< Markus 5 >

1 Og de kom over til hin Side af Søen til Gerasenernes Land.
Da su ka zo daya ketaren tekun, wanda ya ke cikin yankin Garasinawa.
2 Og da han traadte ud af Skibet, kom der ham straks i Møde ud fra Gravene en Mand med en uren Aand.
Sa'adda Yesu ya sauko daga cikin jirgin ruwan sai wani mutum mai aljanu ya fito daga cikin kaburbura ya tarbe shi.
3 Han havde sin Bolig i Gravene, og ingen kunde længer binde ham, end ikke med Lænker.
Mutumin yana zama a cikin kaburbura. An daure shi da sarkoki da mari
4 Thi han havde ofte været bunden med Bøjer og Lænker, og Lænkerne vare sprængte af ham og Bøjerne sønderslidte, og ingen kunde tæmme ham.
An daure shi da sarkoki da mari sau da yawa, amma ya tsuntsunke sarkoki da marin. har ma ba wanda zai iya daure shi kuma.
5 Og han var altid Nat og Dag i Gravene og paa Bjergene, skreg og slog sig selv med Stene.
Dare da rana a cikin kabarbarun da duwatsu mutumin ya na ihu ya na yaiyage jikinsa da duwatsu masu kaifi.
6 Men da han saa Jesus langt borte, løb han hen og kastede sig ned for ham
Sa'adda ya hango Yesu daga nesa, sai ya tarbi Yesu ya durkusa a gabansa.
7 og raabte med høj Røst og sagde: „Hvad har jeg med dig at gøre, Jesus, den højeste Guds Søn? Jeg besværger dig ved Gud, at du ikke piner mig.‟
Ya tada muryarsa da karfi ya ce, ina ruwa na da kai? Yesu Dan Allah Madaukaki Ina rokon ka da sunan Allah kada ka bani wahala,
8 Thi han sagde til ham: „Far ud af Manden, du urene Aand!‟
Gama Yesu ya ce masa kai aljani ka fito daga cikinsa.”
9 Og han spurgte ham: „Hvad er dit Navn?‟ Og han siger til ham: „Legion er mit Navn; thi vi ere mange.‟
Ya tambaye shi, “Yaya sunanka? Ya ce suna na tari gama muna da yawa.
10 Og han bad ham meget om ikke at drive dem ud af Landet.
Ya yi ta rokonsa kada ya raba su da wannan yankin kasar.
11 Men der var der ved Bjerget en stor Hjord Svin, som græssede;
Akwai babban garken aladu a wurin suna kiwo a gindin tsauni.
12 og de bade ham og sagde: „Send os i Svinene, saa vi maa fare i dem.‟
Sai suka roke shi ya bar su su shiga cikin wadannan aladun.
13 Og han tilstedte dem det. Og de urene Aander fore ud og fore i Svinene; og Hjorden styrtede sig ned over Brinken ud i Søen, omtrent to Tusinde, og de druknede i Søen.
Shi kuma ya yardar masu. Aljanun suka fita suka shiga cikin aladun su kimanin dubu biyu. Aladun dubu biyu suka gangaro daga gindin tsaunin suka fada cikin ruwa.
14 Og deres Hyrder flyede og forkyndte det i Byen og paa Landet; og de kom for at se, hvad det var, som var sket.
Mutanen da ke kiwon aladun su ka shiga cikin gari da kewaye suka bada labarin abin da ya faru. Mutane da yawa suka je su ga abin da ya faru
15 Og de komme til Jesus og se den besatte, ham, som havde haft Legionen, sidde paaklædt og ved Samling, og de frygtede.
Sai suka zo wurin Yesu suka ga mutumin mai aljanun a zaune, cikin hankalinsa, saye da tufafi, sai suka tsorata.
16 Men de, som havde set det, fortalte dem, hvorledes det var gaaet den besatte, og om Svinene.
Wadanda suka zo su ka ga abin da ya faru da mutumin mai aljanun, suka je suka fada wa mutane abin da suka gani game da aladun.
17 Og de begyndte at bede ham om, at han vilde gaa bort fra deres Egn.
Mutanen suka roke shi ya fita daga yankin kasarsu.
18 Og da han gik om Bord i Skibet, bad den, som havde været besat, ham om, at han maatte være hos ham.
Shi mutumin da aljanu ke iko da shi, sa'adda ya ga Yesu zai shiga cikin jirgin ruwa ya tafi, ya roki Yesu da ya bi shi.
19 Og han tilstedte ham det ikke, men siger til ham: „Gaa til dit Hus, til dine egne, og forkynd dem, hvor store Ting Herren har gjort imod dig, og at han har forbarmet sig over dig.‟
Amma Yesu bai yarda masa ba. Ya ce masa ka tafi gidanku, wurin mutanenka ka gaya ma su alherin da Ubangiji ya yi maka.
20 Og han gik bort og begyndte at kundgøre i Dekapolis, hvor store Ting Jesus havde gjort imod ham; og alle undrede sig.
Mutumin ya shiga cikin Dikafolis yana shaidar babban abin da Yesu ya yi masa, dukansu suka cika da mamaki.
21 Og da Jesus igen i Skibet var faren over til hin Side, samledes der en stor Skare om ham, og han var ved Søen.
Sa'adda Yesu ya sake ketaren kogin zuwa daya gefen, acikin jirgin, sai taron jama'a suka keweye shi, a gefen tekun.
22 Og der kommer en af Synagogeforstanderne ved Navn Jairus, og da han ser ham, falder han ned for hans Fødder.
Sai wani daya daga cikin shugabannin Majami'a mai suna Yayirus, ya zo, wurinsa sa'adda ya ganshi ya durkusa a gabansa.
