< Nehemias 2 >

1 Og det skete i Nisan Maaned i Kong Artakserkses's tyvende Aar, da stod der Vin for hans Ansigt, og jeg tog Vinen og gav Kongen, og jeg havde ikke vist mig sørgmodig for hans Ansigt.
A watan Nisan a shekara ta ashirin ta mulkin Sarki Artazerzes, sa’ad aka kawo masa ruwan inabi, sai na karɓa na ba shi. Ban taɓa ɓata fuskata a gabansa ba, sai wannan karo.
2 Da sagde Kongen til mig: Hvorfor er du sørgmodig? og du er ikke syg, det er ikke dette, men dit Hjerte er sørgmodigt; da frygtede jeg saare meget.
Saboda haka sarki ya tambaye ni ya ce, “Me ya sa fuskarka ta ɓaci, ga shi, ba ciwo kake ba? Ba abin da ya kawo wannan, in ba dai kana baƙin ciki ba.” Sai na ji tsoro ƙwarai,
3 Og jeg sagde til Kongen: Kongen leve evindelig! hvorfor skulde jeg ikke være sørgmodig, da den Stad, i hvilken mine Fædres Begravelsers Hus er, ligger øde, og dens Porte ere fortærede af Ild?
na amsa na ce wa sarki, “Ran sarki yă daɗe! Me zai hana fuskata ta ɓaci, sa’ad da birnin da aka binne kakannina tana zaman kango, aka kuma rushe ƙofofinsa da wuta?”
4 Da sagde Kongen til mig: Hvad er det, du søger om? da bad jeg til Gud i Himmelen.
Sai sarki ya ce mini, “Me kake so?” Sai na yi addu’a ga Allah na sama,
5 Da sagde jeg til Kongen: Dersom det synes Kongen godt, og dersom din Tjener synes god for dit Ansigt, da sende du mig til Juda, til mine Fædres Begravelsers Stad, at jeg maa bygge den op.
na kuwa ba wa sarki amsa, na ce, “In ya gamshi sarki, in kuma bawanka ya sami tagomashi a idonka, bari ka aike ni in tafi ƙasar Yahuda, birnin da aka binne kakannina, domin in sāke gina shi.”
6 Da sagde Kongen og Dronningen, som sad hos ham, til mig: Hvor længe skal din Rejse vare, og naar vil du komme igen? Og det syntes Kongen godt, og han sendte mig hen, og jeg satte ham en bestemt Tid.
Sai sarki, a lokacin sarauniya da tana zama kusa da shi, ya tambaye ni, ya ce, “Kwana nawa tafiyar za tă ɗauke ka, kuma yaushe za ka dawo?” Ya gamshi sarki ya aike ni; saboda haka na shirya lokaci.
7 Og jeg sagde til Kongen: Dersom det synes Kongen godt, da lad dem give mig Breve til Landshøvdingerne paa hin Side Floden, at de lade mig komme frem, indtil jeg kommer til Juda,
Na kuma ce masa, “In ya gamshi sarki, zai yi kyau in sami wasiƙu zuwa ga gwamnonin Kewayen Kogin Yuferites, domin su tanada kāriya har sai na isa Yahuda?
8 og Brev til Asaf, som har Opsyn over Kongens Lysthave, at han maa give mig Træ til at sammentømre Porten paa Borgen, som hører til Huset, og ligeledes til Stadsmurene og til det Hus, som jeg skal drage ind udi; og Kongen gav mig det, efterdi min Guds gode Haand var over mig.
A kuma ba ni wasiƙa zuwa ga Asaf, sarkin daji, yă ba ni katako don yin ƙofofin kagara na kusa da fadar haikali da kuma don katangar birni, da na wurin da zan zauna?” Sarki kuwa ya ba ni abin da na roƙa, gama Allah yana tare da ni.
9 Da kom jeg til Landshøvdingerne paa hin Side Floden og gav dem Kongens Breve, og Kongen sendte Stridshøvedsmænd og Ryttere med mig.
Saboda haka na tafi wurin gwamnonin Kewayen Kogin Yuferites, na ba su wasiƙun sarki. Sarki kuma ya aika da hafsoshin mayaƙa da kuma mahayan dawakai tare da ni.
10 Men der Sanballat, Horoniten, og Tobia, den ammonitiske Tjener, hørte det, da gjorde det dem saare ondt, at der var kommet et Menneske til at søge Israels Børns Bedste.
Da Sanballat mutumin Horon da Tobiya wakilin ƙasar Ammon suka ji cewa wani ya zo domin yă ƙarfafa zaman lafiyar mutanen Isra’ila, sai suka damu ƙwarai.
