< Matthæus 2 >

1 Men da Jesus var født i Bethlehem i Judæa, i Kong Herodes's Dage, se, da kom der vise fra Østerland til Jerusalem og sagde:
Bayan an haifi Yesu a Betlehem, a Yahudiya, a zamanin Sarki Hiridus, sai waɗansu Masana, daga gabas suka zo Urushalima
2 „Hvor er den Jødernes Konge, som er født? thi vi have set hans Stjerne i Østen og ere komne for at tilbede ham.”
suka yi tambaya suka ce, “Ina shi wanda aka haifa sarkin Yahudawa? Gama mun ga tauraronsa a gabas mun kuwa zo ne domin mu yi masa sujada.”
3 Men da Kong Herodes hørte det, blev han forfærdet, og hele Jerusalem med ham;
Da Sarki Hiridus ya ji wannan, sai hankalinsa ya tashi haka ma na dukan Urushalima.
4 og han forsamlede alle Folkets Ypperstepræster og skriftkloge og adspurgte dem, hvor Kristus skulde fødes.
Bayan ya kira dukan manyan firistoci da malaman dokoki na mutane wuri ɗaya, sai ya tambaye su inda za a haifi Kiristi.
5 Og de sagde til ham: „I Bethlehem i Judæa; thi saaledes er der skrevet ved Profeten:
Suka amsa suka ce, “A Betlehem ne, cikin Yahudiya, gama haka annabin ya rubuta.
6 Og du, Bethlehem i Judas Land, er ingenlunde den mindste iblandt Judas Fyrster; thi af dig skal der udgaa en Fyrste, som skal vogte mit Folk Israel.”
“‘Amma ke Betlehem, a cikin ƙasar Yahuda, ba ke ce mafi ƙanƙanta a cikin masu mulki a Yahuda ba, gama daga cikinki mai mulki zai zo, wanda zai zama makiyayin mutanena Isra’ila.’”
7 Da kaldte Herodes hemmeligt de vise og fik af dem nøje Besked om Tiden, da Stjernen havde ladet sig til Syne.
Sai Hiridus ya kira Masanan nan a ɓoye, yă gano daga wurinsu daidai lokacin da tauraron ya bayyana.
8 Og han sendte dem til Bethlehem og sagde: „Gaar hen og forhører eder nøje om Barnet; men naar I have fundet det, da forkynder mig det, for at ogsaa jeg kan komme og tilbede det.”
Sai ya aike su Betlehem ya ce, “Ku je ku binciko a hankali game da yaron nan. Da kun same shi, sai ku kawo mini labari nan da nan, domin ni ma in je in yi masa sujada.”
9 Men da de havde hørt Kongen, droge de bort; og se, Stjernen, som de havde set i Østen, gik foran dem, indtil den kom og stod oven over, hvor Barnet var.
Bayan sun saurari sarki, sai suka kama hanyarsu, tauraron da suka gani a gabas kuwa yana tafe a gabansu, sai da ya kai inda yaron yake.
10 Men da de saa Stjernen, bleve de saare meget glade.
Da suka ga tauraron, sai suka yi farin ciki ƙwarai.
11 Og de gik ind i Huset og saa Barnet med dets Moder Maria og faldt ned og tilbade det og oplode deres Gemmer og ofrede det Gaver, Guld og Røgelse og Myrra.
Suka shiga gidan, suka kuwa ga yaron tare da mahaifiyarsa Maryamu. Suka durƙusa har ƙasa, suka yi masa sujada. Sa’an nan suka kunce dukiyarsu, suka miƙa masa kyautai na zinariya da na turare da na mur.
12 Og da de vare blevne advarede af Gud i en Drøm, at de ikke skulde vende tilbage til Herodes, droge de ad en anden Vej tilbage til deres Land.
Bayan an gargaɗe su cikin mafarki kada su koma wurin Hiridus, sai suka koma ƙasarsu ta wata hanya dabam.
13 Men da de vare dragne bort, se, da viser en Herrens Engel sig i en Drøm for Josef og siger: „Staa op, og tag Barnet og dets Moder med dig og fly til Ægypten og bliv der, indtil jeg siger dig til; thi Herodes vil søge efter Barnet for at dræbe det.”
Bayan sun tafi, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa, ku gudu zuwa Masar. Ku zauna a can sai na gaya muku, gama Hiridus zai nemi yaron don yă kashe.”
14 Og han stod op og tog Barnet og dets Moder med sig om Natten og drog bort til Ægypten.
Sai Yusuf ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa da dad dare suka tafi Masar,
15 Og han var der indtil Herodes's Død, for at det skulde opfyldes, som er talt af Herren ved Profeten, der siger: „Fra Ægypten kaldte jeg min Søn.”
inda ya zauna har sai da Hiridus ya mutu. Ta haka kuwa aka cika abin da Ubangiji ya faɗa ta bakin annabin cewa, “Daga Masar na kira ɗana.”
16 Da Herodes nu saa, at han var bleven skuffet af de vise, blev han saare vred og sendte Folk hen og lod alle Drengebørn ihjelslaa, som vare i Bethlehem og i hele dens Omegn, fra to Aar og derunder, efter den Tid, som han havde faaet Besked om af de vise.
Da Hiridus ya gane cewa Masanan nan sun yi masa wayo, sai ya husata ƙwarai, ya yi umarni cewa a karkashe dukan’yan yara maza da suke a Betlehem da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa ƙasa, bisa ga lokacin da ya sami labarin daga Masanan nan.
17 Da blev det opfyldt, som er talt ved Profeten Jeremias, som siger:
Sai abin da aka faɗa ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa,
18 „En Røst blev hørt i Rama, Graad og megen Jamren; Rakel græd over sine Børn og vilde ikke lade sig trøste, thi de ere ikke mere.”
“An ji murya a Rama, tana kuka da makoki mai tsanani, Rahila ce take kuka domin’ya’yanta, an kāsa ta’azantar da ita, don ba su.”
19 Men da Herodes var død, se, da viser en Herrens Engel sig i en Drøm for Josef i Ægypten og siger:
Bayan Hiridus ya mutu, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki a Masar,
20 „Staa op, og tag Barnet og dets Moder med dig, og drag til Israels Land; thi de ere døde, som efterstræbte Barnets Liv.”
ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa ku tafi ƙasar Isra’ila, domin waɗanda suke neman ran yaron sun mutu.”
21 Og han stod op og tog Barnet og dets Moder med sig og kom til Israels Land.
Sai ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa suka tafi ƙasar Isra’ila.
22 Men da han hørte, at Arkelaus var Konge over Judæa i sin Fader Herodes's Sted, frygtede han for at komme derhen; og han blev advaret af Gud i en Drøm og drog bort til Galilæas Egne.
Amma da ya ji Arkelawus ne yake mulki a Yahudiya a matsayin wanda ya gāji mahaifinsa Hiridus, sai ya ji tsoron zuwa can. Bayan an gargaɗe shi a mafarki, sai ya ratse zuwa gundumar Galili,
23 Og han kom og tog Bolig i en By, som kaldes Nazareth, for at det skulde opfyldes, som er talt ved Profeterne, at han skulde kaldes Nazaræer.
ya je ya zauna a wani garin da ake kira Nazaret. Ta haka aka cika abin da aka faɗa ta bakin annabawa cewa, “Za a ce da shi Banazare.”

< Matthæus 2 >