< 4 Mosebog 21 >

1 Der Kananiten, Arads Konge, som boede i Sydlandet, hørte, at Israel kom ind ad Spejdernes Vej, da stred han imod Israel og førte nogle af dem bort i Fangenskab.
Sa’ad da sarkin Arad, mutumin Kan’ana, wanda yake zaune a Negeb, da ya ji cewa Isra’ila yana zuwa ta hanyar Atarim, sai ya fito, yă yaƙi Isra’ilawa, yă kuma kama waɗansunsu.
2 Da lovede Israel Herren et Løfte og sagde: Dersom du giver dette Folk i min Haand, da vil jeg lyse deres Stæder i Band.
Sai Isra’ila suka yi alkawari wa Ubangiji suka ce, “In ka ba da waɗannan mutane a hannunmu, za mu hallaka dukan garuruwansu ƙaf.”
3 Og Herren hørte Israels Røst og overgav Kananiterne, og man bandlyste dem og deres Stæder og kaldte det Steds Navn Horma.
Ubangiji kuwa ya saurari kukan Isra’ila, ya kuma ba da Kan’aniyawa a gare su. Suka hallaka su da biranensu ƙaf; saboda haka aka sa wa wurin suna Horma.
4 Saa rejste de fra det Bjerg Hor paa Vejen til det røde Hav, for at drage omkring Edoms Land; og Folkets Sjæl blev utaalmodig paa Vejen.
Suka kama hanya daga Dutsen Hor ta hanya zuwa Jan Teku, don su kauce wa Edom. Amma mutane suka rasa haƙuri a hanya;
5 Og Folket talede imod Gud og imod Mose: Hvorfor førte I os op af Ægypten for at dø i Ørken? thi her er hverken Brød eller Vand, og vor Sjæl kedes ved denne ringe Mad.
suka yi wa Allah da Musa gunaguni, suka ce, “Me ya sa kuka fitar da mu daga Masar, kuka kawo mu mu mutu a wannan hamada? Babu abinci! Babu ruwa! Mu dai mun gaji da wannan abinci marar amfani!”
6 Da sendte Herren giftige Slanger iblandt Folket, og de bed Folket, og der døde meget Folk af Israel.
Sai Ubangiji ya aiko da macizai masu dafin a cikinsu, suka sassari mutane, Isra’ilawa masu yawa kuwa suka mutu.
7 Da kom Folket til Mose, og de sagde: Vi have syndet, thi vi have talet imod Herren og imod dig, bed til Herren, at han vil tage de Slanger fra os; og Mose bad for Folket.
Mutanen suka zo wurin Musa, suka ce, “Mun yi zunubi, da muka yi wa Ubangiji da kai gunaguni. Ka yi addu’a don Ubangiji yă ɗauke mana macizan nan.” Saboda haka Musa ya yi addu’a domin mutane.
8 Da sagde Herren til Mose: Gør dig en Slange, og sæt den paa en Stang; og det skal ske, at hver som er bidt og ser den, han skal leve.
Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ƙera siffar maciji ka rataye shi a bisa doguwar sanda; kowa da maciji ya sare shi, idan ya dubi macijin nan da ka rataye, zai rayu.”
9 Da gjorde Mose en Kobberslange og satte den paa en Stang; og det skete, naar en Slange havde bidt nogen, og han saa til den Kobberslange, da blev han i Live.
Saboda haka Musa ya ƙera macijin tagulla, ya kuma rataye shi bisa doguwar sanda. Sa’an nan duk wanda maciji ya sare shi, ya kuma dubi macijin tagullar, zai warke.
10 Og Israels Børn rejste derfra, og de lejrede sig i Oboth.
Isra’ilawa suka kama hanya, suka yi sansani a Obot.
11 Og de rejste fra Oboth, og de lejrede sig ved Abirams Høje i Ørken, som er lige foran Moab, mod Solens Opgang.
Sai suka tashi daga Obot, suka yi sansani a Iye Abarim a hamadar da take fuskantar Mowab, wajen fitowar rana.
