< 4 Mosebog 15 >

1 Og Herren talede til Mose og sagde:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Tal til Israels Børn, og du skal sige til dem: Naar I komme til det Land, som I skulle bo udi, hvilket jeg vil give eder,
“Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Bayan kun shiga ƙasar da nake ba ku a matsayin gida,
3 og I ville gøre Herren et Ildoffer, Brændoffer eller Slagtoffer, for at indfri et særligt Løfte, eller som et frivilligt Offer, eller paa eders bestemte Tider, for at berede Herren en behagelig Lugt, af stort Kvæg eller smaat Kvæg:
kuka yi hadayar da akan yi da wuta ga Ubangiji, daga cikin shanu, ko tumaki, abin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji, ko hadaya ta ƙonawa, ko hadayu don alkawura na musamman, ko hadayar yardar rai, ko kuma hadaya ta biki,
4 Da skal den, som ofrer sit Offer, ofre til Herren et Madoffer af en tiende Part Mel, blandet med en fjerde Part af en Hin Olie;
sai shi wanda ya kawo hadayar yă miƙa wa Ubangiji hadaya ta gari mai laushi mai kyau, kashi ɗaya bisa goma na efa wanda aka kwaɓa da kwalaba ɗaya na mai.
5 og en fjerde Part af en Hin Vin til et Drikoffer skal du befede, tillige med Brændofret eller Slagtofret, til hvert Lam.
Da kowane ɗan rago don hadaya ta ƙonawa, a shirya kwalaba ɗaya na ruwan inabi, a matsayin hadaya ta sha.
6 Eller er det til en Væder, saa skal du lave Madoffer af tvende tiende Parter Mel, blandet med en tredje Part af en Hin Olie;
“‘In da rago ne za a miƙa, to, sai a shirya hadaya ta gari mai laushi, garin yă zama kashi biyu bisa goma na efa. A kwaɓa shi da kashi ɗaya bisa uku na garwan mai,
7 og Vin til et Drikoffer, en tredje Part af en Hin, skal du ofre til en behagelig Lugt for Herren.
da kashi ɗaya bisa uku na garwan ruwan inabi, a matsayin hadaya ta sha. A miƙa ta abin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji.
8 Og naar du vil lave en ung Tyr til et Brændoffer eller Slagtoffer, for at indfri et særligt Løfte eller gøre et Takoffer for Herren,
“‘Sa’ad da kuka shirya rago don hadaya ta ƙonawa saboda alkawari na musamman, ko hadaya ta salama ga Ubangiji,
9 da skal man ofre tillige med den unge Tyr som Madoffer tre tiende Parter Mel, blandet med en halv Hin Olie.
sai ku kawo hadaya ta gari tare da bijimi, kashi ɗaya bisa uku na gari mai laushi kwaɓaɓɓe da rabin garwan mai.
10 Og du skal ofre Vin til Drikofret, en halv Hin; det er et Ildoffer, en behagelig Lugt for Herren.
A kuma kawo rabin garwan ruwan inabi na hadaya ta sha. Za tă zama hadayar da aka yi da wuta mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
11 Paa denne Maade skal det ske med een Okse eller med een Væder eller med eet Lam af Faarene eller af Gederne;
Haka za a yi da kowane bijimi, ko rago, ko ɗan rago, ko bunsuru.
12 efter det Tal, som I skulle bringe, skulle I lave det paa denne Maade, for ethvert efter deres Tal.
Haka za a yi da kowannensu bisa ga abin da aka shirya.
13 Hver indfødt skal gøre disse Ting paa denne Maade for at ofre et Ildoffer, en behagelig Lugt for Herren.
“‘Duk wanda yake ɗan ƙasa, ta haka ne dole zai aikata waɗannan abubuwa sa’ad da ya kawo hadaya da akan yi da wuta mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
14 Og om en fremmed opholder sig hos eder, eller en, som er midt iblandt eder hos eders Efterkommere, og han vil gøre et Ildoffer, en behagelig Lugt for Herren, saa skal han gøre, ligesom I skulle gøre.
Idan baƙon da yake baƙunci a cikinku, ko kowane ne da yake tare da ku a dukan zamananku, yana so yă ba da hadayar da akan yi da wuta don a yi ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji, dole yă yi kamar yadda kuke yi.
