< 4 Mosebog 12 >
1 Og Maria og Aron talede imod Mose for den morlandske Hustrus Skyld, som han havde taget; thi han havde taget en morlandsk Hustru.
Miriyam da Haruna suka fara zargin Musa saboda matarsa’yar ƙasar Kush da ya aura.
2 Og de sagde: Taler Herren ene og alene ved Mose? mon han ikke ogsaa taler ved os? og Herren hørte det.
Suka ce, “Ubangiji ya yi magana ta wurin Musa ne kaɗai? Ashe, bai yi magana ta wurinmu mu ma ba?” Ubangiji kuwa ya ji wannan.
3 Men den Mand Mose var saare sagtmodig, fremfor alle Mennesker paa Jorderige.
(Musa kuwa mutum ne mai tawali’u ƙwarai, mafi tawali’u fiye da kowane mutum a duniya.)
4 Og Herren sagde hastelig til Mose og til Aron og til Maria: Gaar ud, I tre, til Forsamlingens Paulun; og de tre gik ud.
Nan da nan Ubangiji ya ce wa Musa, da Haruna da kuma Miriyam, “Ku fita ku tafi Tentin Sujada, dukanku uku.” Sai dukansu uku suka tafi.
5 Da kom Herren ned i en Skystøtte og stod i Paulunets Dør; og han kaldte ad Aron og Maria, og de gik begge ud.
Sai Ubangiji ya sauko a cikin ginshiƙin girgije; ya tsaya a bakin ƙofar Tenti, ya kira Haruna da Miriyam. Sa’ad da su biyu suka gusa gaba,
6 Og han sagde: Kære, hører mine Ord: Dersom der er en Profet iblandt eder, giver jeg, Herren, mig tilkende for ham i Synet, i Drømmen taler jeg med ham.
sai ya ce, “Ku ji abin da zan faɗa, “Duk lokacin da akwai annabin Ubangiji a cikinku, nakan bayyana kaina gare shi cikin wahayi, in yi magana da shi cikin mafarkai.
7 Ikke saa med min Tjener Mose; han er tro i mit ganske Hus.
Amma ba haka nake magana da Musa bawana ba; na sa shi yă lura da dukan jama’ata Isra’ila.
8 Jeg taler mundtlig med ham og synlig og ikke i mørk Tale, og han beskuer Herrens Lignelse; hvi frygtede I da ikke at tale imod min Tjener, imod Mose?
Da shi nake magana fuska da fuska, a fili kuma, ba a kacici-kacici ba; yakan ga siffar Ubangiji. To, me ya sa ba ku ji tsoro ku yi magana a kan bawana Musa ba?”
9 Og Herrens Vrede optændtes imod dem, og han gik bort.
Sai fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kansu, ya kuma rabu da su.
10 Og Skyen veg bort fra Paulunet, og se, Maria var spedalsk som Sne; og Aron vendte sig til Maria, og se, hun var spedalsk.
Da girgijen ya tashi daga bisa Tentin, sai ga Miriyam tsaye, kuturwa, fari fat. Haruna kuwa ya juya wajenta ya ga ta kuturce;
11 Og Aron sagde til Mose: Hør mig dog, min Herre, læg ikke den Synd paa os, i hvilken vi have gjort daarlig, og i hvilken vi have syndet.
sai Haruna ya ce wa Musa, “Ranka yă daɗe, ina roƙonka kada ka hukunta mu, gama zunubin da muka yi, mun yi ne cikin wauta.
12 Kære, lad hende ikke være som en Død, hvis halve Kød, naar han kommer ud af sin Moders Liv, er fortæret.
Kada ka sa ta zama kamar haifaffen mataccen jariri daga cikin mahaifiya wanda rabin jikin ruɓaɓɓe ne.”
13 Da raabte Mose til Herren og sagde: Ak, Gud! helbred hende.
Saboda haka sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Allah, ina roƙonka ka warkar da ita!”
14 Og Herren sagde til Mose: Om hendes Fader havde spyttet hende i hendes Ansigt, skulde hun da ikke skamme sig syv Dage? Lad hende blive udelukket fra Lejren syv Dage, og derefter maa hun optages.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Da a ce mahaifinta ne ya tofa mata miyau a fuskarta, ashe, ba za tă ji kunya har kwana bakwai ba? A fitar da ita bayan sansani kwana bakwai; bayan haka za a iya dawo da ita.”
15 Og Maria blev udelukket fra Lejren syv Dage, og Folket rejste ikke, førend Maria blev optaget.
Haka aka fitar da Miriyam bayan sansani kwana bakwai, mutane kuwa ba su ci gaba da tafiya ba sai da aka dawo da ita.
16 Og derefter rejste Folket fra Hazeroth, og de lejrede sig i Ørken Paran.
Bayan haka sai mutane suka bar Hazerot suka sauka a Hamadan Faran.