11 Og der jeg kom til Jerusalem og havde været der i tre Dage,
Sai na je Urushalima, bayan na zauna a can na kwanaki uku,
12 da gjorde jeg mig rede om Natten, jeg og faa Mænd med mig, og jeg gav ikke til Kende for noget Menneske, hvad min Gud indgav mit Hjerte at gøre for Jerusalem, og der var intet Dyr med mig uden det Dyr, som jeg red paa.
sai na fita da dare tare da mutane kalila. Ban faɗa wa wani abin da Allahna ya sa a zuciyata in yi don Urushalima ba. Ba waɗansu dabbobi kuma tare da ni, sai dai dabbar da na hau.
13 Og jeg drog ud ad Dalporten om Natten og hen imod Dragekilden og hen til Møgporten, og jeg undersøgte Jerusalems Mure, som vare nedrevne, og dens Porte, som vare fortærede af Ild.
Da dare na fita ta Ƙofar Kwari wajen Rijiyar Dila da Ƙofar Juji, ina dudduba katangar Urushalima waɗanda aka rushe da kuma ƙofofinta waɗanda aka ƙone da wuta.
14 Og jeg drog over til Kildeporten og til Kongens Dam, og der var ikke Rum for Dyret til at komme frem under mig.
Sa’an nan na ci gaba zuwa wajen Ƙofar Maɓuɓɓuga da kuma Tafkin Sarki, amma babu isashen wuri saboda abin da na hau yă bi;
15 Og jeg drog om Natten op i Dalen, og jeg undersøgte Muren, og jeg vendte om og kom ind ad Dalporten og vendte tilbage.
saboda haka na haura ta kwarin da dad dare, ina dudduba katangar. A ƙarshe, na juya na sāke shiga ta Ƙofar Kwari.
16 Og Forstanderne vidste ikke, hvor jeg var gaaet hen, eller hvad jeg gjorde, og for Jøderne og Præsterne og de ypperste og Forstanderne og de øvrige, som skulde have med Gerningen at gøre, havde jeg ikke hidindtil tilkendegivet det.
Shugabanni ba su san inda na tafi, ko abin da nake yi ba, domin ban riga na faɗa wa Yahudawa, ko firistoci, ko manyan gari, ko shugabanni, ko sauran waɗanda za su yi aiki, kome ba.
17 Da sagde jeg til dem: I se den Ulykke, i hvilken vi ere, at Jerusalem er øde, og dens Porte ere opbrændte af Ild: Kommer og lader os opbygge Jerusalems Mure, at vi ikke ydermere skulle være til Spot.
Sai na ce musu, “Kun ga matsalar da muke ciki, yadda Urushalima ta zama kango, an kuma ƙone ƙofofinta da wuta. Ku zo mu sāke gina katangar Urushalima, ba za mu ƙara shan kunya ba.”
18 Og jeg fortalte dem om min Guds Haand, som var god over mig, tilmed om Kongens Ord, som han havde sagt mig; og de sagde: Lader os gøre os rede og bygge, og de styrkede deres Hænder til det gode Værk.
Na kuma faɗa musu game da yadda alherin Allahna yake tare da ni da kuma abin da sarki ya faɗa mini. Suka amsa, suka ce, “Mu tashi, mu kama gini.” Sai suka fara wannan aiki mai kyau.
19 Men der Sanballat, Horoniten, og Tobia, den ammonitiske Tjener, og Gesem, Araberen, hørte det, da bespottede de os og foragtede os, og de sagde: Hvad er dette for en Ting, som I gøre? ville I være genstridige imod Kongen?
Amma sa’ad da Sanballat mutumin Horon da Tobiya wakilin ƙasar Ammon da kuma Geshem mutumin Arab suka ji game da wannan, sai suka yi mana ba’a suka kuma yi mana dariya. Suka ce, “Me kuke tsammani kuke yi? Kuna so ku yi wa sarki tawaye ne?”
20 Da svarede jeg dem og sagde til dem: Gud i Himmelen, han skal lade det lykkes for os, og vi hans Tjenere, vi ville gøre os rede og bygge; men I have ikke Del eller Ret eller Ihukommelse i Jerusalem.
Na amsa musu na ce, “Allah na sama zai ba mu nasara. Mu bayinsa za mu tashi mu fara gini, amma game da ku kam, ba ku da rabo cikin Urushalima, ba ku da wani hakki ko wani abin tunawa.”

< Nehemias 2 >