< Johannes 3 >

1 Men der var en Mand af Farisæerne, han hed Nikodemus, en Raadsherre iblandt Jøderne.
akwai wani Bafarise da ake kira Nikodimu, shugaba a cikin Yahudawa.
2 Denne kom til ham om Natten og sagde til ham: „Rabbi! vi vide, at du er en Lærer kommen fra Gud; thi ingen kan gøre disse Tegn, som du gør, uden Gud er med ham.‟
Wannan mutum ya zo wurin Yesu da dare ya ce masa, “Rabbi, mun sani cewa kai malami ne da kazo daga wurin Allah, gama ba wanda zai iya yin wadannan alamu da kake yi sai idan Allah na tare da shi.”
3 Jesus svarede og sagde til ham: „Sandelig, sandelig, siger jeg dig, uden nogen bliver født paany, kan han ikke se Guds Rige.‟
Yesu ya amsa masa, “Hakika, hakika, idan ba a sake haifuwar mutum ba, ba zai iya ganin mulkin Allah ba.”
4 Nikodemus siger til ham: „Hvorledes kan et Menneske fødes, naar han er gammel? Mon han kan anden Gang komme ind i sin Moders Liv og fødes?‟
Nikodimu ya ce masa, “Yaya za a sake haifuwar mutum bayan ya tsufa? Ba zai iya sake shiga cikin cikin uwarsa kuma a haife shi ba, zai iya?”
5 Jesus svarede: „Sandelig, sandelig, siger jeg dig, uden nogen bliver født af Vand og Aand, kan han ikke komme ind i Guds Rige.
Yesu ya amsa, “Hakika, hakika, idan ba a haifi mutum da ruwa da kuma Ruhu ba, ba zai iya shiga cikin mulkin Allah ba.
6 Hvad der er født af Kødet, er Kød; og hvad der er født af Aanden, er Aand.
Abin da aka haifa ta wurin jiki, jiki ne, kuma abin da aka haifa ta wurin Ruhu, Ruhu ne.
7 Forundre dig ikke over, at jeg sagde til dig: I maa fødes paany.
Kada ka yi mamaki don na ce maka, 'dole a maya haifuwar ka.'
8 Vinden blæser, hvorhen den vil, og du hører dens Susen, men du ved ikke, hvorfra den kommer, og hvor den farer hen; saaledes er det med hver den, som er født af Aanden.‟
Iska takan hura duk inda ta ga dama. Ka kan ji motsin ta, amma ba ka san inda ta fito ko inda za ta tafi ba. Haka duk wanda aka haifa daga Ruhu.”
9 Nikodemus svarede og sagde til ham: „Hvorledes kan dette ske?‟
Nikodimu ya amsa yace masa, “Yaya wannan zai yiwu?”
10 Jesus svarede og sagde til ham: „Er du Israels Lærer og forstaar ikke dette?
Yesu ya amsa yace masa, “Kai malami ne a Israila amma ba ka san wadannan al'amura ba?
11 Sandelig, sandelig, siger jeg dig, vi tale det, vi vide, og vidne det, vi have set; og I modtage ikke vort Vidnesbyrd.
Hakika, hakika, ina gaya maka, muna fadin abubuwan da muka sani, kuma muna shaida abubuwan da muka gani. Duk da haka ba ku karbi shaidar mu ba.
12 Naar jeg siger eder de jordiske Ting, og I ikke tro, hvorledes skulle I da tro, naar jeg siger eder de himmelske?
Idan na gaya maka abubuwan da ke na duniya amma baka gaskata ba, to yaya zaka gaskata idan na gaya maka abubuwa na sama?
13 Og ingen er faren op til Himmelen, uden han, som for ned fra Himmelen, Menneskesønnen, som er i Himmelen.
Babu wanda ya taba hawa zuwa sama sai dai shi wanda ya sauko daga sama: wato Dan Mutum.
14 Og ligesom Moses ophøjede Slangen i Ørkenen, saaledes bør Menneskesønnen ophøjes,
Kamar yadda Musa ya ta da maciji a jeji, haka ma dole a ta da Dan Mutum
15 for at hver den, som tror, skal have et evigt Liv i ham. (aiōnios g166)
domin dukan wadanda suka bada gaskiya gareshi su sami rai na har abada. (aiōnios g166)
16 Thi saaledes elskede Gud Verden, at han gav sin Søn den enbaarne, for at hver den, som tror paa ham, ikke skal fortabes, men have et evigt Liv. (aiōnios g166)
Gama Allah ya kaunaci duniya sosai, har ya ba da makadaicin Dansa, domin duk wanda ya bada gaskiya gareshi, kada ya mutu, amma ya samu rai madawwami. (aiōnios g166)
17 Thi Gud sendte ikke sin Søn til Verden, for at han skal dømme Verden, men for at Verden skal frelses ved ham.
Gama Allah bai aiko da Dansa cikin duniya domin ya kayar da duniya ba, amma domin a ceci duniya ta wurin sa.
18 Den, som tror paa ham, dømmes ikke; men den, som ikke tror, er allerede dømt, fordi han ikke har troet paa Guds enbaarne Søns Navn.
