< Jonas 4 >

1 Men det gjorde Jonas overmaade meget ondt, og hans Vrede optændtes.
Sai abin ya ɓata wa Yunana rai ƙwarai har ya yi fushi.
2 Og han bad til Herren og sagde: Ak, Herre! var dette ikke mit Ord, der jeg endnu var i mit Land? derfor har jeg villet forekomme det ved at fly til Tharsis; thi jeg ved, at du er en naadig og barmhjertig Gud, langmodig og af stor Miskundhed, og angrer det onde.
Sai ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, ba irin abin da na faɗa ke nan ba tun ina gida? Wannan ne ya sa na yi ƙoƙarin tserewa zuwa Tarshish. Ai, na sani kai Allah ne mai alheri da tausayi, mai jinkirin fushi da cikakkiyar ƙauna, kai Allah ne mai dakatar da nufinka na yin hukunci.
3 Og nu, Herre! tag dog min Sjæl fra mig; thi det er mig bedre at dø end at leve.
Yanzu, ya Ubangiji, ka ɗauki raina, domin ya fi sauƙi a gare ni in mutu da in rayu.”
4 Og Herren sagde: Mon det er ret, at din Vrede optændes?
Amma Ubangiji ya amsa, ya ce; “Daidai ne ka yi fushi?”
5 Og Jonas gik ud af Staden og tog Ophold Østen for Staden, og han gjorde sig der en Hytte og satte sig under den i Skyggen, indtil han kunde se, hvad der vilde ske med Staden.
Sai Yunana ya fita daga birnin ya yi wajen gabas, ya zauna. A nan ya yi wa kansa rumfa, ya zauna cikin inuwarta yana jira yă ga abin da zai sami birnin.
6 Da beskikkede Gud Herren et Kikajon, og det voksede op over Jonas til at give Skygge over hans Hoved, at fri ham fra hans Onde; og Jonas glædede sig over dette Kikajon med stor Glæde.
Sai Ubangiji Allah ya sa wata’yar kuringa ta tsiro, ta yi girma a inda Yunana yake, don ta inuwantar da shi, yă ji daɗi. Yunana kuwa ya yi murna matuƙa da wannan kuringa.
7 Men Gud beskikkede, da Morgenrøden den næste Dag oprandt, en Orm, og den stak Kikajonet, og det visnede.
Amma kashegari da safe sai Allah ya sa tsutsa ta cinye’yar kuringar har ta mutu.
8 Og det skete, der Solen gik op, da beskikkede Gud en lummer Østenvind, og Solen stak Jonas paa Hovedet, saa han blev afmægtig; da bad han, at hans Sjæl maatte dø, og sagde: Det er bedre, at jeg dør end lever.
Sa’ad da rana ta yi sama, sai Allah ya sa iskar gabas mai zafi ta huro, zafin ranar kuma ya buga kan Yunana, har ya ji sai ka ce zai suma. Ya so a ce ya mutu ma, sai ya ce, “Gara in mutu da a ce ina zaune da rai.”
9 Men Gud sagde til Jonas: Mon det er ret, at din Vrede optændes for dette Kikajons Skyld? og han sagde: Ja, det er ret, at min Vrede er optændt indtil Døden.
Amma Allah ya ce wa Yunana, “Daidai ne ka yi fushi saboda wannan kuringa?” Sai Yunana ya ce, “I, daidai ne, ina fushi matuƙa, har ina so da na mutu ma.”
10 Og Herren sagde: Du ynkes over Kikajonet, som du ikke har arbejdet for og ej faaet til at vokse, det, som blev til paa een Nat og blev ødelagt paa een Nat;
Sai Ubangiji ya ce, “Ai, wannan kuringa ta tsira dare ɗaya ta kuma ɓace kafin dare na biyu, ba ka yi wata wahala dominta ba, ba kai ne ka sa ta yi girma ba, duk da haka ranka ya ɓace saboda ita.
11 og jeg skulde ikke ynkes over Ninive, den store Stad, i hvilken der er mange flere end tolv Gange ti Tusinde Mennesker, som ikke vide Forskel paa højre og venstre, og mange Dyr?
Ashe, ba dole ne in ji tausayin babban birnin nan Ninebe mai mutum sama da dubu ɗari da ashirin marasa alhaki, da kuma dabbobi masu yawa ba?”

< Jonas 4 >