< Matthæus 11 >

1 Og det skete, da Jesus var færdig med at give sine tolv Disciple Befaling, gik han videre derfra for at lære og prædike i deres Byer.
Bayan Yesu ya gama yi wa almajiransa sha biyun nan umarni, sai ya yi gaba daga can don yă koyar yă kuma yi wa’azi a garuruwan Galili.
2 Men da Johannes hørte i Fængselet om Kristi Gerninger, sendte han Bud med sine Disciple og lod ham sige:
Sa’ad da Yohanna Mai Baftisma ya ji a kurkuku abin da Kiristi yake yi, sai ya aiki almajiransa
3 „Er du den, som kommer, eller skulle vi vente en anden?”
su tambaye shi, “Kai ne wanda zai zo, ko kuwa mu sa ido ga wani?”
4 Og Jesus svarede og sagde til dem: „Gaar hen, og forkynder Johannes de Ting, som I høre og se:
Yesu ya amsa ya ce, “Ku koma ku gaya wa Yohanna abin da kuka ji, kuka kuma gani.
5 blinde se, og lamme gaa, spedalske renses, og døve høre, og døde staa op, og Evangeliet forkyndes for fattige;
Makafi suna gani, guragu suna tafiya, ana warkar da waɗanda suke da kuturta, kurame suna ji, ana tā da matattu, ana kuma yi wa matalauta wa’azin labari mai daɗi.
6 og salig er den, som ikke forarges paa mig.”
Mai albarka ne mutumin da bai yi tuntuɓe ba saboda ni.”
7 Men da disse gik bort, begyndte Jesus at sige til Skarerne om Johannes: „Hvad gik I ud i Ørkenen at skue? Et Rør, som bevæges hid og did af Vinden?
Sa’ad da almajiran Yohanna suke barin wurin, sai Yesu ya fara yi wa taron magana game da Yohanna. “Me kuka je kallo a hamada? Ciyawar da iska take kaɗawa ne?
8 Eller hvad gik I ud at se? Et Menneske, iført bløde Klæder? Se, de, som bære bløde Klæder, ere i Kongernes Huse.
In ba haka ba, to, me kuka je kallo? Mutum mai sanye da riguna masu kyau ne? A’a, masu sa riguna masu kyau, ai, a fadan sarakuna suke.
9 Eller hvad gik I ud at se? En Profet? Ja, siger jeg eder, endog mere end en Profet.
To, me kuka je kallo ne? Annabi? I, ina gaya muku, ya ma fi annabi.
10 Thi han er den, om hvem der er skrevet: Se, jeg sender min Engel for dit Ansigt, han skal berede din Vej foran dig.
Wannan shi ne wanda aka rubuta game da shi cewa, “‘Zan aiki ɗan saƙona yă sha gabanka, wanda zai shirya hanyarka a gabanka.’
11 Sandelig, siger jeg eder, iblandt dem, som ere fødte af Kvinder, er ingen større fremstaaet end Johannes Døberen; men den mindste i Himmeriges Rige er større end han.
Gaskiya nake gaya muku. A cikin dukan waɗanda mata suka haifa, ba wani da ya taso da ya fi Yohanna Mai Baftisma girma; duk da haka mafi ƙanƙanta a mulkin sama ya fi shi girma.
12 Men fra Johannes Døberens Dage indtil nu tages Himmeriges Rige med Vold, og Voldsmænd rive det til sig.
Tun daga kwanakin Yohanna Mai Baftisma har yă zuwa yanzu, mulkin sama yana sha da ƙyar, fitanannu kuma sun kama mulkin sama sun riƙe gam.
13 Thi alle Profeterne og Loven have profeteret indtil Johannes.
Gama dukan Annabawa da kuma Doka sun yi ta annabci har yă zuwa kan Yohanna.
14 Og dersom I ville tage imod det: Han er Elias, som skal komme.
In kuna niyya ku yarda da wannan, to, shi ne Iliya da dā ma zai zo.
15 Den, som har Øren at høre med, han høre!
Duk mai kunnen ji, yă ji.
16 Men hvem skal jeg ligne denne Slægt ved? Den ligner Børn, som sidde paa Torvene og raabe til de andre og sige:
“Da me zan kwatanta wannan zamani? Suna kama da yara da suke zaune a kasuwa, suna kiran juna, suna cewa,
17 Vi blæste paa Fløjte for eder, og I dansede ikke; vi sang Klagesange, og I jamrede ikke.
“‘Mun yi muku busa, ba ku kuwa yi rawa ba, mun rera waƙar makoki, ba ku kuwa yi makoki ba.’
