< Jonas 1 >
1 Og Herrens Ord kom til Jonas, Amithajs Søn, saa lydende:
Maganar Ubangiji ta zo wa Yunana ɗan Amittai cewa,
2 Gør dig rede, gak til Ninive, den store Stad, og raab over den; thi deres Ondskab er stegen op for mit Ansigt.
“Tafi babban birnin nan Ninebe ka yi mata wa’azi, saboda muguntarta ta haura zuwa gabana.”
3 Men Jonas gjorde sig rede for at fly til Tharsis fra Herrens Ansigt; og han drog ned til Jafo og fandt et Skib, som vilde fare til Tharsis, og han gav Fragt derfor og gik om Bord for at fare med dem til Tharsis fra Herrens Ansigt.
Amma Yunana ya gudu daga Ubangiji ya nufi Tarshish. Ya gangara zuwa Yaffa, inda ya sami jirgin ruwa mai shirin tashi daga tashar. Bayan ya biya kuɗin tafiya, sai ya shiga jirgi ya kama hanya zuwa Tarshish don yă tsere wa Ubangiji.
4 Men Herren kastede et stort Vejr paa Havet, og der blev en stor Storm paa Havet, og Skibet lod til at skulle sønderbrydes.
Sai Ubangiji ya aika da babban iska a bisan teku, hadiri ya tsananta ƙwarai har jirgin ya yi barazanar farfashewa.
5 Og Skibsfolkene frygtede, og de raabte hver til sin Gud, og de kastede Redskaberne, som vare udi Skibet, i Havet for at skaffe sig Lettelse; men Jonas var stegen ned i det nederste Skibsrum og laa og sov hart.
Dukan matuƙan jirgin suka tsorata, kowannensu kuma ya yi kuka ga allahnsa, suka kuma jefar da kayan jirgi a cikin teku domin su rage nauyin jirgin. Ana cikin haka, ashe, Yunana ya sauka can ƙarƙashin jirgi ya je ya kwanta, yana ta sharar barcinsa.
6 Men Styrmanden gik til ham og sagde til ham: Hvorledes kan du sove saa hart? staa op, kald paa din Gud, maaske den Gud vil tænke mildelig paa os, at vi ikke forgaa.
Sai kyaftin ɗin ya je wajensa ya ce masa, “Don me kake barci? Tashi ka kira bisa ga allahnka! Mai yiwuwa yă ji mu, yă cece mu don kada mu hallaka.”
7 Og de sagde, den ene til den anden: Kommer, og lader os kaste Lod, at vi kunne faa at vide, for hvis Skyld denne Ulykke hændes os; og de kastede Lod, og Lodden faldt paa Jonas.
Matuƙan jirgin suka ce wa juna, “Ku zo, mu jefa ƙuri’a mu ga wa ke da alhakin wannan masifa.” Sai suka jefa ƙuri’a, ƙuri’ar kuwa ta fāɗa a kan Yunana.
8 Da sagde de til ham: Kundgør os dog, for hvis Skyld denne Ulykke hændes os! hvad er din Bestilling? og hvorfra kommer du? hvilket er dit Land? og af hvad Folk er du?
Saboda haka suka tambaye shi suka ce, “Yanzu, gaya mana, dalilin da ya sa wannan masifa ta zo mana? Mene ne aikinka? Daga ina ka fito? Ina ne ƙasarka? Daga wacce kabila ce ka fito?”
9 Og han sagde til dem: Jeg er en Hebræer, og jeg frygter Herren, Himmelens Gud, som har skabt Havet og det tørre Land.
Sai ya amsa, “Ni mutumin Ibraniyawa ne, ina kuma bauta wa Ubangiji Allah na sama, wanda ya yi teku da tuddai.”
10 Da grebes Mændene af en stor Frygt, og de sagde til ham: Hvad har du dog gjort? thi Mændene havde faaet at vide, at han flyede fra Herrens Ansigt, thi han havde kundgjort dem det.
Sai matuƙan jirgin suka tsorata ƙwarai, suka ce masa, “Wane irin mugun abu ne ka aikata haka?” (Sun gane cewa yana gudu ne daga wurin Ubangiji, domin ya riga ya faɗa musu.)
11 Og de sagde til ham: Hvad skulle vi gøre dig, at Havet kan stilles for os? thi Havet vedblev at storme mere og mere.
Sai tekun ya daɗa rikicewa. Sai suka tambaye shi, “Me za mu yi da kai domin tekun yă daina hauka?”
12 Og han sagde til dem: Tager mig, og kaster mig i Havet, saa stilles Havet for eder; thi jeg ved, at denne store Storm er over eder for min Skyld.
Ya amsa musu ya ce, “Ku ɗauke ni ku jefa a cikin teku, tekun zai kwanta. Na san cewa laifina ne ya jawo wannan babban hadirin da ya auka muku.”
13 Og Mændene roede for at naa tilbage til Land, men de kunde ikke; thi Havet vedblev at storme imod dem mere og mere.
Maimakon mutanen su yi haka, sai suka yi ƙoƙari su tura jirgin ruwan zuwa bakin teku. Amma ba su iya ba, saboda iskar ta sa tekun ya yi ta ƙara hauka.
14 Da raabte de til Herren og sagde: Ak, Herre! lad os dog ikke omkomme for denne Mands Sjæls Skyld, og læg ikke uskyldigt Blod paa os; thi du, Herre! har gjort, som det behagede dig.
Sai suka yi kuka ga Ubangiji suka ce, “Ya Ubangiji, in ka yarda kada ka bar mu mu mutu saboda ran mutumin nan. Kada ka yi mana hukuncin masu kisankai, gama kai ne, ya Ubangiji, ka ga ya gamshe ka.”
15 Og de toge Jonas og kastede ham i Havet; da blev Havet stille efter sin heftige Brusen.
Sa’an nan suka ɗauki Yunana suka jefar da shi daga jirgin, sai tekun ya kwanta.
16 Og Mændene frygtede Herren med en stor Frygt, og de ofrede Herren Slagtoffer og gjorde Løfter.
Ganin haka sai mutanen suka cika da tsoron Ubangiji, suka kuma miƙa wa Ubangiji hadaya, suka yi wa’adi da shi.
17 Og Herren beskikkede en stor Fisk til at opsluge Jonas, og Jonas var i Fiskens Bug tre Dage og tre Nætter.
Amma Ubangiji ya tanada wani babban kifi da zai haɗiye Yunana, Yunana kuwa ya yi yini uku da dare uku a ciki cikin kifin.