< Lukas 13 >

1 Men paa den samme Tid var der nogle til Stede, som fortalte ham om de Galilæere, hvis Blod Pilatus havde blandet med deres Ofre.
A yanzun fa, akwai waɗansu da suka kasance a lokacin can, suka ba Yesu labarin Galiliyawa da Bilatus ya gauraye jininsu tare da jinin hadayunsu.
2 Og han svarede og sagde til dem: „Mene I, at disse Galilæere vare Syndere fremfor alle Galilæere, fordi de have lidt dette?
Yesu ya amsa ya ce, “Kuna tsammani waɗannan Galiliyawan sun fi dukan sauran Galiliyawa zunubi ne, shi ya sa suka sha irin wannan wahala?
3 Nej, siger jeg eder; men dersom I ikke omvende eder, skulle I alle omkomme ligesaa.
Ina gaya muku, a’a! Amma in ba ku tuba ba, ku ma duka za ku hallaka.
4 Eller hine atten, som Taarnet i Siloam faldt ned over og ihjelslog, mene I, at de vare skyldige fremfor alle Mennesker, som bo i Jerusalem?
Ko kuwa kuna tsammani, sha takwas ɗin nan da suka mutu lokacin da hasumiya a Silowam ya fāɗi a kansu, sun fi dukan sauran mutanen Urushalima laifi ne?
5 Nej, siger jeg eder; men dersom I ikke omvende eder, skulle I alle omkomme ligesaa.”
Ina gaya muku, a’a! Amma in ba ku tuba ba, ku ma duka za ku hallaka.”
6 Men han sagde denne Lignelse: „En havde et Figentræ, som var plantet i hans Vingaard; og han kom og ledte efter Frugt derpaa og fandt ingen.
Sai ya ba su wannan misali ya ce, “Wani mutum yana da itacen ɓaure, da aka shuka a gonar inabinsa. Da ya je cire’ya’yan itacen, sai ya tarar ba tă yi’ya’ya ba.
7 Men han sagde til Vingaardsmanden: Se, i tre Aar er jeg nu kommen og har ledt efter Frugt paa dette Figentræ og ingen fundet; hug det om; hvorfor skal det tilmed gøre Jorden unyttig?
Sai ya ce wa mai lura da gonar inabin, ‘Yau shekara uku ke nan ina zuwa neman’ya’yan ɓaure daga itacen nan, amma ba na samun kome. Sare shi! Don me za a bar shi ya tare wuri.’
8 Men han svarede og sagde til ham: Herre! lad det staa endnu dette Aar, indtil jeg faar gravet om det og gødet det;
“Mutumin ya amsa ya ce, ‘Ranka yă daɗe, ka bar shi, in yi masa banƙasa, in kuma zuba masa taki har na shekara ɗaya.
9 maaske vil det bære Frugt i Fremtiden; men hvis ikke, da hug det om!”
In kuwa ya ba da’ya’ya shekara mai zuwa, yana da kyau! In kuwa ba haka ba, sai ka sare shi.’”
10 Men han lærte i en af Synagogerne paa Sabbaten.
Wata ranar Asabbaci, Yesu yana koyarwa a wata majami’a,
11 Og se, der var en Kvinde, som havde haft en Svagheds Aand i atten Aar, og hun var sammenbøjet og kunde aldeles ikke rette sig op.
a wurin kuwa, akwai wata mace wadda aljani ya gurgunta, har na shekaru goma sha takwas. Duk ta tanƙware, ba ta ma iya miƙewa ko kaɗan.
12 Men da Jesus saa hende, kaldte han paa hende og sagde til hende: „Kvinde! du er løst fra din Svaghed.”
Da Yesu ya gan ta, sai ya kirata gaba, ya ce mata, “Mace, an’yantar da ke daga rashin lafiyarki.”
13 Og han lagde Hænderne paa hende; og straks rettede hun sig op og priste Gud.
Sai ya ɗibiya hannuwansa a kanta, nan da nan sai ta miƙe, ta yabi Allah.
