< Mikas 4 >
1 Men det skal ske i de sidste Dage, at Herrens Hus's Bjerg skal være grundfæstet oven paa Bjergene og ophøjet over Højene, og Folkene skulle strømme til det.
A kwanakin ƙarshe za a kafa dutsen haikalin Ubangiji yă zama babba a cikin duwatsu. Za a ɗaga shi sama da tuddai, mutane kuma za su riƙa ɗunguma zuwa gare shi.
2 Og mange Hedninger skulle komme og sige: Kommer og lader os gaa op til Herrens Bjerg og til Jakobs Guds Hus, at han maa lære os sine Veje, og vi maa vandre paa hans Stier; thi fra Zion skal udgaa Lov og Herrens Ord fra Jerusalem.
Al’ummai da yawa za su zo su ce, “Ku zo, bari mu haura zuwa dutsen Ubangiji, zuwa gidan Allah na Yaƙub. Zai koya mana hanyoyinsa, don mu yi tafiya cikin hanyoyinsa.” Doka za tă fita daga Sihiyona, maganar Ubangiji kuma daga Urushalima.
3 Og han skal dømme imellem mange Folkeslag og holde Ret for vældige Hedningefolk ud i det fjerne; og de skulle omsmede deres Sværd til Hakker og deres Spyd til Haveknive, et Folk skal ikke løfte Sværd imod et andet, og de skulle ikke ydermere øve sig i. Krig.
Zai shari’anta tsakanin mutane yă kuma sulhunta tsakanin manyan al’ummai nesa da kuma kusa. Har su mai da takubansu su zama garemani, māsunsu kuma su zama wuƙaƙen askin itace. Al’umma ba za tă ɗauki takobi gāba da wata al’umma ba, ko a yi horarwa don yaƙi.
4 Men de skulle bo, hver under sit Vintræ og under sit Figentræ, og ingen skal forfærde dem; thi den Herre Zebaoths Mund har talt.
Kowa zai zauna a tushen kuringar inabinsa da tushen ɓaurensa, kuma ba wanda zai tsoratar da su, gama Ubangiji Maɗaukaki ne ya faɗa.
5 Thi alle Folk vandre hvert i sin Guds Navn; men vi vandre i Herrens vor Guds Navn, evindelig og altid.
Dukan al’ummai za su iya tafiya a cikin sunan allolinsu; mu dai za mu yi tafiya a cikin sunan Ubangiji Allahnmu har abada abadin.
6 Paa denne Dag, siger Herren, vil jeg sanke det haltende og samle det fordrevne og det, som jeg har handlet ilde med.
“A wannan rana,” in ji Ubangiji, “zan tattara guragu; zan kuma tara masu zaman bauta, da waɗanda na sa suka damu.
7 Og jeg vil gøre det haltende til en Levning og det bortkomne til et stærkt Folk; og Herren skal regere over dem paa Zions Bjerg, fra nu og indtil Evighed.
Zan mai da guragu su zama raguwa, waɗanda aka kora, su zama al’umma mai ƙarfi. Ubangiji zai yi mulkinsu a Dutsen Sihiyona daga wannan rana da kuma har abada.
8 Og du, Hyrdetaarn, Zions Datters Høj! til dig skal det komme; ja, komme skal det tidligere Herredømme, Kongedømmet over Jerusalems Datter.
Game da ke, ya hasumiyar tsaron garke, Ya mafaka Diyar Sihiyona, za a maido miki da mulkinki na dā, sarauta kuma za tă zo wa Diyar Urushalima.”
9 Nu, hvorfor raaber du saa saare? er der ingen Konge udi dig? eller er din Raadgiver omkommen? thi Smerte har betaget dig som den fødende Kvinde.
Don me yanzu kike kuka da ƙarfi, ba ki da sarki ne? Masu shawararki sun hallaka ne, da zafi ya cika ki kamar mace mai naƙuda?
10 Vrid dig, og vaand dig i Smerte, du Zions Datter som den fødende Kvinde! thi nu skal du drage ud af Staden og bo paa Marken og komme lige til Babel; der skal du udfries, der skal Herren genløse dig af dine Fjenders Haand.
Ki yi birgima cikin zafin azaba, ya Diyar Sihiyona, kamar macen da take naƙuda, don yanzu dole ki bar birni ki kafa sansani a filin Allah. Za ki tafi Babilon; a can za a kuɓutar da ki. A can ne Ubangiji zai fanshe ki daga hannun maƙiyanki.
11 Og nu ere vel mange Folkefærd samlede imod dig, hvilke sige: Hun vorde vanhelliget! og vore Øjne se deres Lyst paa Zion!
Amma yanzu al’ummai da yawa suna gāba da ke. Suna cewa, “Bari a ƙazantar da ita, bari mu zuba wa Sihiyona ido.”
12 Men de kende ikke Herrens Tanker og forstaa ikke hans Raad, thi han har samlet dem som Neg til Tærskepladsen.
Amma ba su san tunanin Ubangiji ba; ba su fahimci shirinsa ba, shi da ya tattara su kamar dammuna a masussuka.
13 Gør dig rede og tærsk, du Zions Datter! thi jeg gør dit Horn til Jern og gør dine Hove til Kobber, at du maa sønderknuse mange Folk, og at jeg kan vie Herren deres Bytte og hele Jordens Herre deres Gods.
“Ki tashi ki yi sussuka, ya Diyar Sihiyona, gama zan ba ki ƙahonin ƙarfe; zan ba ki kofatan tagulla domin ki ragargaje al’ummai masu yawa.” Za ki ba Ubangiji dukan dukiyarsu da suka tara ta hanyar zamba, wadatarsu kuma ga Ubangiji dukan duniya.