< 3 Mosebog 10 >

1 Og Arons Sønner, Nadab og Abihu, toge hver sit Ildkar og lagde Ild derudi og lagde Røgelse derpaa, og de bragte fremmed Ild for Herrens Ansigt, hvilket han ikke havde befalet dem.
’Ya’yan Haruna maza, Nadab da Abihu suka ɗauki farantansu, suka sa wuta a ciki, suka zuba turare a kai; suka kuma miƙa haramtacciyar wuta a gaban Ubangiji, ba irin wadda Ubangiji ya umarta ba.
2 Da for en Ild ud fra Herrens Ansigt og fortærede dem, og de døde for Herrens Ansigt.
Sai wuta ta fito daga Ubangiji ta cinye su, suka kuma mutu a gaban Ubangiji.
3 Da sagde Mose til Aron: Dette er det, som Herren har talet og sagt: Jeg vil helliggøres i dem, som staa mig nær, og jeg vil herliggøres for alt Folkets Aasyn; og Aron tav.
Sai Musa ya ce Haruna, “Ga abin da Ubangiji yake nufi sa’ad da ya ce, “‘A cikin waɗanda suka kusace ni za a tabbata ni mai tsarki ne; a fuskar dukan mutane za a kuwa girmama ni.’” Haruna ya yi shiru.
4 Men Mose kaldte ad Misael og ad Elzafan, Sønner af Usiel, Arons Farbroder, og sagde til dem: Træder frem, bærer eders Brødre fra Helligdommen hen uden for Lejren.
Sai Musa ya kira Mishayel da Elzafan,’ya’yan Uzziyel kawun Haruna, ya ce musu, “Ku zo nan; ku ɗauki’yan’uwanku waje da sansani, daga gaban wuri mai tsarki.”
5 Og de traadte frem og bare dem i deres Kjortler hen udenfor Lejren, som Mose havde sagt.
Sai suka zo suka ɗauke su, suna nan cikin taguwoyinsu, zuwa waje da sansani yadda Musa ya umarta.
6 Da sagde Mose til Aron og til hans Sønner, Eleasar og Ithamar: I skulle ikke blotte eders Hoveder og ej sønderrive eders Klæder, at I ikke skulle dø, og Herren skulde blive vred paa al Menigheden; men lader eders Brødre af alt Israels Hus græde over denne Brand, som Herren har optændt.
Sa’an nan Musa ya ce wa Haruna da Eleyazar da Itamar’ya’yansa maza, “Kada ku bar gashin kanku barkatai, kada kuma ku yage tufafinku, don kada ku mutu. Yin haka zai jawo fushin Ubangiji a kan dukan jama’a. Amma dangoginku, wato, dukan Isra’ilawa, suna iya kuka saboda waɗanda Ubangiji ya hallaka da wuta.
7 Men I skulle ikke gaa ud af Forsamlingens Pauluns Dør, at I ikke skulle dø, thi Herrens Salveolie er paa eder; og de gjorde efter Mose Ord.
Kada ku bar ƙofar Tentin Sujada ko kuwa ku mutu, domin man Shafan Ubangiji yana kanku.” Saboda haka suka yi kamar yadda Musa ya faɗa.
8 Men Herren talede til Aron og sagde:
Sa’an nan Ubangiji ya yi magana da Haruna ya ce,
9 Du og dine Sønner med dig skulle ikke drikke Vin eller stærk Drik, naar I gaa ind i Forsamlingens Paulun, paa det I ikke skulle dø; det skal være en evig Skik hos eders Efterkommere,
“Kai da’ya’yanka maza, ba za ku sha ruwan inabi ko wani abu mai sa jiri ba a duk sa’ad da za ku shiga cikin Tentin Sujada, in ba haka ba za ku mutu. Wannan dawwammamiyar farilla ce wa tsararraki masu zuwa.
10 for at I kunne gøre Skilsmisse imellem det hellige og det vanhellige og imellem det urene og det rene,
Dole ku bambanta tsakanin mai tsarki da marar tsarki, tsakanin marar tsabta da mai tsabta,
11 og for at I kunne lære Israels Børn alle de Skikke, som Herren har sagt til dem ved Mose.
za ku kuma koyar da Isra’ilawa dukan farillan da Ubangiji ya ba su ta wurin Musa.”
