< Lukas 22 >

1 Men de usyrede Brøds Højtid, som kaldes Paaske, nærmede sig.
Anan nan idin gurasa mara yisti ya yi kusa, wanda a ke kira Idin ketarewa.
2 Og Ypperstepræsterne og de skriftkloge søgte, hvorledes de kunde slaa ham ihjel; thi de frygtede for Folket.
Manyan firistoci da marubuta suka yi shawara yadda za su kashe Yesu, gama suna jin tsoron mutane.
3 Men Satan gik ind i Judas, som kaldes Iskariot og var en af de tolv.
Shaidan ya shiga Yahuza Iskariyoti, daya daga cikin goma sha biyun.
4 Og han gik hen og talte med Ypperstepræsterne og Høvedsmændene om, hvorledes han vilde forraade ham til dem.
Yahuza ya je ya yi shawara da manyan firistoci da Jarumawa yadda zai ba da Yesu a garesu.
5 Og de bleve glade og lovede at give ham Penge.
Suka yi farin ciki, suka yarda su ba shi kudi.
6 Og han tilsagde det; og han søgte Lejlighed til at forraade ham til dem uden Opløb.
Sai ya yarda, sai ya nimi dama yadda zai ba da shi garesu a lokacin da babu taro.
7 Men de usyrede Brøds Dag kom, paa hvilken man skulde slagte Paaskelammet.
Ranar idin gurasa mara yisti ya yi, da dole za a yi hadayan rago na Idin ketarewa.
8 Og han udsendte Peter og Johannes og sagde: „Gaar hen og bereder os Paaskelammet, at vi kunne spise det.‟
Yesu ya aiki Bitrus da Yahaya, ya ce masu, “Ku je ku shirya mana abincin Idin ketarewa, domin mu ci.”
9 Men de sagde til ham: „Hvor vil du, at vi skulle berede det?‟
Suka tambaye shi, “A ina ka ke so mu shirya?”
10 Men han sagde til dem: „Se, naar I ere komne ind i Staden, skal der møde eder en Mand, som bærer en Vandkrukke; følger ham til Huset, hvor han gaar ind,
Ya amsa masu, “Ku ji, sa'adda ku ka shiga birnin, wani mutum mai dauke da tulun ruwa zai same ku. Ku bishi zuwa cikin gidan da za ya shiga.
11 og I skulle sige til Husbonden i Huset: Mesteren siger: Hvor er det Herberge, hvor jeg kan spise Paaskelammet med mine Disciple?
Sai ku gaya wa mai gidan, 'Malam ya ce, “Ina dakin baki, inda zan ci abincin Idin ketarewa da almajirai na?'”
12 Og han skal vise eder en stor Sal opdækket; der skulle I berede det.‟
Zai nuna maku babban bene wanda yake a shirye. Ku shirya a can.”
13 Og de gik hen og fandt det saaledes, som han havde sagt dem; og de beredte Paaskelammet.
Sai suka tafi, suka sami komai kamar yadda ya gaya masu. Sai suka shirya abincin Idin ketarewan.
14 Og da Timen kom, satte han sig til Bords, og Apostlene med ham.
Sa'adda lokacin ya yi, ya zauna da almajiran.
15 Og han sagde til dem: „Jeg har hjerteligt længtes efter at spise dette Paaskelam med eder, førend jeg lider.
Sai ya ce masu, “Ina da marmari matuka in ci wannan abincin Idin ketarewa da ku kamin in sha wahala.
16 Thi jeg siger eder, at jeg skal ingen Sinde mere spise det, førend det bliver fuldkommet i Guds Rige.‟
Gama na ce maku, ba zan ci shi kuma ba, sai dai an cika shi a mulkin Allah.”
17 Og han tog en Kalk, takkede og sagde: „Tager dette, og deler det imellem eder!
Sai Yesu ya dauki koko, sa'adda ya yi godiya, sai yace, “Karba wannan, ku rarraba a tsakaninku.
18 Thi jeg siger eder, at fra nu af skal jeg ikke drikke af Vintræets Frugt, førend Guds Rige kommer.‟
Gama ina ce maku, ba zan sha wannan ruwan inabi kuma ba, sai dai mulkin Allah ya zo.”
19 Og han tog Brød, takkede og brød det og gav dem det og sagde: „Dette er mit Legeme, det, som gives for eder; gører dette til min Ihukommelse!‟
Sai ya dauki gurasa, sa'adda ya yi godiya, ya kakkarya shi, sai ya ba su, cewa, “Wannan jikina ne wanda aka bayar dominku. Ku yi wannan domin tunawa da ni.”