23 Og han beder ham meget og siger: „Min lille Datter er paa sit yderste; o! at du vilde komme og lægge Hænderne paa hende, for at hun maa frelses og leve!‟
Ya yi ta rokonsa, yana cewa, “Diya ta ba ta da lafiya har ma ta kusa mutuwa. Ina rokonka mu je gida na ka dora ma ta hannu domin ta warke. ta rayu.”
24 Og han gik bort med ham, og en stor Skare fulgte ham, og de trængte ham.
Sai ya tafi tare da shi, babban taro suka biyo shi har ma suna matse shi.
25 Og der var en Kvinde, som havde haft Blodflod i tolv Aar,
Akwai wata mace wadda ta ke zubar jini ta kai tsawon shekara goma sha biyu.
26 og hun havde døjet meget af mange Læger og havde tilsat alt, hvad hun ejede, og hun var ikke bleven hjulpen, men tværtimod, det var blevet værre med hende.
Ta sha wahala kwarai da gaske ta je wurin likitoci da yawa ta kashe kudi sosai, amma ba ta warke ba abin ma sai karuwa ya ke yi.
27 Da hun havde hørt om Jesus, kom hun bagfra i Skaren og rørte ved hans Klædebon.
Ta ji labarin Yesu. Sai ta biyo bayansa yana tafiya cikin taro, ta taba habar rigarsa.
28 Thi hun sagde: „Dersom jeg rører blot ved hans Klæder, bliver jeg frelst.‟
Domin ta ce “Idan dai na taba ko da habar rigarsa zan warke.”
29 Og straks tørredes hendes Blods Kilde, og hun mærkede i sit Legeme, at hun var bleven helbredet fra sin Plage.
Da dai ta taba shi sai zubar jinin ta ta tsaya, ta ji a jikin ta ta warke, daga damuwarta.
30 Og straks da Jesus mærkede paa sig selv, at den Kraft var udgaaet fra ham, vendte han sig om i Skaren og sagde: „Hvem rørte ved mine Klæder?‟
Nan da nan, Yesu ya ji iko ya fita daga gare shi sai ya ce “wanene ya taba rigata?”
31 Og hans Disciple sagde til ham: „Du ser, at Skaren trænger dig, og du siger: Hvem rørte ved mig?‟
Almajiransa suka ce, “a cikin wannan taron mutane da yawa ka ce wanene ya taba ni?”
32 Og han saa sig om for at se hende, som havde gjort dette.
Amma Yesu ya waiga ya ga ko wanene ya taba shi.
33 Men da Kvinden vidste, hvad der var sket hende, kom hun frygtende og bævende og faldt ned for ham og sagde ham hele Sandheden.
Matar ta san abin da ya faru sai ta zo cikin tsoro da rawar jiki ta durkusa a gaban Yesu ta fada masa gaskiya.
34 Men han sagde til hende: „Datter! din Tro har frelst dig; gaa bort med Fred, og vær helbredet fra din Plage!‟
Sai ya ce da ita, “Diya bangaskiyarki ta warkar da ke, ki tafi lafiya kin sami warkewa daga cutarki”.
35 Endnu medens han talte, komme nogle fra Synagogeforstanderens Hus og sige: „Din Datter er død, hvorfor umager du Mesteren længere?‟
Sa'adda ya ke magana da ita sai ga mutane daga gidan shugaban majami'a suka ce “Diyarka ta mutu me ya sa za ka dami malam?”
36 Men Jesus hørte det Ord, som blev sagt, og han siger til Synagogeforstanderen: „Frygt ikke, tro blot!‟
Amma sa'adda Yesu ya ji abin da suka ce, sai ya ce da shugaban majami'ar, “kada ka ji tsoro ka ba da gaskiya kawai.”
37 Og han tilstedte ingen at følge med sig uden Peter og Jakob og Johannes, Jakobs Broder.
Bai bari kowa ya kasance tare da shi ba sai Bitrus da Yakubu da Yahaya dan'uwan Yakubu.
38 Og de komme ind i Synagogeforstanderens Hus, og han ser en larmende Hob, der græd og hylede meget.
Suka zo gidan shugaban majami'ar ya ga mutane suna bakin ciki, suna kuka sosai.
39 Og han gaar ind og siger til dem: „Hvorfor larme og græde I? Barnet er ikke død, men det sover.‟
Sa'adda ya shiga gidan ya ce da mutane “Me ya sa kuke damuwa da kuka?” Yarinyar ba ta mutu ba barci ta ke yi.
40 Og de lo ad ham; men han drev dem alle ud, og han tager Barnets Fader og Moder og sine Ledsagere med sig og gaar ind, hvor Barnet var.
Sai su kayi masa dariya. Amma ya fitar da su waje su duka. Ya kira baban yarinyar da mamar ta da wadansu da ke tare da shi su ka shiga wurin da yarinyar ta ke.
41 Og han tager Barnet ved Haanden og siger til hende: „Talitha kumi!‟ hvilket er udlagt: „Pige, jeg siger dig, staa op!‟
Ya kama hannun yarinyar ya ce da ita “Tilatha koum” wato yarinya na ce ki tashi”
42 Og straks stod Pigen op og gik omkring; thi hun var tolv Aar gammel. Og de bleve straks overmaade forfærdede.
Nan da nan yarinyar ta tashi ta yi tafiya [gama shekarun ta sun kai goma sha biyu]. Nan da nan mutanen suka yi mamaki kwarai da gaske.
43 Og han bød dem meget, at ingen maatte faa dette at vide; og han sagde, at de skulde give hende noget at spise.
Ya ummurce su da gaske kada kowa ya sani. Ya ce da su su ba ta abinci ta ci.

< Markus 5 >