< Klagesangene 2 >
1 Hvorledes har Herren indhyllet Zions Datter med Mørke i sin Vrede? han har kastet Israels Herlighed fra Himmelen til Jorden, og han kom ikke sine Fødders Fodskammel i Hu paa sin Vredes Dag.
Yadda Ubangiji ya rufe Diyar Sihiyona da gizagizan fushi! Ya jefar da darajar Isra’ila daga sama zuwa ƙasa; bai tuna da wurin ɗora ƙafafunsa ba a ranar fushinsa.
2 Herren har opslugt og ikke sparet nogen af Jakobs Boliger, han har nedbrudt Judas Datters Befæstninger i sin Fortørnelse, han har nedkastet dem til Jorden; han har vanhelliget Riget og dets Fyrster.
Ubangiji ya hallakar da wurin zaman Yaƙub ba tausayi; A cikin fushinsa kuma zai rurrushe kagaran Diyar Yahuda. Ya ƙasƙantar da mulki da masu mulki.
3 Han har afhugget hvert Horn i Israel i sin brændende Vrede, han har draget sin højre Haand tilbage over for Fjenden; og der brændte i Jakob som en Ildslue, den har fortæret trindt omkring.
A cikin zafin fushi ya fasa kowane ƙaho na Isra’ila. Ya janye hannun damansa sa’ad da maƙiyi ya zo. Ya yi ƙuna a cikin Yaƙub kamar wuta mai ƙone duk abin da yake kusa da ita.
4 Han har spændt sin Bue som en Fjende, han har stillet sig med sin højre Haand som en Modstander og har ihjelslaget alle dem, som vare en Lyst for Øjnene; han udøste sin Harme i Zions Datters Paulun som en Ild.
Kamar abokin gāba, ya ɗana bakansa; hannun damansa na shirye. Kamar maƙiyi, ya kashe duk wanda idonsa ya ji daɗin gani; ya zuba fushinsa kamar wuta a kan tenti na Diyar Sihiyona.
5 Herren er bleven som en Fjende, han har opslugt Israel, han har opslugt alle dens Paladser, ødelagt dens Befæstninger og voldet Judas Datter megen Sorg og Bedrøvelse.
Ubangiji kamar maƙiyi ne; ya hallaka Isra’ila. Ya hallaka wurarenta duka ya kuma hallaka kagaranta. Ya ƙara yawan makoki da baƙin ciki wa Diyar Yahuda.
6 Og han har med Vold nedrevet sit Gærde som en Haves, forstyrret sin Festforsamling; Herren har ladet Festforsamling og Sabbat glemmes i Zion og foragtet Konge og Præst i sin Vredes Heftighed.
Ya rushe haikalinsa kamar lambu; ya hallaka wurin yi masa sujada. Ubangiji ya sa Sihiyona ta manta da bukukkuwanta da kuma ranakunta na Asabbaci; a cikin zafin fushinsa ya watsar da sarki da firist.
7 Herren har forkastet sit Alter, ringeagtet sin Helligdom, overgivet dens Paladsers Mure i Fjendens Haand; man opløftede en Røst i Herrens Hus, som var det en Festforsamlings Dag.
Ubangiji ya ƙi bagadensa ya kuma yi wofi da haikalinsa. Ya ba maƙiyinta fadodinta; suka yi sowa a cikin gidan Ubangiji kamar a ranar da ake yin biki.
8 Herren har besluttet at ødelægge Zions Datters Mur, han har udstrakt en Maalesnor; han har ikke draget sin Haand tilbage fra Ødelæggelsen; og han lod Værn og Mur sørge; sammensunkne ligge de begge.
Ubangiji ya ƙuduri niyya yă rushe bangon da yake kewaye da Diyar Sihiyona. Ya auna da igiyar awo bai fasa hallaka ta ba. Ya sa katanga da katanga duk suka lalace.
9 Hendes Porte sank i Jorden, han ødelagde og sønderbrød hendes Portstænger; hendes Konger og hendes Fyrster ere iblandt Hedningerne; der er ingen Lov, selv hendes Profeter finde ikke Syn fra Herren.
Ƙofofinta sun nutse a cikin ƙasa; ya kakkarya ƙarafanta. Sarakunanta da’ya’yan sarakunanta duk an kai su bauta cikin waɗansu ƙasashe, babu sauran doka, annabawa kuma ba su samun wahayi daga wurin Ubangiji.
10 Zions Datters Ældste sidde paa Jorden, de ere tavse; de kastede Støv over deres Hoved, iførte sig Sæk; Jerusalems Jomfruer sænkede deres Hoved ned imod Jorden.
Dattawan Diyar Sihiyona sun zauna shiru a ƙasa; suka kuma sa rigar buhu.’Yan matan Urushalima suka sunkuyar da kawunansu ƙasa.
11 Mine Øjne forsmægte af Graad, mine Indvolde syde, min Lever er udgydt paa Jorden formedelst mit Folks Datters Ødelæggelse, idet de spæde og diende Børn vansmægte paa Stadens Gader.
Idanuna sun dushe don yawan kuka, raina na cike da baƙin ciki; zuciyata ta karaya domin mutanena sun hallaka, domin yara da jarirai suna suma a kan hanyoyi a cikin birni.
