< Mikas 3 >

1 Og jeg sagde: Hører dog, I Jakobs Øverster og Israels Hus's Dommere! burde I ikke kende Retten?
Sa’an nan na ce, “Ku kasa kunne, ku shugabannin Yaƙub, ku masu mulkin gidan Isra’ila. Ya kamata ku san shari’a,
2 De hade det gode og elske det onde; de rive deres Hud af dem og deres Kød af deres Ben.
ku da kuke ƙin abu mai kyau kuke ƙaunar mugunta, ku da kuke feɗe mutanena kuke tuge nama daga ƙasusuwansu;
3 Det er dem, som æde mit Folks Kød og drage deres Hud af dem og bryde deres Ben, og de brede dem ud som i en Gryde og som Kød midt i en Kedel.
ku da kuke cin naman mutanena, ku feɗe fatar jikinsu kuke kakkarya ƙasusuwansu, kuke yayyanka su gunduwa-gunduwa kamar naman da za a toya, kamar naman da za a sa a dafa.”
4 Da skulle de raabe til Herren, og han skal ikke bønhøre dem; men han skal skjule sit Ansigt for dem paa den Tid, eftersom de have gjort ilde i deres Idrætter.
Sa’an nan za su kira ga Ubangiji, amma ba zai amsa musu ba. A wannan lokaci zai ɓoye fuskarsa daga gare su saboda irin muguntar da suka yi.
5 Saa siger Herren imod Profeterne, som forvilde mit Folk, og som, naar de faa noget at bide med deres Tænder, forkynde Fred, men naar nogen intet giver dem for deres Mund, da prædike de Krig imod ham:
Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “Game da annabawa masu ɓad da mutanena, in wani ya ciyar da su, sai su ce akwai ‘salama’ amma in bai ciyar da su ba, a shirye suke su kai masa hari.
6 Derfor skal det blive Nat for eder, uden Syner, og Mørke for eder; uden Spaadom; og Solen skal gaa ned over Profeterne, og Dagen skal blive sort over dem.
Saboda haka dare yana zuwa a bisanku, ba tare da wahayi ba, kuma duhu, ba tare da duba ba. Rana za tă fāɗi wa annabawa, yini kuma zai zama musu duhu.
7 Og Seerne skulle beskæmmes og Spaamændene blive til Skamme, og de skulle skjule Skægget over Munden alle sammen; thi der er intet Svar fra Gud.
Masu gani za su ji kunya, masu duba kuma za su ji taƙaici. Dukansu za su rufe fuskokinsu gama ba amsa daga Allah.”
8 Men jeg er derimod fuld af Kraft, Herrens Aand, og af Ret og Styrke til at kundgøre Jakob hans Overtrædelse og Israel hans Synd.
Amma game da ni, ina cike da iko ta wurin Ruhun Ubangiji da kuma adalci da ƙarfi, don a sanar da Yaƙub laifofinsa, ga Isra’ila kuma zunubinsa.
9 Hører dog dette, I Jakobs Hus's Øverster og Israels Hus's Dommere! I, som afsky Ret og gøre det lige kroget!
Ku ji wannan, ku shugabannin gidan Yaƙub, ku masu mulkin gidan Isra’ila, ku da kuke ƙyamar gaskiya, kuka karkatar duk abin da yake na gaskiya;
10 Hver, som bygger Zion med Blod og Jerusalem med Uretfærdighed!
kuka gina Sihiyona ta wurin zub da jini, Urushalima kuma ta wurin mugunta.
11 Dens Øverster dømmes for Skænk, og dens Præster lære for Betaling, og dens Profeter spaa for Penge; dog forlade de sig fast paa Herren, sigende: Er ikke Herren midt iblandt os? der skal ikke komme Ulykker over os.
Hukunce-hukuncen shugabannin ƙasar na cin hanci ne, firistocinta kuma suna koyarwa don a biya su, annabawanta kuwa suna yin annabci don neman kuɗi. Duk da haka suna jingina a kan Ubangiji suna cewa, “Ba Ubangiji yana tare da mu ba? Ba bala’in da zai zo mana.”
12 Derfor, for eders Skyld, skal Zion pløjes som en Ager og Jerusalem blive til Stenhobe og Husets Bjerg til Skovhøje.
Don haka, saboda ku, za a nome Sihiyona kamar gona, Urushalima kuma ta zama tarin juji, tudun haikali kuwa zai zama kurmin ƙayayyuwa.

< Mikas 3 >