< 4 Mosebog 14 >

1 Da opløftede og hævede al Menigheden sin Røst, og Folket græd den samme Nat.
A daren nan, sai dukan jama’ar suka tā da murya, suka yi kuka da ƙarfi.
2 Og alle Israels Børn knurrede imod Mose og imod Aron, og al Menigheden sagde til dem: Gid vi vare døde i Ægyptens Land, eller gid vi vare døde i denne Ørk!
Dukan Isra’ilawa suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna, dukan taron kuwa suka ce musu, “Da ma mun mutu a Masar! Ko kuma a wannan hamada ma!
3 Og hvorfor fører Herren os til dette Land til at falde ved Sværdet? vore Hustruer og vore smaa Børn maa blive til Rov; er det os ikke bedst at vende tilbage til Ægypten?
Don me Ubangiji yana kawo mu wannan ƙasa yă bar mu kawai mu mutu da takobi? A kuma kwashe matanmu da’ya’yanmu ganima. Ashe, bai fi mana mu koma Masar ba?”
4 Og den ene sagde til den anden: Lader os indsætte en Høvedsmand og vende tilbage til Ægypten.
Sai suka ce wa junansu, “Mu naɗa wa kanmu shugaba, mu koma Masar.”
5 Men Mose og Aron faldt ned paa deres Ansigter, for Israels Børns hele Menigheds Forsamling.
Sai Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki a gaban jama’ar Isra’ilawa da suka taru a can.
6 Og Josva, Nuns Søn, og Kaleb, Jefunne Søn, der vare blandt dem, der havde bespejdet Landet, de sønderreve deres Klæder.
Yoshuwa ɗan Nun da Kaleb ɗan Yefunne waɗanda suke tare da masu leƙo asirin ƙasar, suka yayyage tufafinsu
7 Og de sagde til al Israels Børns Menighed, sigende: Det Land, som vi vandrede igennem til at bespejde det, er et saare, ja saare godt Land.
suka ce wa dukan taron Isra’ilawa, “Ƙasar da muka ratsa, muka kuma leƙi asirinta, tana da kyau sosai.
8 Dersom Herren har Behagelighed til os, da fører han os ind i dette Land og giver os det, et Land, som flyder med Mælk og Honning.
In Ubangiji ya ji daɗinmu, zai kai mu ƙasan nan, ƙasar da take zub da madara da zuma, yă kuwa ba mu ita.
9 Men værer kun ikke genstridige imod Herren, og I, frygter ikke Folket i det Land, thi dem tage vi som en Bid Brød; deres Værn er veget fra dem; men med os er Herren, frygter ikke for dem.
Sai dai kada ku tayar wa Ubangiji. Kada kuma ku ji tsoron mutane ƙasar, domin za mu gama da su. Kāriyarsu ta gama, amma Ubangiji yana nan tare da mu. Kada ku ji tsoronsu.”
10 Da sagde den ganske Menighed, at man skulde stene dem med Stene, og Herrens Herlighed blev set i Forsamlingens Paulun for alle Israels Børn.
Amma taron jama’a suka ce za su jajjefe su da duwatsu. Sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana a Tentin Sujada ga dukan Isra’ilawa.
11 Og Herren sagde til Mose: Hvor længe skal dette Folk opirre mig? og hvor længe ville de ikke tro paa mig, uagtet alle de Tegn, som jeg har gjort midt iblandt dem?
Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yaushe mutanen nan za su rena ni? Har yaushe za su ƙi gaskata da ni, duk da yawan mu’ujizan da nake yi a cikinsu?
12 Jeg vil slaa dem med Pest og udrydde dem; og jeg vil gøre dig til et større og stærkere Folk, end dette er.
Zan buge su duka da annoba, in hallaka su, amma zan mai da kai al’umma mai girma, da kuma ƙarfi fiye da su.”
13 Da sagde Mose til Herren: Ægypterne have hørt, at du har ført dette Folk med din Kraft ud af deres Midte.
Sai Musa ya ce wa Ubangiji, “Ai, Masarawa za su ji game da wannan! Da ikonka ka fitar da mutanen nan daga cikinsu.
14 Og de have sagt det til dette Lands Indbyggere; de have hørt, at du, Herre! er midt iblandt dette Folk, for hvilket du, Herre! ses øjensynlig, og at din Sky staar over dem, og at du gaar for deres Ansigt i en Skystøtte om Dagen og i en Ildstøtte om Natten.
Za su kuwa gaya wa mutanen wannan ƙasa. Sun riga sun ji cewa kai, ya Ubangiji, kana tare da waɗannan mutane, kuma cewa kai, ya Ubangiji, an gan ka fuska da fuska, cewa girgijenka ya tsaya bisansu, cewa kana tafiya a gabansu cikin ginshiƙin girgije da rana, da ginshiƙin wuta kuma da dare.
