< Mikas 7 >
1 Ve mig! thi det er gaaet mig som ved Indsamlingen af Sommerfrugt, som ved Eftersankningen efter Vinhøsten; der er ikke en Vindrue til at æde, ingen tidlig moden Figen, som min Sjæl havde Lyst til.
Tawa ta ƙare! Ina kama da wanda yake tattara’ya’yan itatuwa a lokacin kalar’ya’yan inabi; babu sauran nonon inabin da za a tsinka a ci, babu kuma’ya’yan ɓaure na farko-farkon da raina yake marmari.
2 Den fromme er forsvunden fra Jorden, og der er ikke en oprigtig iblandt Menneskene: De lure alle efter Blod, jage den ene deji anden i Garnet.
An kawar da masu tsoron Allah daga ƙasar; babu sauran mai adalcin da ya rage. Dukan mutane suna kwanto don su zub da jini; kowa yana farautar ɗan’uwansa da tarko.
3 Til det onde ere Hænder rede for at gøre det til Gavns; Fyrsten gør Fordring, og Dommeren er villig for Gentjeneste, og den mægtige udtaler sin Sjæls Attraa, og saa sno de det sammen.
Dukan hannuwansu sun gwaninta wajen yin mugunta; shugabanni suna nema a ba su kyautai, alƙalai suna nema a ba su cin hanci, masu iko suna faɗar son zuciyarsu, duk suna ƙulla makirci tare.
4 Den bedste af dem er som Torn, den oprigtigste som et Tjørnegærde; dine Vægteres Dag, din Hjemsøgelse kommer; nu skal deres Forstyrrelse være der.
Mafi kyau a cikinsu yana kama da ƙaya, mafi gaskiyarsu ya fi shingen ƙaya muni. Ranar da Allah zai ziyarce ku ta zo, ranar da masu gadinku za su hura ƙaho. Yanzu ne lokacin ruɗewarku.
5 Tror ikke paa en Ven, forlader eder ikke paa en fortrolig: Var din Munds Døre for hende, som ligger ved din Barm.
Kada ka yarda da maƙwabci; kada ka sa begenka ga abokai. Ko ma wadda take kwance a ƙirjinka, ka yi hankali da kalmominka.
6 Thi Sønnen ringeagter Faderen, Datteren sætter sig op imod sin Moder, Sønnens Hustru imod sin Mands Moder, en Mand har Fjender i sine egne Husfolk.
Gama ɗa yakan ce wannan ba mahaifinsa ba ne, diya kuma takan tayar wa mahaifiyarta, matar ɗa takan yi gāba da uwar mijinta, abokan gāban mutum su ne iyalin cikin gidansa.
7 Men jeg vil skue ud efter Herren, jeg vil bie efter min Frelses Gud; min Gud vil høre mig.
Amma game da ni, zan sa bege ga Ubangiji, ina sauraron Allah Mai Cetona; Allahna kuwa zai ji ni.
8 Glæd dig ikke over mig, min Modstanderinde! thi er jeg falden, skal jeg staa op igen, og sidder jeg i Mørket, skal Herren være mit Lys.
Kada ku yi farin ciki, ku maƙiyana! Ko da yake na fāɗi, zan tashi. Ko da yake na zauna a cikin duhu, Ubangiji zai zama haskena.
9 Herrens Vrede vil jeg bære, thi jeg har syndet imod ham, — indtil han udfører min Sag og skaffer mig Ret; han skal føre mig ud til Lyset, jeg skal skue hans Retfærdighed.
Domin na yi masa zunubi, zan fuskanci fushin Ubangiji, har sai ya dubi batuna ya kuma tabbatar da’yancina. Zai kawo ni zuwa wurin haske; zan ga adalcinsa.
10 Og min Modstanderinde maa se det, og Skam skal bedække hende, idet hun siger til mig: Hvor er Herren din Gud? mine Øjne skulle se deres Lyst paa hende; nu skal hun blive til at nedtrædes som Dynd paa Gader.
Sa’an nan maƙiyina zai gani yă kuma sha kunya, shi da yake ce da ni “Ina Ubangiji Allahnka?” Zai gani, yă kuma ji kunya. Ko yanzu ma za a tattake shi kamar taɓo a tituna.
11 Der kommer en Dag, da man skal bygge dine Mure; paa denne Dag skal Grænse være fjern.
Ranar gina katangarka tana zuwa, a ranar za a fadada iyakokinka.
12 Paa den Dag, da skal man komme til dig lige fra Assur og Ægyptens Stæder, og lige fra Ægypten og indtil Floden, og til Hav fra Hav, og fra Bjerg til Bjerget.
A wannan rana mutane za su zo gare ka daga Assuriya da kuma biranen Masar, daga Masar ma har zuwa Yuferites daga teku zuwa teku, kuma daga dutse zuwa dutse.
13 Og Jorden skal blive til Øde for sine Beboeres Skyld, formedelst deres Idrætters Frugt.
Duniya za tă zama kufai saboda mazaunanta, saboda ayyukansu.
14 Vogt med din Stav dit Folk, din Arvs Hjord, som bor ene for sig, i Skoven midt paa Karmel; lad dem græsse i Basan og Gilead som i gamle Dage!
Ka yi kiwon mutanenka da sandarka, garken gādonka, wanda yake zaune shi kaɗai a kurmi, a ƙasa mai kyau ta kiwo, bari su yi kiwo a Bashan da Gileyad kamar a kwanakin dā.
15 Som i de Dage, da du drog ud af Ægyptens Land, vil jeg lade det se underfulde Ting.
“Kamar a kwanakin da kuka fito daga Masar, zan nuna musu al’ajabaina.”
16 Hedningerne skulle se det og beskæmmes for al deres Vælde; de skulle lægge Haand paa Mund; deres Øren skulle blive døve.
Al’ummai za su gani su kuma ji kunya, za a kuma ƙwace musu dukan ikonsu. Za su kama bakinsu kunnuwansu kuma za su zama kurame.
17 De skulle slikke Støv som Slangen, som Jordens Kryb skulle de komme bævende frem fra deres Borge; til Herren vor Gud skulle de skælvende komme og frygte for dig.
Za su lashi ƙura kamar maciji, kamar dabbobi masu rarrafe a ƙasa. Za su fito daga maɓuyarsu da rawan jiki, za su juya cikin tsoro ga Ubangiji Allahnmu su kuma ji tsoronku.
18 Hvo er en Gud som du, der borttager Misgerning og gaar Overtrædelse forbi for det overblevne af sin Arv? han holder ikke fast ved sin Vrede evindelig, thi han har Lyst til Miskundhed.
Wane ne Allah kamar ka, wanda yake yafe zunubi yă kuma gafarta laifofin mutanensa da suka ragu? Ba ka zama mai fushi har abada amma kana marmari ka nuna jinƙai.
19 Han skal atter forbarme sig over os, han skal træde vore Misgerninger under Fødder; og du skal kaste alle deres Synder i Havets Dyb.
Za ka sāke jin tausayinmu; za ka tattake zunubanmu a ƙarƙashin sawunka ka kuma tura dukan kurakuranmu zuwa cikin zurfafan teku.
20 Du skal bevise Jakob Sandhed, Abraham Miskundhed, som du har svoret vore Fædre fra de gamle Dage af.
Za ka yi wa Yaƙub aminci, ka kuma nuna jinƙai ga Ibrahim, kamar yadda ka yi alkawari da rantsuwa ga kakanninmu tun a kwanankin dā.