Duk wanda ya bada gaskiya gare shi ba a kayar da shi ba, amma duk wanda bai bada gaskiya gare shi ba an riga an kayar da shi, domin bai bada gaskiya ga sunan wannan da shi kadai ne Dan Allah ba.
19 Og dette er Dommen, at Lyset er kommet til Verden, og Menneskene elskede Mørket mere end Lyset; thi deres Gerninger vare onde.
Wannan shi ne dalilin shari'ar, domin haske ya zo duniya, amma mutane suka kaunaci duhu fiye da hasken, sabili da ayyukan su na mugunta ne.
20 Thi hver den, som øver ondt, hader Lyset og kommer ikke til Lyset, for at hans Gerninger ikke skulle revses.
Domin duk wanda ke mugayen ayyuka ya ki haske, kuma baya zuwa wurin hasken domin kada ayyukansa su bayyanu.
21 Men den, som gør Sandheden, kommer til Lyset, for at hans Gerninger maa blive aabenbare; thi de ere gjorte i Gud.‟
Sai dai duk wanda yake aikata gaskiya kan zo wurin hasken domin ayyukansa, da ake aiwatarwa ga Allah, su bayyanu.
22 Derefter kom Jesus og hans Disciple ud i Judæas Land, og han opholdt sig der med dem og døbte.
Bayan wannan, Yesu da almajiransa suka tafi kasar Yahudiya. A can ya dan zauna tare da su ya kuma yi Baftisma.
23 Men ogsaa Johannes døbte i Ænon, nær ved Salem, fordi der var meget Vand der; og man kom derhen og lod sig døbe.
Yahaya ma yana Baftisma a Ainon kusa da Salim domin akwai ruwa da yawa a can. Mutane na zuwa wurin sa yana masu Baftisma,
24 Thi Johannes var endnu ikke kastet i Fængsel.
domin a lokacin ba a jefa Yahaya a kurkuku ba tukuna.
25 Da opkom der en Strid imellem Johannes's Disciple og en Jøde om Renselse.
Sai gardama ta taso tsakanin almajiran Yahaya da wani Bayahude akan al'adun tsarkakewa.
26 Og de kom til Johannes og sagde til ham: „Rabbi! han, som var hos dig hinsides Jordan, han, hvem du gav Vidnesbyrd, se, han døber, og alle komme til ham.‟
Suka je wurin Yahaya suka ce, “Rabbi, wanda yake tare da kai a dayan ketaren kogin Urdun, kuma ka shaida shi, duba, yana baftisma, kuma mutane duka suna zuwa wurin sa.”
27 Johannes svarede og sagde: „Et Menneske kan slet intet tage, uden det er ham givet fra Himmelen.
Yahaya ya amsa, “Mutum ba zai iya samun wani abu ba sai an ba shi daga sama.
28 I ere selv mine Vidner paa, at jeg sagde: Jeg er ikke Kristus, men jeg er udsendt foran ham.
Ku da kanku zaku shaida na ce, 'Ba ni ne Almasihu ba' amma amaimakon haka, 'an aiko ni kafin shi.'
29 Den, som har Bruden, er Brudgom; men Brudgommens Ven, som staar og hører paa ham, glæder sig meget over Brudgommens Røst. Saa er da denne min Glæde bleven fuldkommen.
Amaryar ta angon ce. Yanzu abokin angon, wanda ke tsaye yana saurarensa, yana murna sosai saboda muryan angon. Murnata ta cika domin wannan.
30 Han bør vokse, men jeg forringes.
Dole shi ya karu, ni kuma in ragu.
31 Den, som kommer ovenfra, er over alle; den, som er af Jorden, er af Jorden og taler af Jorden; den, som kommer fra Himmelen, er over alle.
Shi wanda ya fito daga sama ya fi kowa. Shi Wanda ya zo daga duniya, na duniya ne, kuma game da duniya yake magana. Shi wanda ya fito daga sama yana saman kowa.
32 Og det, som han har set og hørt, vidner han; og ingen modtager hans Vidnesbyrd.
Ya shaida abubuwan da ya ji ya kuma gani, amma babu wanda ya karbi shaidarsa.
33 Den, som har modtaget hans Vidnesbyrd, har beseglet, at Gud er sanddru.
Duk wanda ya karbi shaidarsa ya tabbatar Allah gaskiya ne.
34 Thi han, hvem Gud udsendte, taler Guds Ord; Gud giver nemlig ikke Aanden efter Maal.
Domin duk wanda Allah ya aika kan yi magana da kalmomin Allah. Domin bai bada Ruhun da ma'auni ba.
35 Faderen elsker Sønnen og har givet alle Ting i hans Haand.
Uban ya kaunaci Dan, ya kuma ba da dukan komai a hanunsa.
36 Den, som tror paa Sønnen, har et evigt Liv; men den, som ikke vil tro Sønnen, skal ikke se Livet, men Guds Vrede bliver over ham.‟ (aiōnios g166)
Shi wanda ya bada gaskiya ga Dan ya na da rai madawwami, amma wanda ya ki yiwa Dan biyayya ba zai ga rai ba, amma fushin Allah na kansa. (aiōnios g166)

< Johannes 3 >