< Johannes 16 >

1 „Dette har jeg talt til eder, for at I ikke skulle forarges.
“Na faɗa muku wannan duka, domin kada ku bauɗe.
2 De skulle udelukke eder af Synagogerne, ja, den Tid skal komme, at hver den, som slaar eder ihjel, skal mene, at han viser Gud en Dyrkelse.
Za su kore ku daga majami’a; lalle, lokaci yana zuwa da duk wanda ya kashe ku, zai ɗauka yana yin wa Allah hidima ne.
3 Og dette skulle de gøre, fordi de hverken kende Faderen eller mig.
Za su yi waɗannan abubuwa ne domin ba su san Uba ko ni ba.
4 Men dette har jeg talt til eder, for at I, naar Timen kommer, skulle komme i Hu, at jeg har sagt eder det; men dette sagde jeg eder ikke fra Begyndelsen, fordi jeg var hos eder.
Na faɗa muku wannan, domin in lokacin ya yi, ku tuna na gargaɗe ku. Ban faɗa muku wannan tun da fari ba domin ina tare da ku.
5 Men nu gaar jeg hen til ham, som sendte mig, og ingen af eder spørger mig: Hvor gaar du hen?
“Yanzu zan tafi wurin wanda ya aiko ni, duk da haka ba waninku da ya tambaye ni, ‘Ina za ka?’
6 Men fordi jeg har talt dette til eder, har Bedrøvelsen opfyldt eders Hjerte.
Saboda na faɗa waɗannan abubuwa ga shi kun cika da baƙin ciki.
7 Men jeg siger eder Sandheden: Det er eder gavnligt, at jeg gaar bort, thi gaar jeg ikke bort, kommer Talsmanden ikke til eder; men gaar jeg bort, saa vil jeg sende ham til eder.
Amma gaskiya nake gaya muku. Don amfaninku ne zan tafi. Sai ko na tafi, in ba haka ba Mai Taimakon nan ba zai zo muku ba. Amma in na tafi, zan aiko shi gare ku.
8 Og naar han kommer, skal han overbevise Verden om Synd og om Retfærdighed og om Dom.
Sa’ad da ya zo kuwa, zai kā da duniya a kan zunubi da adalci da kuma hukunci,
9 Om Synd, fordi de ikke tro paa mig;
a kan zunubi, domin mutane ba su gaskata da ni ba;
10 men om Retfærdighed, fordi jeg gaar til min Fader, og I se mig ikke længere;
a kan adalci, domin zan tafi wurin Uba, inda ba za ku ƙara ganina ba;
11 men om Dom, fordi denne Verdens Fyrste er dømt.
a kan hukunci kuma, domin an yanke hukunci a kan mai mulkin duniyan nan.
12 Jeg har endnu meget at sige eder; men I kunne ikke bære det nu.
“Ina da sauran abubuwa da yawa da zan faɗa muku, amma ba za ku iya ɗauka a yanzu ba.
13 Men naar han, Sandhedens Aand, kommer, skal han vejlede eder til hele Sandheden; thi han skal ikke tale af sig selv, men hvad som helst han hører, skal han tale, og de kommende Ting skal han forkynde eder.
Amma sa’ad da shi, Ruhun gaskiya ya zo, zai bi da ku zuwa ga dukan gaskiya. Ba zai yi magana don kansa ba; zai faɗi abin da ya ji ne kaɗai, zai kuma faɗa muku abin da bai faru ba tukuna.
14 Han skal herliggøre mig; thi han skal tage af mit og forkynde eder.
Zai kawo ɗaukaka gare ni ta wurin ɗaukan abin da yake nawa, ya bayyana muku.
15 Alt, hvad Faderen har, er mit; derfor sagde jeg, at han skal tage af mit og forkynde eder.
Duk abin da yake na Uba nawa ne. Shi ya sa na ce, ‘Ruhun zai ɗauko daga abin da yake nawa, yă bayyana muku.’”
16 Om en liden Stund skulle I ikke se mig længer, og atter om en liden Stund skulle I se mig.”
Yesu ya ci gaba da cewa, “Jim kaɗan, ba za ku ƙara ganina ba, sa’an nan bayan an jima kaɗan kuma, za ku gan ni.”
17 Da sagde nogle af hans Disciple til hverandre: „Hvad er dette, som han siger os: Om en liden Stund skulle I ikke se mig, og atter om en liden Stund skulle I se mig, og: Jeg gaar hen til Faderen?”
A nan fa sai waɗansu almajiransa suka ce wa juna, “Me yake nufi da cewa, ‘Jim kaɗan ba za ku ƙara ganina ba, kuma bayan an jima kaɗan, za ku gan ni,’ da kuma, ‘Domin zan tafi wurin Uba’?”
18 De sagde altsaa: „Hvad er dette, han siger: Om en liden Stund? Vi forstaa ikke, hvad han taler.”
Suka yi ta tambaya, “Me yake nufi da ‘jim kaɗan’? Ba mu fahimci abin da yake faɗi ba.”