12 Og Mose sagde til Aron og til hans Sønner, Eleasar og Ithamar, som vare overblevne: Tager det Madoffer, det som er levnet fra Herrens Ildoffer, og æder det med usyret. Brød ved Alteret; thi det er en højhellig Ting.
Musa ya ce wa Haruna da Eleyazar da Itamar’ya’yansa maza da suka ragu, “Ku ɗauki ragowar hadaya ta gari wadda aka yi hadaya ta ƙonawa da ita ga Ubangiji ku ci ba tare da yisti ba, a gefen bagaden, gama tsattsarka ne.
13 Men I skulle æde det paa et helligt Sted; thi det er din beskikkede Del og dine Sønners beskikkede Del af Herrens Ildofre; thi saaledes er mig befalet.
Ku ci shi a tsattsarkan wuri, gama rabonka ne da na’ya’yanka daga cikin hadayun da akan ƙone da wuta ga Ubangiji; gama haka aka umarce ni.
14 Men Rørelsens Bryst og Gavens Bov skulle I æde paa et rent Sted, du og dine Sønner og dine Døtre med dig; thi til din beskikkede Del og dine Børns beskikkede Del ere de givne af Israels Børns Takofre.
Amma kai da’ya’yanka maza da mata za su iya ci ƙirjin da aka kaɗa, da kuma cinyar da aka miƙa. Ku ci su a wuri mai tsabta; an ba da su gare ku da kuma’ya’yanku a matsayin rabo daga hadaya ta salama ta Isra’ilawa.
15 Gavens Bov og Rørelsens Bryst, som høre til Ildofrene af Fedtstykkerne, skulle de bære frem for at lade dem røre med en Rørelse for Herrens Ansigt; og det skal, være dig og dine Børn med dig en evig beskikket Del, som Herren har befalet.
Cinyar da aka miƙa da kuma ƙirjin da aka kaɗa, dole a kawo su tare da ɓangarori kitsen hadayun da aka yi ta wuri wuta, don a kaɗa a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa. Wannan zai zama na kullayaumi gare ka da’ya’yanka, yadda Ubangiji ya umarta.”
16 Og Mose ledte flittigt efter Syndofrets Buk, og se, den var opbrændt; og han blev vred paa Eleasar og paa Ithamar, Arons Sønner, dem som vare overblevne, og sagde:
Sa’ad da Musa ya nemi sani game da akuyar hadaya don zunubi, ya kuwa gane cewa an ƙone shi, sai ya yi fushi da Eleyazar da kuma Itamar,’ya’yan Haruna maza da suka ragu, ya kuma yi tambaya,
17 Hvi have I ikke ædt Syndofret paa det hellige Sted? thi det er en højhellig Ting; og han har givet eder det, at I skulle bære Menighedens Skyld, for at I skulle gøre Forligelse for dem, for Herrens Ansigt.
“Me ya sa ba ku ci hadaya don zunubi a cikin wuri mai tsarki ba? Mafi tsaki ne; an ba ku ne don a ɗauke laifin jama’a ta wurin yin kafara saboda su a gaban Ubangiji.
18 Se, dets Blod er ikke bragt indenfor i Helligdommen; I skulde jo have ædt det paa et helligt Sted, saa som jeg har befalet.
Da yake ba a kai jininsa cikin wuri mai tsarki ba, ya kamata ku ci akuyar a wuri mai tsarki, kamar yadda na umarta.”
19 Men Aron sagde til Mose: Se, i Dag have de ofret deres Syndoffer og deres Brændoffer for Herrens Ansigt, og mig er sligt vederfaret; skulde jeg da have ædt Syndofret i Dag, skulde det have været godt for Herrens Øjne?
Sai Haruna ya amsa wa Musa, “Yau sun miƙa hadayarsu don zunubi da kuma hadayarsu ta ƙonawa a gaban Ubangiji, ga kuma irin waɗannan abubuwa da suka same ni, da a ce na ci hadaya don zunubi yau, da zai yi kyau ke nan a gaban Ubangiji?”
20 Der Mose hørte det, da syntes det ham at være godt.
Da Musa ya ji haka, sai ya gamsu.

< 3 Mosebog 10 >