20 Ligesaa tog han ogsaa Kalken efter Aftensmaaltidet og sagde: „Denne Kalk er den nye Pagt i mit Blod, det, som udgydes for eder.
Sai ya dauki kokon kuma bayan jibi, cewa, “Wannan koko sabon alkawari ne cikin jinina, wanda aka zubar dominku.
21 Men se, hans Haand, som forraader mig, er her paa Bordet hos mig.
Amma ku yi lura. Wanda zai bashe ni yana tare da ni a teburi.
22 Thi Menneskesønnen gaar bort, som det er beskikket; dog ve det Menneske, ved hvem han bliver forraadt!‟
Gama Dan Mutum zai tafi lallai kamar yadda aka kaddara. Amma kaiton wannan mutum da shine za ya bashe shi!”
23 Og de begyndte at spørge hverandre indbyrdes om, hvem af dem det dog kunde være, som skulde gøre dette.
Sai suka fara tambaya a tsakaninsu, wanene a cikinmu da zai yi wannan abu.
24 Men der opstod ogsaa en Trætte iblandt dem om, hvem af dem der maatte synes at være den største.
Sai gardama ta tashi a tsakaninsu game da wanene mafi girma.
25 Men han sagde til dem: „Folkenes Konger herske over dem, og de, som bruge Myndighed over dem, kaldes deres Velgørere.
Ya ce masu, “Sarakunan al'ummai suna nuna iko akansu, kuma wadanda suke da iko a kansu ana ce da su masu mulki da daraja.
26 I derimod ikke saaledes; men den ældste iblandt eder blive som den yngste, og Føreren som den, der tjener.
Amma kada ya zama haka da ku. A maimakon haka, bari wanda ya ke mafi girma a cikinku ya zama mafi kankanta. Bari wanda yafi muhimmanci kuma ya zama kamar mai hidima.
27 Thi hvem er størst: den, som sidder til Bords? eller den, som tjener? Mon ikke den, som sidder til Bords? Men jeg er iblandt eder som den, der tjener.
Gama wanene yafi girma, wanda ya zauna a teburi, ko kuwa wanda yake yin hidima? Ba wanda ya zauna a teburi ba? Duk da haka ina kamar mai hidima a tsakaninku.
28 Men I ere de, som have holdt ud med mig i mine Fristelser.
Amma ku ne wadanda ku ke tare da ni a cikin jarabobina.
29 Og ligesom min Fader har tildelt mig Kongedømme, tildeler jeg eder
Na baku mulki, kamar yadda Ubana ya ba ni mulki,
30 at skulle spise og drikke ved mit Bord i mit Rige og sidde paa Troner og dømme Israels tolv Stammer.‟
domin ku ci ku kuma sha a teburi na mulkina. Za ku zauna a kan kursiyai kuna shari'anta kabilun nan goma sha biyu na Israila.
31 Men Herren sagde: „Simon, Simon! se, Satan begærede eder for at sigte eder som Hvede.
Siman, Siman, ka yi hankali, shaidan ya nemi izini a bada kai domin ya tankade ka kamar alkama.
32 Men jeg bad for dig, at din Tro ikke skal svigte; og naar du engang omvender dig, da styrk dine Brødre!‟
Amma na yi maka addu'a, saboda kada bangaskiyarka ta fadi. Bayan da ka juyo kuma, ka karfafa 'yan'uwanka.”
33 Men han sagde til ham: „Herre! jeg er rede til at gaa med dig baade i Fængsel og i Døden.‟
Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ina shirye in tafi tare da kai zuwa cikin kurkuku da zuwa mutuwa.”
34 Men han sagde: „Peter! jeg siger dig: Hanen skal ikke gale i Dag, førend du tre Gange har nægtet, at du kender mig.‟
Yesu ya amsa masa, “Ina gaya maka, Bitrus, kamin caran zakara a yau, za ka yi musu na sau uku cewa ba ka sanni ba.”
35 Og han sagde til dem: „Da jeg udsendte eder uden Pung og Taske og Sko, manglede I da noget?‟ Og de sagde: „Intet.‟
Sa'annan Yesu ya ce masu, “Lokacin da na aike ku babu jaka, ko burgami ko takalma, ko kun rasa wani abu? Sai suka amsa, “Babu.”
36 Men han sagde til dem: „Men nu, den, som har en Pung, tage den med, ligesaa ogsaa en Taske; og den, som ikke har noget Sværd, sælge sin Kappe og købe et!
Ya kuma ce masu, “Amma yanzu, wanda ya ke da jaka, bari ya dauka, da kuma burgami. Wanda ba shi da takobi sai ya sayar da taguwarsa ya sayi guda.