12 De sige til deres Mødre: Hvor er Korn og Vin? idet de vansmægte som saarede paa Stadens Gader, idet de udaande deres Sjæl i deres Moders Skød.
Suna ce wa uwayensu, “Ina burodi da ruwan inabi?” Yayinda suke suma kamar mutanen da aka ji masu ciwo a cikin birni, sa’ad da suke mutuwa a hannuwan uwayensu.
13 Hvad skal jeg vidne for dig, hvorved skal jeg ligne dig, Jerusalems Datter? hvad skal jeg agte dig lig, at jeg kan trøste dig, du Jomfru, Zions Datter? thi din Ødelæggelse er stor som Havet; hvo kan læge dig?
Me zan ce miki? Da me zan kwatanta ki, ke Diyar Urushalima? Da me zan misalta ki, yadda zan iya yi miki ta’aziyya, Ke Budurwa Diyar Sihiyona? Ciwonki yana da zurfi kamar teku. Wane ne zai iya warkar da ke?
14 Dine Profeter havde tomme og daarlige Syner angaaende dig, og de aabenbarede ikke din Misgerning, saa at de afvendte dit Fangenskab; men deres Syner om dig vare tomme Spaadomme og Forførelse.
Wahayin annabawanki ƙarya ne kuma marasa amfani; ba su tona zunubanki ba yadda za su iya ceto ki daga bauta ba. Sun yi miki annabcin ƙarya marar amfani.
15 Alle de, som gaa forbi ad Vejen, klappe i Hænderne over dig, de spotte og ryste med deres Hoved over Jerusalems Datter: Er det den Stad, hvilken man sagde at være hel dejlig, al Jordens Glæde?
Duk masu wucewa suna yi miki tafi na reni; suna yi wa Diyar Urushalima tsaki suna kaɗa kai suna cewa, “Wannan ne birnin da aka ce kyakkyawa ne, mai farantawa dukan duniya rai?”
16 Alle dine Fjender opspile deres Mund imod dig, de spotte og skære Tænder; de sige: Vi have opslugt den; dette er kun den Dag, som vi biede efter, vi have fundet, vi have set det.
Maƙiyanki duka suna ta surutu game da ke; suna tsaki suna cizon haƙora suna cewa, “Mun hallaka ta. Wannan ce ranar da muke jira; yau mun gan ta.”
17 Herren har gjort det, som han havde besluttet, han har udført sit Ord, som han fra gamle Dage havde befalet, han har nedbrudt og ikke sparet; og han lod Fjenden glæde sig over dig, han ophøjede dine Modstanderes Horn.
Ubangiji ya yi abin da ya shirya; ya cika maganarsa, wadda ya umarta tun daɗewa. Ya jefar da ke ba tausayi, ya bari maƙiya sun yi nasara da ke, ya ɗaukaka ƙahon maƙiyanki.
18 Deres Hjerte raabte til Herren: O Zions Datters Mur! lad Taarerne strømme ned som en Bæk Dag og Nat, giv dig ingen Hvile, lad din Øjesten ikke være rolig!
Zuciyar mutane ta yi kuka ga Ubangiji. Ya bangon Diyar Urushalima, bar hawayenki su zuba kamar rafi dare da rana; kada ki huta, kada idanunki su huta.
19 Staa op, raab højt om Natten, med Begyndelsen af Nattevagterne, udøs dit Hjerte som Vand for Herrens Ansigt; opløft dine Hænder til ham for dine spæde Børns Liv; thi de vansmægte af Hunger paa alle Gadehjørner.
Ki tashi, ki yi kuka cikin dare, dare na yi sai ki fara kuka; kina buɗewa Ubangiji zuciyarki. Ki ɗaga hannuwanki gare shi domin rayukan’ya’yanki, waɗanda suka suma don yunwa a kan kowane titi.
20 Herre! se og sku, hvem du har handlet saaledes med; mon Kvinder skulle æde deres Livsfrugt, de spæde Børn, som man bærer paa Hænderne? mon Præst og Profet skulle ihjelslaas i Herrens Helligdom?
“Ka duba, ka gani ya Ubangiji. Wane ne ka taɓa yi wa haka? Ko ya kamata uwaye su ci’ya’yansu,’ya’yan da suka yi reno? Ko ya kamata a kashe firistoci da annabawa a cikin haikalin Ubangiji?
21 Der ligger paa Jorden i Gaderne ung og gammel, mine Jomfruer og mine unge Karle ere faldne for Sværdet; du ihjelslog paa din Vredes Dag, du slagtede, du sparede ikke.
“Matasa da tsofaffi duk suna kwanciya a cikin ƙurar tituna; an karkashe matasa da’yan matana da takobi. Ka kashe su a ranar fushinka; ka kashe su ba tausayi.
22 Du kalder som til en Festforsamlings Dag Rædsler over mig trindt omkring fra, og der er ingen, som undkom eller blev tilovers paa Herrens Vredes Dag; dem, som jeg havde baaret paa Hænderne og opdraget, dem har min Fjende gjort Ende paa.
“Kamar yadda kake yin gayyata a ranar biki, haka kake kawo mini tsoro a kowane gefe. A ranar fushin Ubangiji ba mai tserewa ba wanda zai tsira; maƙiyina ya kashe waɗanda na yi renonsu, na kuma lura da su.”