12 Derfra rejste de og lejrede sig ved den Bæk Sered.
Daga nan kuma suka ci gaba, suka yi sansani a Kwarin Zered.
13 Derfra rejste de og lejrede sig paa denne Side Arnon, som er i Ørken, og som gaar ud fra Amoriternes Landemærke; thi Arnon var Moabs Landemærke imellem Moab og imellem Amoriterne.
Suka tashi daga nan, suka sauka kusa da Arnon wanda yake a hamadar da ta miƙe zuwa iyakar Amoriyawa. Arnon shi ne iyakar Mowab, wanda yake tsakanin Mowab da Amoriyawa.
14 Derfor siges i Herrens Stridsbog: „Vaheb i Sufa og Arnons Bække,
Shi ya sa Littafin Yaƙoƙin Ubangiji ya ce, “Waheb ta cikin yankin Sufa, da kwaruruka na tuddan Arnon,
15 og Bækkenes Løb, som strækker sig til Ars Bolig og støder paa Moabs Landemærke.
da gangaren kwaruruka, wanda ya nausa zuwa garin Ar, ya kuma dangana da kan iyakar Mowab.”
16 Og derfra rejste de til Beer, det er den Brønd, som Herren talede om til Mose: Saml Folket, og jeg vil give dem Vand.
Daga can, suka gangara zuwa Beyer, wato, rijiyar da Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tattara mutane duka, zan kuwa ba su ruwa.”
17 Da sang Israel denne Sang: „Stig, Brønd! sjunger om den.
Sai Isra’ilawa suka rera wannan waƙa, “Ki ɓuɓɓugo da ruwa, Ke rijiya! Rera waƙa game da ita,
18 Brønd, som er graven af Fyrsterne, kastet af de ædle iblandt Folket, med Fyrstespir, med deres Herskerstave!” Og fra den Ørk rejste de til Matthana,
game da rijiyar da’ya’yan sarki suka haƙa, rijiyar da manyan mutane masu sandunan sarauta suka nuna da sandunansu.” Sa’an nan suka tashi daga hamadar, suka tafi Mattana,
19 og fra Matthana til Nahaliel, og fra Nahaliel til Bamoth,
daga Mattana, suka tafi Nahaliyel, daga Nahaliyel, suka tafi Bamot,
20 og fra Bamoth til den Dal, som er paa Moabs Mark, mod Toppen af Pisga, der skuer ud over Ørken.
daga Bamot kuma suka tafi kwarin da yake cikin Mowab inda ƙwanƙolin Fisga yake fuskantar hamada.
21 Og Israel sendte Bud hen til Sihon, Amoriternes Konge, og lod sige:
Isra’ila suka aiki manzanni wurin Sihon sarkin Amoriyawa su ce,
22 Lad mig gaa igennem dit Land, vi ville ikke bøje ind paa Ager eller paa Vingaard, vi ville ikke drikke Vand af nogen Brønd, vi ville drage ad Kongevejen, indtil vi ere komne igennem dit Landemærke.
“Ka bari mu ratsa ta ƙasarka. Ba za mu shiga wata gona ba, ba za mu kuma shiga gonar inabi, ko mu sha ruwa daga wata rijiya ba. Za mu bi ta babbar hanyar sarki, har mu fita ƙasarka.”
23 Og Sihon vilde ikke tilstede Israel at gaa igennem sit Landemærke; men Sihon samlede alt sit Folk og drog ud mod Israel i Ørken og kom til Jaza; og han stred imod Israel.
Amma Sihon bai bar Isra’ila su ratsa ta yankinsa ba. Sai ya tara dukan sojojinsa, suka fita zuwa cikin hamada, su yaƙi Isra’ila. Da ya kai Yahaz, sai ya yaƙi Isra’ila.
24 Men Israel slog ham med skarpe Sværd og indtog hans Land til Ejendom, fra Arnon indtil Jabok, indtil Ammons Børn; men Ammons Børns Landemærke var fast.