37 Thi jeg siger eder: Det, som er skrevet, bør opfyldes paa mig, dette: „Og han blev regnet iblandt Overtrædere; ‟ thi ogsaa med mig har det en Ende.‟
Gama ina ce maku, abin da aka rubuta game da ni dole sai ya cika, 'An lisafta shi kamar daya daga cikin masu karya doka.' Gama abinda aka fada akaina ya cika.”
38 Men de sagde: „Herre! se, her ere to Sværd.‟ Men han sagde til dem: „Det er nok.‟
Sai suka ce, “Ubangiji, duba! Ga takuba biyu.” Sai ya ce masu, “Ya isa.”
39 Og han gik ud og gik efter sin Sædvane til Oliebjerget; men ogsaa Disciplene fulgte ham.
Bayan cin abincin yamma, Yesu ya tafi, kamar yadda ya saba yi, zuwa dutsen Zaitun, sai almajiran suka bi shi.
40 Men da han kom til Stedet, sagde han til dem: „Beder om ikke at falde i Fristelse.‟
Sa'adda suka iso, ya ce masu, “Ku yi addu'a domin kada ku shiga cikin jaraba.”
41 Og han rev sig løs fra dem, saa meget som et Stenkast, og faldt paa Knæ, bad og sagde:
Ya rabu da su misalin nisan jifa, sai ya durkusa kasa ya yi addu'a,
42 „Fader, vilde du dog tage denne Kalk fra mig! dog ske ikke min Villie, men din!‟
yana cewa “Uba, in ka yarda, ka dauke wannan kokon daga gareni. Ko da yake ba nufina ba, amma bari naka nufin ya kasance.”
43 Men en Engel fra Himmelen viste sig for ham og styrkede ham.
Sai mala'ika daga sama ya bayyana a wurinsa, yana karfafa shi.
44 Og da han var i Dødsangest, bad han heftigere; men hans Sved blev som Blodsdraaber, der faldt ned paa Jorden.
Yana cikin wahala sosai, sai ya dukufa cikin addu'a, har zufarsa kuma tana diga a kasa kamar gudajen jini.
45 Og da han stod op fra Bønnen og kom til Disciplene, fandt han dem sovende af Bedrøvelse.
Sa'adda ya tashi daga addu'arsa, sai ya zo wurin almajiran, ya same su suna barci domin bakin cikinsu,
46 Og han sagde til dem: „Hvorfor sove I? Staar op og beder, for at I ikke skulle falde i Fristelse.‟
sai ya tambaye su, “Don me kuke barci? Tashi ku yi addu'a, saboda kada ku shiga cikin jaraba.”
47 Medens han endnu talte, se, da kom der en Skare; og han, som hed Judas, en af de tolv, gik foran dem og nærmede sig til Jesus for at kysse ham.
Sa'adda yana cikin magana, sai, ga taron jama'a suka bayana, tare da Yahuza, daya daga cikin sha biyun, ya na jagabansu. Sai ya zo kusa da Yesu domin ya yi masa sumba,
48 Men Jesus sagde til ham: „Judas! forraader du Menneskesønnen med et Kys?‟
amma Yesu ya ce masa, “Yahuza, za ka ba da Dan Mutum da sumba?”
49 Men da de, som vare omkring ham, saa, hvad der vilde ske, sagde de: „Herre! skulle vi slaa til med Sværd?‟
Sa'adda wadanda suke kewaye da Yesu suka ga abin da yake faruwa, sai suka ce, “Ubangiji, mu yi sara da takobi ne?”
50 Og en af dem slog Ypperstepræstens Tjener og afhuggede hans højre Øre.
Sai daya daga cikinsu ya kai wa bawan babban firist sara a kunne, sai ya yanke masa kunnensa na dama.
51 Men Jesus tog til Orde og sagde: „Lad dem gøre ogsaa dette!‟ Og han rørte ved hans Øre og lægte ham.
Yesu ya ce, “Ya isa haka.” Sai ya taba kunnensa, sai ya warkar da shi.
52 Men Jesus sagde til Ypperstepræsterne og Høvedsmændene for Helligdommen og de Ældste, som vare komne til ham: „I ere gaaede ud som imod en Røver med Sværd og Knipler.
Yesu yace wa manyan firistoci, da masu tsaron haikali, da dattawa wadanda suke gaba da shi, “Kun fito kamar za ku kama dan fashi, da takuba da sanduna?
53 Da jeg var daglig hos eder i Helligdommen, udrakte I ikke Hænderne imod mig; men dette er eders Time og Mørkets Magt.‟
Sa'adda nake tare da ku kowace rana a haikali, ba ku kama ni ba. Amma wannan shine lokacinku, da kuma ikon duhu.”