14 Men Synagogeforstanderen, som var vred, fordi Jesus helbredte paa Sabbaten, tog til Orde og sagde til Folkeskaren: „Der er seks Dage, paa hvilke man bør arbejde; kommer derfor paa dem og lader eder helbrede, og ikke paa Sabbatsdagen!”
Amma mai mulkin majami’ar ya ji haushi da Yesu ya yi warkarwa a ranar Asabbaci. Sai ya ce wa mutanen, “Akwai ranaku shida da ya kamata a yi aiki. Saboda haka, ku zo a ranakun nan a warkar da ku, ba ranar Asabbaci ba.”
15 Men Herren svarede ham og sagde: „I Hyklere! løser ikke enhver iblandt eder sin Okse eller sit Asen fra Krybben paa Sabbaten og fører dem til Vands?
Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Ku munafukai! Ashe, kowannenku ba yakan kunce bijiminsa ko jakinsa, yă kai shi waje yă ba shi ruwa, a ranar Asabbaci ba?
16 Men denne, som er en Abrahams Datter, hvem Satan har bundet, se, i atten Aar, burde hun ikke løses fra dette Baand paa Sabbatsdagen?”
Ashe, bai kamata a’yantar da macen nan, diyar zuriyar Ibrahim, wadda Shaiɗan ya daure, har shekara goma sha takwas, a ranar Asabbaci, daga abin da ya daure ta ba?”
17 Og da han sagde dette, bleve alle hans Modstandere beskæmmede; og hele Skaren glædede sig over alle de herlige Gerninger, som gjordes af ham.
Sa’ad da ya faɗi wannan, sai duka masu gāba da shi suka kunyata. Amma mutane kuwa suka yi murna saboda dukan abubuwan banmamaki da yake yi.
18 Han sagde da: „Hvad ligner Guds Rige, og hvormed skal jeg ligne det?
Sai Yesu ya yi tambaya ya ce, “Yaya mulkin Allah yake? Da me zan kwatanta shi?
19 Det ligner et Sennepskorn, som et Menneske tog og lagde i sin Have; og det voksede og blev til et Træ, og Himmelens Fugle byggede Rede i dets Grene.”
Yana kama da ƙwayar mustad, wadda wani mutum ya ɗauka, kuma ya shuka a gonarsa. Ta yi girma, ta zama itace, kuma tsuntsayen sararin sama suka huta a rassansa.”
20 Og atter sagde han: „Hvormed skal jeg ligne Guds Rige?
Ya sāke tambaya, “Da me zan kwatanta mulkin Allah?
21 Det ligner en Surdejg, som en Kvinde tog og lagde ned i tre Maal Mel, indtil det blev syret alt sammen.”
Yana kama da yisti wadda mace ta ɗauka, ta kwaɓa garin alkama mai yawa da shi, har sai da yistin ya gauraye kullun duka.”
22 Og han gik igennem Byer og Landsbyer og lærte og tog Vejen til Jerusalem.
Sa’ad da Yesu yana kan hanyarsa zuwa Urushalima, sai ya bi ta cikin garuruwan da ƙauyukan, yana koyarwa.
23 Men en sagde til ham: „Herre! mon de ere faa, som blive frelste?” Da sagde han til dem:
Sai wani ya tambaye shi ya ce, “Ya Ubangiji, shin, wai mutane kima ne kawai za su sami ceto?” Ya ce musu,
24 „Kæmper for at komme ind igennem den snævre Port; thi mange, siger jeg eder, skulle søge at komme ind og ikke formaa det.
“Ku yi matuƙar ƙoƙari ku shiga ta matsattsiyar ƙofa, domin ina faɗa muku, mutane da yawa za su yi ƙoƙarin shiga, amma ba za su iya ba.
25 Fra den Stund Husbonden er staaet op og har lukket Døren, og I begynde at staa udenfor og banke paa Døren og sige: Herre, luk op for os! da vil han svare og sige til eder: Jeg kender eder ikke, hvorfra I ere;
Da zaran maigidan ya tashi ya rufe ƙofar, za ku tsaya a waje kuna ƙwanƙwasawa, kuna roƙo cewa, ‘Ranka yă daɗe, buɗe mana ƙofa.’ “Amma shi zai amma ya ce, ‘Ni ban san ku, ko inda kuka fito ba.’
