< Malakias 2 >
1 Og nu, denne Bestemmelse gælder eder, I Præster!
“Yanzu fa wannan gargaɗi dominku ne, ku firistoci.
2 Dersom I ikke høre det, og dersom I ikke lægge det paa Hjerte at give mit Navn Ære, siger den Herre Zebaoth, da vil jeg sende Forbandelsen paa eder og forbande eders Velsignelser; ja, jeg har allerede forbandet dem, fordi I ikke ville lægge det paa Hjerte.
In ba ku saurara ba, in kuma ba ku sa zuciyarku ga girmama sunana ba, zan aukar muku da la’ana, zan kuma la’antar da albarkunku. I, na riga na la’anta su, domin ba ku sa zuciyarku ga girmama ni ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
3 Se, jeg truer Sæden for eder og spreder Møg over eders Ansigter, Møget af eders Festofre, og man skal bringe eder hen til dette.
“Saboda ku zan tsawata wa zuriyarku; zan watsa kashin dabbobin hadayunku a fuskokinku, a kuma kwashe ku tare da shi.
4 Og I skulle fornemme, at jeg har sendt denne Bestemmelse imod eder, for at den skal vorde min Pagt med Levi, siger den Herre Zebaoth.
Za ku kuwa san cewa ni ne na aika muku da wannan gargaɗi domin alkawarina da Lawi yă ci gaba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
5 Min Pagt var med ham, Livet og Freden, og jeg gav ham dem til Frygt, og han frygtede mig, og for mit Navn var han forfærdet.
“Alkawarina da shi, alkawari ne na rai da salama, wanda na ba shi; domin yă girmama ni, ya kuwa girmama ni, ya kuma ji tsoron sunana ƙwarai.
6 Sandheds Lov var i hans Mund, og der blev ikke fundet Uret paa hans Læber; i Fred og i Oprigtighed vandrede han med mig og omvendte mange fra Misgerning.
Umarnin gaskiya yana a bakinsa, ba a kuma sami wani ƙarya a leɓunansa ba. Ya yi tafiya tare da ni cikin salama da adalci, ya kuwa juyo da mutane masu yawa daga zunubi.
7 Thi en Præsts Læber skulle bevare Kundskab, og Loven skal man søge af hans Mund; thi han er den Herre Zebaoths Sendebud.
“Gama ya kamata leɓunan firist su kiyaye ilimi, ya kamata kuma mutane su nemi umarni daga bakinsa, domin shi ne manzon Ubangiji Maɗaukaki.
8 Men I ere afvegne fra Vejen, I have bragt mange til at støde an imod Loven; I have fordærvet Levis Pagt, siger den Herre Zebaoth.
Amma sai kuka kauce hanya, ta wurin koyarwarku kuma kuka sa mutane da yawa suka yi tuntuɓe; kun keta alkawarin da na yi da Lawi,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
9 Derfor gør ogsaa jeg eder foragtelige og ringe for alt Folket, eftersom I ikke agte paa mine Veje, men anse Personer ved Anvendelse af Loven.
“Saboda haka na sa a rena ku, a kuma wulaƙanta ku a gaban dukan mutane, domin ba ku bi hanyoyina ba amma kuka nuna sonkai a al’amuran shari’a.”
10 Have vi ikke alle sammen een Fader? har ikke een Gud skabt os? hvorfor handle vi troløst, den ene imod den anden, for at vanhellige vore Fædres Pagt?
Ashe, ba Mahaifi guda dukanmu muke da shi ba? Ba Allah ɗaya ne ya halicce mu ba? Don me muka keta alkawarin kakanninmu ta wurin cin amanar juna?
11 Juda har handlet troløst, og der er sket Vederstyggelighed i Israel og i Jerusalem; thi Juda har vanhelliget Herrens Helligdom, som han elsker, og taget til Ægte en fremmed Guds Datter.
Yahuda ya ci amana. An yi abin kunya a Isra’ila da kuma a Urushalima. Yahuda ya ƙazantar da wuri mai tsarkin da Ubangiji yake ƙauna, ta wurin auren’yar wani baƙon allah.
12 For den Mand, som gør dette, udrydde Herren den, som er vaagen, og den, som svarer, af Jakobs Telte, og den, som fremfører Offergaver til den Herre Zebaoth!
Game da mutumin da ya aikata wannan, ko wane ne shi, bari Ubangiji yă yanke shi daga tentunan Yaƙub, ko da ma ya kawo hadayu ga Ubangiji Maɗaukaki.
13 For det andet gøre I ogsaa dette: I bedække Herrens Alter med Taarer, med Graad og Suk, saa at han ikke mere vender sit Ansigt til Offergaven eller modtager noget som velbehageligt af eders Haand.
Ga kuma wani abin da kuke yi. Kukan cika bagaden Ubangiji da hawaye. Kukan yi kuka kuna ihu gama Ubangiji ba ya mai da hankali ga hadayunku ko yă karɓe su da farin ciki.
14 Og I sige: Hvorfor? Fordi Herren har været Vidne imellem dig og din Ungdoms Hustru, som du har handlet troløst imod, da hun dog var din Ægtefælle og din Pagts Hustru.
Kukan ce, “Don me ba ya karɓan hadayunmu?” Ai, domin Ubangiji ya zama shaida tsakaninka da matar ƙuruciyarka, gama ka keta amanar da ka yi mata, ko da yake ita abokiyar zamanka ce, matar aurenka ta alkawari.
15 Og een, som havde en Rest af Aand, har ikke handlet saaledes. Men hvad gjorde den ene? Han søgte den af Gud forjættede Sæd. Saa skulle I vogte eder for eders Aands Skyld, og ingen handle troløst imod sin Ungdoms Hustru!
Ashe, Ubangiji bai maishe su ɗaya ba? Cikin jiki da ruhu, su nasa ne. Me ya sa suke ɗaya? Domin yana neman’ya’ya masu tsoron Allah. Saboda haka sai ka lura da kanka, kada kuma ka ci amanar matar ƙuruciyarka.
16 Thi jeg hader Skilsmisse, siger den Herre Israels Gud, og man bedækker derved sit Klædebon med Vold, siger den Herre Zebaoth; saa skulle I vogte eder for eders Aands Skyld og ikke handle troløst.
“Na ƙi kisan aure,” in ji Ubangiji, Allah na Isra’ila. “Na kuma ƙi mutumin da ya rufe kansa da tashin hankali kamar riga,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. Saboda haka sai ka lura da kanka, kada kuma ka ci amana.
17 I have trættet Herren med eders Ord; og dog sige I: Hvormed have vi trættet ham? Idet I sige: Hver, som gør ondt, er god for Herrens Øjne, og til dem har han Lyst, eller: Hvor er Dommens Gud?
Kun sa Ubangiji Maɗaukaki ya gaji da maganganunku. Sai kuka ce, “Yaya muka sa ya gaji?” Kun yi haka ta wurin cewa, “Duk waɗanda suke aikata mugunta, mutanen kirki ne a gaban Ubangiji, yana kuwa jin daɗinsu,” kuna kuma cewa, “Ina Allah mai adalci yake?”