15 Du Menighed! der skal være een Skik for eder og for den fremmede, som opholder sig hos eder, det er en evig Skik hos eders Efterkommere; som det er for eder, saa skal det være for den fremmede, for Herrens Ansigt.
Ƙa’ida ɗaya ce ga jama’a da kuma baƙin da suke zama a cikinku, wannan za tă zama dawwammamiyar farilla a dukan tsararraki masu zuwa. Da ku, da baƙi, za ku zama ɗaya a gaban Ubangiji.
16 Een Lov og een Ret skal være for eder og for den fremmede, som opholder sig hos eder.
Doka ɗaya da ƙa’ida ɗaya za a yi aiki da ita a kan ku da kuma baƙin da suke zama a cikinku.’”
17 Og Herren talede til Mose og sagde:
Ubangiji ya ce wa Musa,
18 Tal til Israels Børn, og du skal sige til dem: Naar I komme i det Land, hvorhen jeg vil føre eder,
“Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga ƙasar da ina kai ku,
19 da skal det ske, naar I æde af Landets Brød, at I skulle bringe en Offergave for Herren.
kuka ci abincin ƙasar, ku miƙa wani sashe na amfanin ƙasar a matsayin hadaya ga Ubangiji.
20 Det første af eders Dejg, nemlig en Kage, skulle I bringe til en Gave, ligesom Gaven fra Loen, saaledes skulle I bringe den.
Ku kawo waina daga nunan fari na ɓarzajjen hatsinku, ku kuma miƙa shi a matsayin hadaya daga masussuka.
21 Af det første af eders Dejg skulle I give Herren en Gave, hos eders Efterkommere.
A duk tsararraki masu zuwa, za ku miƙa wannan hadaya daga nunan fari na ɓarzajjen hatsinku ga Ubangiji.
22 Og naar I forse eder og ikke gøre alle disse Bud, som Herren har talet til Mose,
“‘To, in ku a matsayin jama’a, da gangan kuka ƙi kiyaye waɗannan ƙa’idodi da Ubangiji ya ba wa Musa ba,
23 alt det, som Herren har budet eder ved Mose, fra den Dag af, da Herren har befalet det, og derefter, hos eders Efterkommere:
ko wani daga cikin umarnan da Ubangiji ya ba ku ta wurinsa, daga ranar da Ubangiji ya ba da su, har zuwa tsararraki masu zuwa,
24 Da skal det ske, om noget er skjult for Menighedens Øjne og er gjort af Vanvare, at den ganske Menighed skal lave en ung Tyr til Brændoffer, til en behagelig Lugt for Herren, og dens Madoffer og dens Drikoffer efter vanlig Vis, og een Gedebuk til Syndoffer.
in kuwa aka yi haka ba da gangan ba, kuma da rashin sani, sai duk jama’a su miƙa ɗan bijimi don hadaya ta ƙonawa mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji, tare da ƙayyadadden hadaya ta gari, da hadaya ta sha, da kuma bunsuru na hadaya don zunubi.
25 Saa skal Præsten gøre Forligelse for al Israels Børns Menighed, og det bliver dem forladt; thi det er af Vanvare, og de skulle føre deres Offer frem til et Ildoffer for Herren, og deres Syndoffer for Herrens Ansigt for deres Vanvares Skyld,
Firist kuwa zai yi kafara domin dukan jama’ar Isra’ilawa, za a kuma gafarta musu, gama ba da gangan ba ne suka aikata, kuma sun kawo wa Ubangiji hadayar da akan yi da wuta da kuma hadaya don zunubi saboda laifinsu.
26 og det bliver al Israels Børns Menighed og den fremmede, som opholder sig midt iblandt dem, forladt, efterdi det er vederfaret det ganske Folk af Vanvare.
Za a gafarta wa dukan jama’ar Isra’ilawa, da baƙin da suke zama a cikinsu, gama duk laifin da aka yi da rashin sani, yakan shafi dukan mutane.
27 Men naar en enkelt synder af Vanvare, da skal han ofre en aargammel Ged til et Syndoffer.
“‘Amma in mutum ɗaya ne kaɗai ya yi laifi ba da gangan ba, dole yă kawo akuya domin hadaya don zunubi.