Isra’ila fa suka kashe shi da takobi, suka ƙwace ƙasarsa, tun daga kogin Arnon har zuwa kogin Yabbok, zuwa kan iyakar Ammonawa kawai, gama sun yi wa iyakansu katanga.
25 Saa indtog Israel alle disse Stæder, og Israel tog Bolig i alle Amoriternes Stæder, i Hesbon, og alle dens tilliggende Byer.
Isra’ila suka ci dukan biranen Amoriyawa, suka kuma zauna a cikinsu, haɗe da babban birnin Heshbon da dukan ƙauyukanta.
26 Thi Hesbon var Sihons, Amoriternes Konges, Stad; og han havde stridt mod Moabiternes forrige Konge og taget alt hans Land fra ham indtil Arnon.
Sihon sarkin Amoriyawa ya yi mulkin Heshbon, bayan ya ci sarkin Mowab na dā da yaƙi, ya kuma ƙwace dukan ƙasarsa har zuwa arewancin kogin Arnon.
27 Derfor sige de, som tale Ordsprog: „Kommer til Hesbon! Sihons Stad skal bygges og grundfæstes.
Shi ya sa Amoriyawa suka rubuta wannan waƙa game da Heshbon suka ce, “Ku zo mu sāke gina Heshbon, birnin Sihon.
28 Thi der er udgangen en Ild af Hesbon, en Lue af Sihons Stad, den har fortæret Ar i Moab, Herrerne over Arnons Høje.
“Mayaƙansa sun fito kamar harshen wuta suka ƙone birnin Ar na Mowab suna hallaka’yan ƙasar tuddan Arnon.
29 Ve dig, Moab! du, Kamos Folk, er fortabt! han har givet sine Sønner som Flygtninge og sine Døtre som Fanger til Sihon, Amoriternes Konge.
Kaitonki, Mowab! Gunkinki Kemosh ya yashe mutanenki; aka kuma kama su, aka kai su bauta wajen Sihon sarkin Amoriyawa.
30 Og vi have nedskudt dem; Hesbon er tabt indtil Dibon; og vi have lagt dem øde indtil Nofa, som naar indtil Medba.”
“Amma mun tumɓuke su, mun hallaka garuruwan Heshbon har zuwa Dibon. Mun ragargaza su har zuwa Nofa wanda ya miƙe zuwa Medeba.”
31 Saa tog Israel Bolig i Amoriternes Land.
Ta haka Isra’ila suka zauna a ƙasar Amoriyawa.
32 Og Mose sendte ud at bespejde Jaeser, og de indtoge dens tilliggende Byer; og han fordrev Amoriterne, som vare der.
Sai Musa ya aika’yan leƙen asiri zuwa Yazer. Daga baya, sai Isra’ilawa suka ci ƙauyukan da suke kewaye, suka kuma kori Amoriyawa da suke zaune a can.
33 Og de vendte sig og droge op ad Vejen til Basan; da drog Og, Kongen af Basan, ud imod dem, han og alt hans Folk til Strid, til Edrei.
Sai suka juya suka haura kan hanya ta zuwa Bashan, inda Og yake sarauta, ya kuwa fito tare da dukan sojojinsa suka yi yaƙi da Isra’ila a Edireyi.
34 Og Herren sagde til Mose: Frygt ikke for ham; thi jeg har givet ham i din Haand, og alt hans Folk og hans Land; og du skal gøre ved ham, ligesom du gjorde ved Sihon, Amoriternes Konge, som boede i Hesbon.
Ubangiji ya ce wa Musa, “Kada ka ji tsoronsa, gama na ba da shi a gare ka, da dukan sojojinsa da kuma ƙasarsa. Ka yi da shi yadda ka yi da Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon.”
35 Og de sloge ham og hans Sønner og alt hans Folk, saa at man ikke lod nogen blive tilovers for ham, og de indtoge hans Land til Ejendom.
Ta haka suka kashe shi, tare da’ya’yansa maza da kuma dukan sojojinsa, ba wanda ya ragu. Suka kuma mamaye ƙasarsa.

< 4 Mosebog 21 >