15 Men slog du dette Folk ihjel som een Mand, da skulle Hedningerne, naar de høre det Rygte om dig, sige saaledes:
In ka kashe dukan mutanen nan gaba ɗaya, al’ummai da suka ji wannan labari game da kai za su ce,
16 Fordi Herren ikke formaaede at føre dette Folk ind i det Land, som han havde tilsvoret dem, derfor har han slaaet dem ned i Ørken.
‘Ubangiji ya kāsa kai waɗannan mutane a ƙasar da ya yi alkawari da rantsuwa ne, shi ya sa ya kashe su a hamada.’
17 Og nu, lad dog Herrens Kraft vise sig stor, som du har talet og sagt:
“Yanzu bari Ubangiji yă nuna ikonsa, kamar dai yadda ka furta.
18 Herren er langmodig og af megen Miskundhed, som forlader Misgerning og Overtrædelse, og som aldeles ikke skal holde den skyldige for uskyldig, som hjemsøger Fædrenes Misgerning paa Børnene, paa dem i tredje og paa dem i fjerde Led.
‘Ubangiji mai jinkiri fushi ne, mai yawan ƙauna, mai gafarta zunubi da tawaye. Duk da haka ba ya ƙyale mai laifi, babu horo. Yana horin’ya’ya saboda zunubin iyayensu har tsara ta uku, da ta huɗu.’
19 Kære, forlad dette Folk dets Misgerning efter din store Miskundhed, og ligesom du har tilgivet dette Folk, fra Ægypten af og hidindtil
Bisa ga ƙaunarka mai girma, ka gafarta zunubin mutanen nan, kamar dai yadda ka gafarta musu daga lokacin da suka bar Masar har zuwa yanzu.”
20 Og Herren sagde: Jeg har forladt det efter dit Ord.
Ubangiji ya amsa ya ce, “Na gafarta musu, yadda ka roƙa.
21 Men sandelig, saa vist som jeg lever, da skal alt Landet opfyldes med Herrens Herlighed;
Duk da haka, muddin ina raye, kuma muddin ɗaukakar Ubangiji ta cika dukan duniya,
22 thi alle de Mænd, som have set min Herlighed og mine Tegn, som jeg gjorde i Ægypten og i Ørken, og nu have fristet mig ti Gange og ikke hørt paa min Røst,
ko ɗaya daga cikinsu da suka ga ɗaukakata da mu’ujizai da na yi a Masar, da kuma a cikin hamada, da suka ƙi yin mini biyayya, suka kuma gwada ni har sau goma,
23 de skulle ikke se det Land, som jeg har tilsvoret deres Fædre, ja ingen af dem, som have opirret mig, skal se det.
ba ko ɗayansu da zai gan ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa zan ba wa kakanninsu. Ba ko ɗaya da ya rena ni, da zai taɓa ganinta.
24 Men min Tjener Kaleb, fordi der er en anden Aand med ham, og han har fuldkommelig efterfulgt mig, ham vil jeg føre til det Land, hvor han var kommen hen, og hans Sæd skal eje det.
Amma domin Kaleb bawana ya kasance da ruhu dabam, ya kuma bi ni da zuciya ɗaya, zan kai shi cikin ƙasar da ya je, zuriyarsa kuwa za su gāje ta.
25 Men Amalekiten og Kananiten bor i Dalen; vender eder i Morgen og rejser i Ørken ad Vejen til det røde Hav.
Da yake Amalekawa da Kan’aniyawa suna zama a kwarin, gobe sai ka koma baya, ka nufi wajen hamada ta hanyar Jan Teku.”
26 Og Herren talede til Mose og Aron og sagde:
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
27 Hvor længe skal jeg se til denne onde Menighed, dem, som knurre imod mig? jeg har hørt Israels Børns megen Knur, hvormed de knurre imod mig.
“Har yaushe wannan muguwar al’umma za tă yi gunaguni a kaina? Na ji koke-koken waɗannan Isra’ilawa masu gunaguni.
28 Sig til dem: Saa sandt som jeg lever, siger Herren, ligesom I have talet for mine Øren, saaledes vil jeg gøre ved eder.
Saboda haka ka gaya musu cewa, ‘Muddin ina raye, in ji Ubangiji, zan yi muku daidai da abin da na ji kuke faɗa.
29 Eders døde Kroppe skulle falde i denne Ørk, og alle eders talte efter alt eders Tal, fra tyve Aar gamle og derover, I som have knurret imod mig.
A cikin wannan hamadan, jikunanku za su fāɗi, kowanne a cikinku mai shekara ashirin ko fiye, wanda aka ƙirga shi cikin ƙidaya, wanda kuma ya yi gunaguni a kaina, da zai shiga wannan ƙasa.
30 I skulle ikke komme ind i det Land, om hvilket jeg har opløftet min Haand og svoret at ville lade eder bo deri, uden Kaleb, Jefunne Søn, og Josva, Nuns Søn.
Ba ko ɗaya daga cikinku da zai shiga ƙasar da na ɗaga hannu na rantse, za tă zama gidanku, sai dai Kaleb ɗan Yefunne da Yoshuwa ɗan Nun.