28 Og Præsten skal gøre Forligelse for ham, som har forset sig og syndede af Vanvare, for Herrens Ansigt; han skal gøre Forligelse for ham, saa bliver det ham forladt.
Firist zai yi kafara a gaban Ubangiji saboda mutumin nan da ya aikata laifi ba da gangan ba, in kuwa an yi kafara saboda shi, za a gafarta masa.
29 For den indfødte blandt Israels Børn og for den fremmede, som opholder sig midt iblandt dem, hos eder skal være een Lov for den, som gør noget af Vanvare.
Ƙa’ida dai za tă zama ɗaya ga duk wanda ya yi laifi ba da gangan ba, ko shi ɗan ƙasa ne, ko kuma baƙon da yake zama a cikinku.
30 Men den Person, som gør noget af Trodsighed, være sig en indfødt eller en fremmed, han har forhaanet Herren, og den Sjæl skal udryddes midt ud af sit Folk;
“‘Amma duk wanda ya yi zunubi da gangan, ko shi ɗan ƙasa ne, ko baƙo, ya saɓi Ubangiji, dole a ware wannan mutum daga mutanensa,
31 thi han har foragtet Herrens Ord og gjort hans Bud til intet; den Sjæl skal udryddes, hans Misgerning skal være paa ham.
gama ya rena maganar Ubangiji, ya kuma karya umarninsa. Tabbatacce za a kashe wannan mutum, alhakinsa laifinsa kuwa yana wuyansa.’”
32 Og Israels Børn vare i Ørken, og de fandt en Mand, som sankede Ved paa en Sabbatsdag.
Yayinda Isra’ilawa suke ciki hamada, sai aka sami wani mutum yana tattara itace a ranar Asabbaci.
33 Og de, som fandt ham sanke Ved, førte ham frem til Mose og til Aron og til al Menigheden.
Waɗanda suka gan shi, suka kawo shi wurin Musa da Haruna da dukan taro,
34 Og de satte ham i Forvaring; thi det var ikke forklaret, hvad der skulde gøres ved ham.
sai suka sa shi a gidan waƙafi don ba su riga sun san abin da za a yi da shi ba tukuna.
35 Og Herren sagde til Mose: Den Mand skal visselig dødes; den ganske Menighed skal stene ham med Stene uden for Lejren.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Dole mutumin yă mutu. Dole dukan taron su jajjefe shi a bayan sansani.”
36 Da førte al Menigheden ham ud uden for Lejren, og de stenede ham med Stene, og han døde; saasom Herren havde befalet Mose.
Saboda haka taron suka ɗauke shi zuwa bayan sansani, suka kuma jajjefe shi har ya mutu, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
37 Og Herren talte til Mose og sagde:
Ubangiji ya ce wa Musa,
38 Tal til Israels Børn, og du skal sige til dem, at de skulle gøre sig Kvaster paa Fligene af deres Klæder, hos deres Efterkommere, og de skulle sætte en blaa ulden Snor paa hver Fligs Kvast.
“Ka yi magana da Isra’ilawa, ka ce musu, ‘A dukan tsararraki masu zuwa, za ku sa tuntaye a gefen rigunarku, su sa zare mai ruwan shuɗi a bisan kowane tuntu.
39 Og den skulle I have ved hver Kvast, for at I skulle se den og ihukomme alle Herrens Bud og gøre dem; og I skulle ikke søge noget efter eders eget Hjerte og efter eders Øjne, som I bole efter,
Tuntayen za su zama muku abin dubawa don ku riƙa tunawa da dukan umarnan Ubangiji, don kada ku bi son zuciyarku, da sha’awar idanunku yadda kuka taɓa yi.
40 paa det I skulle ihukomme og gøre alle mine Bud; og I skulle være hellige for eders Gud.
Sa’an nan za ku riƙa tuna, ku kuma aikata dukan umarnaina ku zama tsarkaka ga Allahnku.
41 Jeg er Herren eders Gud, som har udført eder af Ægyptens Land for at være eder en Gud; jeg er Herren eders Gud.
Ni ne Ubangiji Allahnku, da ya fitar da ku daga Masar, don in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”

< 4 Mosebog 15 >