26 da skulle I begynde at sige: Vi spiste og drak for dine Øjne, og du lærte paa vore Gader,
“Sa’an nan za ku ce, ‘Haba, mu da muka ci, muka sha tare da kai, har ka yi koyarwa a cikin titi-titi namu.’
27 og han skal sige: Jeg siger eder, jeg kender eder ikke, hvorfra I ere; viger bort fra mig, alle I, som øve Uret!
“Amma shi zai amma ya ce, ‘Ban san ku, ko inda kuka fito ba. Ku rabu da ni, dukan ku masu aikata mugunta!’
28 Der skal der være Graad og Tænders Gnidsel, naar I maa se Abraham og Isak og Jakob og alle Profeterne i Guds Rige, men eder selv blive kastede udenfor.
“Za a yi kuka a can, da cizon haƙora, sa’ad da kuka ga Ibrahim, da Ishaku, da Yaƙub, da dukan annabawa a mulkin Allah, amma ku kuwa, za a jefar da ku a waje.
29 Og de skulle komme fra Øster og Vester og fra Norden og Sønden og sidde til Bords i Guds Rige.
Mutane za su zo daga gabas, da yamma, da kudu, da arewa, su ɗauki wuraren zamansu a bikin, a cikin mulkin Allah.
30 Og se, der er sidste, som skulle være iblandt de første, og der er første, som skulle være iblandt de sidste.”
Tabbatacce, akwai waɗansu da suke na ƙarshe, da za su zama na farko, na farko kuma, da za su zama na ƙarshe.”
31 I den samme Stund kom nogle Farisæere og sagde til ham: „Gaa bort, og drag herfra; thi Herodes vil slaa dig ihjel.”
A wannan lokaci, waɗansu Farisiyawa suka zo suka ce wa Yesu, “Ka bar nan ka tafi wani wuri dabam. Hiridus yana so ya kashe ka.”
32 Og han sagde til dem: „Gaar hen og siger til denne Ræv: Se, jeg uddriver onde Aander og fuldfører Helbredelser i Dag og i Morgen, og paa den tredje Dag fuldendes jeg.
Ya amsa ya ce, “Ku je ku gaya wa dilan nan, wato, mai makirci cewa, ‘Da yau da kuma gobe, zan fitar da aljanu, in kuma warkar da mutane, sa’an nan a rana ta uku in cika burin aikina.
33 Dog bør jeg vandre i Dag og i Morgen og den Dag derefter; thi det sømmer sig ikke, at en Profet dræbes uden for Jerusalem.
Duk da haka, dole in ci gaba da aikin a yau, da kuma gobe, sa’an nan in ci gaba da yin haka kashegari kuma, gama tabbatacce, ba annabi da yakan mutu a bayan birnin Urushalima!’
34 Jerusalem! Jerusalem! som ihjelslaar Profeterne og stener dem, som ere sendte til dig! hvor ofte vilde jeg samle dine Børn, ligesom en Høne samler sine Kyllinger under Vingerne! Og I vilde ikke.
“Urushalima, ayya Urushalima, ke da kika kashe annabawa, kuma kika jefa wa waɗanda aka aika gare ki da duwatsu. Sau da yawa na yi kewan in tattara’ya’yanki wuri ɗaya, kamar yadda kaza takan tattara’ya’yanta cikin fikafikanta, amma ba ki yarda ba!
35 Se, eders Hus overlades til eder selv. Men jeg siger eder: I skulle ingenlunde se mig, førend den Tid kommer, da I sige: Velsignet være den, som kommer, i Herrens Navn!”
Duba, an bar muku gidanku fanko. Ina kuwa faɗa muku, ba za ku sāke ganina ba, sai kun ce, ‘Mai albarka ne shi wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji.’”

< Lukas 13 >