelukkes, at vi ej maa ofre Herren Offer paa dets bestemte Tid, midt iblandt Israels Børn?
suka ce wa Musa, “Mun ƙazantu saboda mun taɓa gawa, don me aka hana mu mu ba da hadaya ga Ubangiji tare da sauran Isra’ilawa a ƙayyadadden lokaci?”
8 Og Mose sagde til dem: Venter lidt, og jeg vil høre, hvad Herren vil nyde om eder.
Musa ya amsa musu ya ce, “Ku dakata sai na sami umarni daga wurin Ubangiji game da ku.”
9 Og Herren talede til Mose og sagde:
Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
10 Tal til Israels Børn og sig: Naar nogen hos eder eller hos eders Efterkommere er bleven uren ved et Lig, eller er paa en lang Rejse, han skal alligevel holde Herren Paaske.
“Gaya wa Isra’ilawa cewa, ‘Sa’ad da waninku ko zuriyarku ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa, ko kuwa ya yi tafiya mai nisa, duk da haka zai kiyaye Bikin Ƙetarewa ta Ubangiji.
11 I den anden Maaned paa den fjortende Dag, imellem de tvende Aftener, skulle de holde den; de skulle æde det med usyrede Brød og beske Urter.
Za su yi bikin da yamma, a rana ta sha huɗu ga wata na biyu. Za su ci naman tunkiya, tare da burodi marar yisti, da ganyaye masu ɗaci.
12 De skulle ikke lade blive tilovers deraf til om Morgenen og ikke bryde noget Ben paa det, efter al Paaskelammets Skik skulle de gøre med det.
Kada su bar kome daga cikinsa yă kai safe, ko a karye ƙashinsa. Sa’ad da suke Bikin Ƙetarewa, dole su kiyaye dukan ƙa’idodinsa.
13 Men den, som er ren og ikke er paa Rejse og efterlader at holde Paaske, den Sjæl skal udryddes fra sit Folk, fordi han ikke har ofret Herrens Offer paa dets bestemte Tid; denne Mand skal bære sin Synd.
Amma in mutumin da yake da tsarki bai kuma yi tafiya ba, ya kuwa ƙi yă yi Bikin Ƙetarewar, dole a ware wannan mutum daga mutanensa, domin bai miƙa hadaya ga Ubangiji a ƙayyadadden lokaci ba. Wannan mutum zai ɗauki alhakin zunubinsa.
14 Og naar en fremmed opholder sig hos eder og holder Herren Paaske, da skal han holde den saa, som Paaskens Skik og som dens Vis er; der skal være een Skik for eder, baade for den fremmede og for den indfødte i Landet.
“‘Baƙon da yake zaune a cikinku wanda yake so yă yi Bikin Ƙetarewar Ubangiji, dole yă yi shi bisa ga dokokinsa da ƙa’idodinsa. Dole ku kasance da ƙa’ida ɗaya ga baƙo da kuma ɗan ƙasa.’”
15 Og paa den Dag, da Tabernaklet blev oprejst, skjulte Skyen Vidnesbyrdets Pauluns Tabernakel; og om Aftenen var over Tabernaklet som en Ild at se til, indtil om Morgenen.
A ranar da aka kafa Tenti na Alkawari, sai girgije ya rufe shi. Daga yamma har safe, girgijen da yake bisa tabanakul ya yi kama da wuta.
16 Saaledes skete det stedse, at Skyen skjulte det; og om Natten var det som en Ild at se til.
Haka ya ci gaba da kasancewa; girgijen ya rufe shi, da dare kuma sai ya yi kamar wuta.
17 Og eftersom Skyen hævede sig op fra Paulunet, rejste Israels Børn derefter; og paa det Sted, hvor Skyen blev, der lejrede Israels Børn sig.
Duk sa’ad da aka ɗaga girgijen daga Tentin, sai Isra’ilawa su kama hanya; duk inda girgijen ya tsaya, a nan Isra’ilawa za su yi sansani.
18 Efter Herrens Mund rejste Israels Børn, og efter Herrens Mund lejrede de sig; alle de Dage, som Skyen boede over Tabernaklet, bleve de liggende.
Da umarnin Ubangiji, Isra’ilawa suke tashi. Da umarninsa kuma suke sauka. Muddin girgijen yana tsaye a bisa tabanakul, sukan yi ta zamansu a sansanoni.
19 Og naar Skyen blev over Tabernaklet mange Dage, da toge Israels Børn Vare paa, hvad Herren vilde have varetaget, og rejste ikke.
Sa’ad da girgijen ya ci gaba da kasancewa a bisan tabanakul na dogon lokaci, Isra’ilawa sukan bi umarnin Ubangiji, ba kuwa za su tashi ba.
20 Og det var ligesaa, naar Skyen var faa Dage over Tabernaklet; efter Herrens Mund lejrede de sig, og efter Herrens Mund rejste de.
Wani lokaci girgijen yakan yi’yan kwanaki ne kawai a bisa tabanakul; da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani da umarninsa kuma su tashi.
21 Og det var ligesaa, naar Skyen var der fra Aftenen indtil Morgenen, og Skyen hævede sig om Morgenen, da rejste de; eller naar Skyen hævede sig om Dagen eller om Natten, da rejste de.
Wani lokaci girgijen yakan zauna daga yamma har safiya ne kawai, sa’ad da kuma aka ɗaga shi da safe, sai su kama hanya. Ko da rana, ko da dare, duk sa’ad da aka ɗaga girgijen, sai su ma su tashi.
22 Eller naar Skyen blev to Dage eller een Maaned eller eet Aar over Tabernaklet, saa den boede over det, da bleve Israels Børn liggende og rejste ikke; men naar den hævede sig, rejste de.
Ko girgijen ya yi kwana biyu a bisa tabanakul, ko wata guda, ko shekara, Isra’ilawa za su zauna a sansani ba kuwa za su tashi ba; amma sa’ad da aka ɗaga shi, sai su kuma su tashi.
23 Efter Herrens Mund lejrede de sig, og efter Herrens Mund rejste de; de toge Vare paa, hvad Herren vilde have varetaget, efter Herrens Mund ved Mose.
Da umarnin Ubangiji sukan kafa sansani, da umarninsa kuma sukan tashi. Sukan bi umarnin Ubangiji, bisa ga umarninsa ta wurin Musa.