54 Og de grebe ham og førte ham bort og bragte ham ind i Ypperstepræstens Hus; men Peter fulgte efter i Frastand.
Suka kama shi, sai suka tafi da shi, suka kawo shi cikin gidan babban firist. Amma Bitrus yana binsa daga nesa.
55 Og de tændte en Ild midt i Gaarden og satte sig sammen, og Peter sad midt iblandt dem.
Bayan da suka hura wuta a tsakiyar gidan da suka zazzauna tare, Bitrus ya zaune a tsakaninsu.
56 Men en Pige saa ham sidde i Lysskæret og stirrede paa ham og sagde: „Ogsaa denne var med ham.‟
Sai wata baranya ta ganshi ya zauna a hasken wuta, sai ta zura masa ido ta ce, “Wannan mutum ma yana tare da shi.”
57 Men han fornægtede ham og sagde: „Jeg kender ham ikke, Kvinde!‟
Amma Bitrus ya yi musu, yana cewa, “Mace, ban san shi ba.”
58 Og lidt derefter saa en anden ham og sagde: „Ogsaa du er en af dem.‟ Men Peter sagde: „Menneske! det er jeg ikke.‟
Bayan dan karamin lokaci sai wani mutum ya gan shi, sai ya ce, “Kaima kana daya daga cikinsu.” Amma Bitrus ya ce, “Mutumin, ba ni ba ne.”
59 Og omtrent en Time derefter forsikrede en anden det og sagde: „I Sandhed, ogsaa denne var med ham; han er jo ogsaa en Galilæer.‟
Bayan sa'a daya sai wani mutum ya nace da cewa, “Gaskiya wannan mutum yana tare da shi, gama shi dan Galili ne.”
60 Men Peter sagde: „Menneske! jeg forstaar ikke, hvad du siger.‟ Og straks, medens han endnu talte, galede Hanen.
Amma Bitrus ya ce, “Mutumin, ban san abin da kake fada ba.” Sai nan da nan, da yana cikin magana, sai zakara ta yi cara.
61 Og Herren vendte sig og saa paa Peter; og Peter kom Herrens Ord i Hu, hvorledes han havde sagt til ham: „Førend Hanen galer i Dag, skal du fornægte mig tre Gange.‟
Yana juyawa, sai Ubangiji ya dubi Bitrus. Sai Bitrus ya tuna kalmar Ubangiji, sa'adda ya ce masa, “Kafin zakara ya yi cara yau za ka musunce ni sau uku.”
62 Og han gik udenfor og græd bitterligt.
Da fitowarsa waje, Bitrus ya yi kuka mai zafi.
63 Og de Mænd, som holdt Jesus, spottede ham og sloge ham;
Sai mutanen da ke tsare da Yesu suka yi masa ba'a da bulala kuma.
64 og de kastede et Klæde over ham og spurgte ham og sagde: „Profetér! hvem var det, som slog dig?‟
Bayan da suka rufe masa idanu, suka tambaye shi, cewa, “Ka yi annabci! Wa ya buge ka?”
65 Og mange andre Ting sagde de spottende til ham.
Suka yi wadansu miyagun maganganu na sabo game da Yesu.
66 Og da det blev Dag, samlede Folkets Ældste sig og Ypperstepræsterne og de skriftkloge, og de førte ham hen for deres Raad
Da gari ya waye, sai dattawa suka hadu tare, da manyan firistoci da marubuta. Sai suka kai shi cikin majalisa
67 og sagde: „Er du Kristus, da sig os det!‟ Men han sagde til dem: „Siger jeg eder det, tro I det ikke.
suka ce, “Gaya mana, in kai ne Almasihu.” Amma yace masu, “Idan na gaya maku, ba za ku gaskanta ba,
68 Og om jeg spørger, svare I mig ikke, ej heller løslade I mig.
idan na yi maku tambaya, ba za ku amsa ba.
69 Men fra nu af skal Menneskesønnen sidde ved Guds Krafts højre Haand.‟
Amma nan gaba, Dan Mutum zai zauna a hannun dama na ikon Allah.”
70 Men de sagde alle: „Er du da Guds Søn?‟ Og han sagde til dem: „I sige det; jeg er det.‟
Suka ce masa, “Ashe kai Dan Allah ne?” Sai Yesu ya ce masu, “Haka kuka ce, nine.”
71 Men de sagde: „Hvad have vi længere Vidnesbyrd nødig? vi have jo selv hørt det af hans Mund!‟
Suka ce, “Don me muke neman shaida? Gama mu da kanmu munji daga bakinsa.”

< Lukas 22 >