31 Og eders smaa Børn, om hvilke I sagde, de skulle blive til Rov, ja dem vil jeg føre derind, at de skulle kende det Land, som I have foragtet.
Amma game da’ya’yanku da kuka ce za a kwashe ganima, zan kawo su cikin ƙasar, su ji daɗin ƙasar wadda kuka ƙi.
32 Men eders døde Kroppe, de skulle falde i denne Ørk.
Amma ku, jikunanku za su fāɗi a wannan hamada.
33 Og eders Børn skulle være Hyrder i Ørken fyrretyve Aar og bøde for eders Bolen, indtil I alle ere blevne til døde Kroppe i denne Ørk.
’Ya’yanku za su zama makiyaya a nan, shekaru arba’in suna shan wahala domin rashin amincinku, har sai mutum na ƙarshe a cikinku ya kwanta a hamada.
34 Efter de Dages Tal, i hvilke I have bespejdet Landet, fyrretyve Dage, et Aar for hver Dag, skulle I bære eders Misgerninger fyrretyve Aar, og I skulle fornemme, at jeg har vendt mig bort.
Shekaru arba’in, shekara ɗaya a madadi kwana ɗaya cikin kwanakin arba’in da kuka ɗauka kuka leƙi asirin ƙasa, za ku sha wahala saboda zunubanku, ku kuma san abin da ake nufi da sa ni in yi gāba da ku.’
35 Jeg Herren har sagt: Jeg vil visselig gøre dette ved hele denne onde Menighed, som har forsamlet sig imod mig; de skulle faa Ende i denne Ørk og dø der.
Ni, Ubangiji na faɗa, zan kuwa aikata waɗannan abubuwa a kan dukan muguwar jama’an nan da suka haɗa kai, suka tayar mini. Za su sadu da ƙarshensu a wannan hamada; a nan za su mutu.”
36 Og de Mænd, som Mose havde sendt til at bespejde Landet, og som vare komne igen og havde bragt al Menigheden til at knurre imod ham, idet de førte ondt Rygte ud om Landet,
Saboda haka mutanen da Musa ya aika, su leƙo asirin ƙasar, waɗanda suka komo, suka sa taron jama’a su yi gunaguni a kansa saboda sun kawo rahoto mai banrazana a kan ƙasar,
37 ja de Mænd døde, som havde ført ondt Rygte ud om Landet, ved Plagen for Herrens Ansigt.
waɗannan mutanen da suka kawo rahoto mai banrazana a kan ƙasar, annoba ta buge su, suka kuwa mutu a gaban Ubangiji.
38 Men Josva, Nuns Søn, og Kaleb, Jefunne Søn, de bleve i Live af de Mænd, som vare gangne til at bespejde Landet.
Daga cikin mutanen da suka leƙo asirin ƙasar, Yoshuwa ɗan Nun, da Kaleb ɗan Yefunne ne, kaɗai suka rayu.
39 Og Mose talede disse Ord til alle Israels Børn; da sørgede Folket saare.
Da Musa ya gaya wa dukan Isra’ilawa wannan labari, sai suka yi baƙin ciki ƙwarai.
40 Og om Morgenen stode de tidlig op og gik oven paa Bjerget og sagde: Se, her ere vi, og vi ville drage op til det Sted, som Herren har talet om; thi vi have syndet.
Kashegari da sassafe suka haura ta wajen ƙasa mai tudu suka ce, “Mun yi zunubi, za mu tafi inda Ubangiji ya yi alkawari.”
41 Men Mose sagde: Hvorfor overtræde I Herrens Befaling? det skal ikke lykkes.
Amma Musa ya ce, “Don me kuke rashin biyayya da umarnin Ubangiji? Wannan ba zai yiwu ba!
42 Drager ikke op, thi Herren er ikke midt iblandt eder, at I ikke skulle blive slagne for eders Fjenders Ansigt.
Kada ku haura, domin Ubangiji, ba ya tare da ku. Magabtanku za su ci nasara a kanku,
43 Thi Amalekiterne og Kananiterne ere der for eders Ansigt, og I skulle falde ved Sværdet; thi fordi I have vendt eder bort fra Herren, skal Herren ikke være med eder.
gama Amalekawa da Kan’aniyawa za su kara da ku a can. Domin kun juya daga Ubangiji, ba zai kasance da ku ba, za a kuma karkashe ku da takobi.”
44 Men de formastede sig hovmodelig til at drage op oven paa Bjerget; men Herrens Pagtes Ark og Mose, de vege ikke ud af Lejren.
Duk da haka, suka yi tsammani ba zai zama haka ba, sai suka haura ta wajen ƙasa mai tudu, Musa da akwatin alkawarin Ubangiji dai ba su gusa daga sansanin ba.
45 Da kom Amalekiten og Kananiten ned, som boede paa det samme Bjerg, og de sloge dem og sønderknusede dem indtil Horma.
Sai Amalekawa da Kan’aniyawa mazaunan ƙasar tudu, suka gangaro suka auka musu, suka bubbuge su suka kokkore su har Horma.

< 4 Mosebog 14 >