19 Jesus vidste, at de vilde spørge ham, og han sagde til dem: „I spørge hverandre om dette, at jeg sagde: Om en liden Stund skulle I ikke se mig, og atter om en liden Stund skulle I se mig.
Yesu ya gane suna so su tambaye shi game da wannan, sai ya ce musu, “Kuna tambayar juna game da abin da nake nufi da na ce, ‘Jim kaɗan ba za ku ƙara ganina ba, da kuma bayan an jima kaɗan, za ku gan ni’?
20 Sandelig, sandelig, siger jeg eder, I skulle græde og jamre, men Verden skal glæde sig; I skulle være bedrøvede, men eders Bedrøvelse skal blive til Glæde.
Gaskiya nake gaya muku, za ku yi kuka da kuma gunji, yayinda duniya take murna. Za ku yi baƙin ciki, amma baƙin cikinku zai koma farin ciki.
21 Naar Kvinden føder, har hun Bedrøvelse, fordi hendes Time er kommen; men naar hun har født Barnet, kommer hun ikke mere sin Trængsel i Hu af Glæde over, at et Menneske er født til Verden.
Macen da za tă haihu takan yi naƙuda domin lokacinta ya yi; amma sa’ad da ta haihu, sai ta manta da wahalar domin farin ciki an haifi jariri a duniya.
22 Ogsaa I have da vel nu Bedrøvelse, men jeg skal se eder igen, og eders Hjerte skal glædes, og ingen tager eders Glæde fra eder.
Haka ku ma, yanzu ne lokacin baƙin cikinku, amma zan sāke ganinku za ku kuma yi farin ciki, ba kuwa wanda zai ɗauke muku farin cikinku.
23 Og paa den Dag skulle I ikke spørge mig om noget. Sandelig, sandelig, siger jeg eder, hvad som helst I bede Faderen om, skal han give eder i mit Navn.
A ranan nan, ba za ku sāke tambaya ta kome ba. Gaskiya nake gaya muku, Ubana zai ba ku kome da kuka roƙa cikin sunana.
24 Hidindtil have I ikke bedet om noget i mit Navn; beder, og I skulle faa, for at eders Glæde maa blive fuldkommen.
Har yanzu dai ba ku roƙi kome cikin sunana ba. Ku roƙa za ku kuwa samu, farin cikinku kuwa zai zama cikakke.
25 Dette har jeg talt til eder i Lignelser; der kommer en Time, da jeg ikke mere skal tale til eder i Lignelser, men frit ud forkynde eder om Faderen.
“Ko da yake ina magana da misalai, lokaci yana zuwa da ba zan ƙara yin magana da misalai ba, sai dai in faɗa muku a fili game da Ubana.
26 Paa den Dag skulle I bede i mit Navn, og jeg siger ikke til eder, at jeg vil bede Faderen for eder;
A ranan nan, za ku roƙa a cikin sunana. Ban ce zan roƙi Uba a madadinku ba.
27 thi Faderen selv elsker eder, fordi I have elsket mig og troet, at jeg er udgaaet fra Gud.
Ai, shi Uban kansa yana ƙaunarku domin kun ƙaunace ni kun kuma gaskata cewa daga Allah na fito.
28 Jeg udgik fra Faderen og er kommen til Verden; jeg forlader Verden igen og gaar til Faderen.”
Na fito daga wurin Uba, na kuma shigo duniya, yanzu kuwa zan bar duniya in koma wurin Uba.”
29 Hans Disciple sige til ham: „Se, nu taler du frit ud og siger ingen Lignelse.
Sai almajiran Yesu suka ce, “Haba, yanzu ne fa kake magana a sarari ba tare da misalai ba.
30 Nu vide vi, at du ved alle Ting og ikke har nødig, at nogen spørger dig; desaarsag tro vi, at du er udgaaet fra Gud.”
Yanzu mun gane cewa ka san kome ba sai wani ya tambaye ka ba. Wannan ya sa muka gaskata ka fito daga Allah.”
31 Jesus svarede dem: „Nu tro I!
Yesu ya amsa ya ce, “A ƙarshe kun gaskata!
32 Se, den Time kommer, og den er kommen, da I skulle adspredes hver til sit og lade mig alene; dog, jeg er ikke alene, thi Faderen er med mig.
Amma lokaci na zuwa, har ma ya yi, da za a warwatsa ku, kowa yă koma gidansa. Za ku bar ni ni kaɗai. Duk da haka ba ni kaɗai ba ne, gama Ubana yana tare da ni.
33 Dette har jeg talt til eder, for at I skulle have Fred i mig. I Verden have I Trængsel; men værer frimodige, jeg har overvundet Verden.”
“Na faɗa muku waɗannan abubuwa ne, domin a cikina ku sami salama. A duniyan nan za ku sha wahala. Amma ku yi ƙarfin hali! Na yi nasara a kan duniya.”

< Johannes 16 >