18 Thi Johannes kom, som hverken spiste eller drak, og de sige: Han er besat.
Gama Yohanna Mai Baftisma ya zo ba ya ciye-ciye, ba ya shaye-shaye, sai suka ce, ‘Ai, yana da aljani.’
19 Menneskesønnen kom, som spiser og drikker, og de sige: Se, en Fraadser og en Vindranker, Tolderes og Synderes Ven! Dog, Visdommen er retfærdiggjort ved sine Børn.”
Ɗan Mutum ya zo yana ciye-ciye, yana shaye-shaye, sai suka ce, ‘Ga mai haɗama da kuma mashayi, abokin masu karɓar haraji da masu zunubi.’ Amma akan tabbatar da hikima ta wurin ayyukanta.”
20 Da begyndte han at skamme de Byer ud, i hvilke hans fleste kraftige Gerninger vare gjorte, fordi de ikke havde omvendt sig:
Sai Yesu ya fara yin tir da biranen da aka yi yawancin ayyukansa na banmamaki, don ba su tuba ba.
21 „Ve dig, Korazin! ve dig, Bethsajda! thi dersom de kraftige Gerninger, som ere skete i eder, vare skete i Tyrus og Sidon, da havde de for længe siden omvendt sig i Sæk og Aske.
“Kaitonki, Korazin! Kaitonki, Betsaida! Da a ce ayyukan banmamakin da aka yi a cikinki ne aka yi a Taya da Sidon, da tuni sun tuba sanye da rigar makoki da toka.
22 Men jeg siger eder: Det skal gaa Tyrus og Sidon taaleligere paa Dommens Dag end eder.
Amma ina gaya muku, za a fi jin tausayin Taya da Sidon a ranar shari’a, fiye da ku.
23 Og du, Kapernaum! som er bleven ophøjet indtil Himmelen, du skal nedstødes indtil Dødsriget; thi dersom de kraftige Gerninger, som ere skete i dig, vare skete i Sodoma, da var den bleven staaende indtil denne Dag. (Hadēs g86)
Ke kuma Kafarnahum, za a ɗaga ki sama ne? A’a, za ki gangara zuwa zurfafa ne. Da a ce ayyukan banmamakin da aka yi a cikinki ne a aka yi a Sodom, da tana nan har yă zuwa yau. (Hadēs g86)
24 Men jeg siger eder: Det skal gaa Sodomas Land taaleligere paa Dommens Dag end dig.”
Amma ina gaya miki, za a fi jin tausayin Sodom fiye da ke a ranar shari’a.”
25 Paa den Tid udbrød Jesus og sagde: „Jeg priser dig, Fader, Himmelens og Jordens Herre! fordi du har skjult dette for vise og forstandige og aabenbaret det for umyndige.
A wannan lokaci sai Yesu ya ce, “Ina yabonka, Uba, Ubangijin sama da ƙasa, gama ka ɓoye waɗannan abubuwa ga masu hikima da masu ilimi, ka kuma bayyana su ga ƙananan yara.
26 Ja, Fader! thi saaledes skete det, som var velbehageligt for dig.
I, Uba, gama wannan shi ne abin da ka ji daɗin yi.
27 Alle Ting ere mig overgivne af min Fader; og ingen kender Sønnen uden Faderen, og ingen kender Faderen uden Sønnen, og den, for hvem Sønnen vil aabenbare ham.
“Dukan kome Ubana ya danƙa mini. Ba wanda ya san Ɗan sai dai Uban, ba kuma wanda ya san Uban, sai dai Ɗan da kuma waɗanda Ɗan ya so yă bayyana musu shi.
28 Kommer hid til mig alle, som lide Møje og ere besværede, og jeg vil give eder Hvile.
“Ku zo gare ni, dukanku da kuka gaji kuke kuma fama da kaya, zan kuwa ba ku hutu.
29 Tager mit Aag paa eder, og lærer af mig; thi jeg er sagtmodig og ydmyg af Hjertet; saa skulle I finde Hvile for eders Sjæle.
Ku ɗauki karkiyata a kanku, ku kuma yi koyi da ni, gama ni mai tawali’u ne marar girman kai, za ku kuwa sami hutu don rayukanku.
30 Thi mit Aag er gavnligt, og min Byrde er let.”
Gama karkiyata mai sauƙi ce, kayana kuma marasa nauyi ne.”

< Matthæus 11 >