< Johannes 1 >

1 I Begyndelsen var Ordet, og Ordet var hos Gud, og Ordet var Gud.
A cikin farko akwai Kalma, Kalmar kuma tana tare da Allah, wannan Kalma kuwa Allah ne.
2 Dette var i Begyndelsen hos Gud.
Shi kuwa tare da Allah yake tun farko.
3 Alle Ting ere blevne til ved det, og uden det blev end ikke een Ting til af det, som er.
Dukan abu ta wurinsa aka yi su, babu abin da aka halitta sai ta wurin sa.
4 I det var Liv, og Livet var Menneskenes Lys.
A cikinsa rai ya ke, kuma wannan rai ya zama haske ga dukan mutane.
5 Og Lyset skinner i Mørket, og Mørket begreb det ikke.
Hasken ya haskaka a cikin duhu, kuma duhun bai rinjaye shi ba.
6 Der kom et Menneske, udsendt fra Gud, hans Navn var Johannes.
Akwai wani mutum wanda Allah ya aiko, mai suna Yahaya.
7 Denne kom til et Vidnesbyrd, for at han skulde vidne om Lyset, for at alle skulde tro ved ham.
Ya zo a matsayin mai ba da shaida game da hasken, domin kowa ya ba da gaskiya ta wurinsa.
8 Han var ikke Lyset, men han skulde vidne om Lyset.
Ba Yahaya ne hasken ba, amma ya zo ne domin ya shaida hasken.
9 Det sande Lys, der oplyser hvert Menneske, var ved at komme til Verden.
Wannan shine haske na gaskiya mai ba da haske ga dukan mutane, da ke zuwa cikin duniya.
10 Han var i Verden, og Verden er bleven til ved ham, og Verden kendte ham ikke.
Yana cikin duniya, kuma an halicci duniya ta wurinsa, amma duniya bata san shi ba.
11 Han kom til sit eget, og hans egne toge ikke imod ham.
Ya zo wurin nasa, amma nasa basu karbe shi ba.
12 Men saa mange, som toge imod ham, dem gav han Magt til at vorde Guds Børn, dem, som tro paa hans Navn;
Amma duk iyakar wadanda suka karbe shi, suka kuma ba da gaskiya ga sunansa, ya ba su 'yanci su zama 'ya'yan Allah.
13 hvilke ikke bleve fødte af Blod, ej heller af Køds Villie, ej heller af Mands Villie, men af Gud.
Wadanda aka haife su ba ta wurin jini ba, ko ta wurin nufin jiki, ko nufin mutum, amma ta wurin Allah.
14 Og Ordet blev Kød og tog Bolig iblandt os, og vi saa hans Herlighed, en Herlighed, som en enbaaren Søn har den fra sin Fader, fuld af Naade og Sandhed.
Kalmar kuma ya zama jiki ya zauna cikin mu. Mun ga daukakarsa, daukaka irin ta makadaici shi kadai wanda ya zo daga Uban, cike da alheri da gaskiya.
15 Johannes vidner om ham og raaber og siger: „Ham var det, om hvem jeg sagde: Den, som kommer efter mig, er kommen foran mig; thi han var før mig.‟
Yahaya ya yi shaida akansa yana kira da karfi, cewa, “Wannan shine wanda na yi magana a kansa cewa, 'Shi wanda ke zuwa bayana, ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'”
16 Thi af hans Fylde have vi alle modtaget, og det Naade over Naade.
Domin daga cikarsa ne muka karbi alheri akan alheri.
17 Thi Loven blev given ved Moses; Naaden og Sandheden er kommen ved Jesus Kristus.
Gama shari'a ta zo daga wurin Musa. Alheri da gaskiya sun zo ta wurin Yesu Almasihu.
18 Ingen har nogen Sinde set Gud; den enbaarne Søn, som er i Faderens Skød, han har kundgjort ham.
Babu lokacin da wani ya taba ganin Allah, shi wanda shi kadai ne Allah, wanda ke jingine da kirjin Uba, shi ya bayyana shi.
19 Og dette er Johannes's Vidnesbyrd, da Jøderne sendte Præster og Leviter ud fra Jerusalem, for at de skulde spørge ham: „Hvem er du?‟
Wannan ita ce shaidar Yahaya sa'adda Yahudawa suka aika da Firistoci da Lawiyawa zuwa gareshi don su tambaye shi, “Wanene kai?”
20 Og han bekendte og nægtede ikke, og han bekendte: „Jeg er ikke Kristus.‟
Ya fada dalla dalla, kuma bai musunta ba, yana amsa masu cewa, “ba nine Almasihu ba.”
21 Og de spurgte ham: „Hvad da? Er du Elias?‟ Han siger: „Det er jeg ikke.‟ „Er du Profeten?‟ Og han svarede: „Nej.‟
Sai suka tambaye shi, “To kai wanene? Kai Iliya ne?” Yace, “Ba ni ba ne.” Suka ce, “Kai ne anabin?” Ya amsa, “A'a”.
22 Da sagde de til ham: „Hvem er du? For at vi kunne give dem Svar, som have udsendt os; hvad siger du om dig selv?‟
Sai suka ce masa, “Kai wanene, domin mu bada amsa ga wadanda suka aiko mu? Me kake fadi game da kanka?”
23 Han sagde: „Jeg er en Røst af en, som raaber i Ørkenen: Jævner Herrens Vej, som Profeten Esajas har sagt.‟
Yace, “Ni murya ne, da ke kira cikin jeji, 'Ku daidaita hanyar Ubangiji,' kamar yadda annabi Ishaya ya fada.”
24 Og de vare udsendte fra Farisæerne,
Su wadanda aka aika daga wurin Farisawa suke. Sai suka tambaye shi cewa,
25 og de spurgte ham og sagde til ham: „Hvorfor døber du da, dersom du ikke er Kristus, ej heller Elias, ej heller Profeten?‟
“To don me kake baftisma idan kai ba Almasihu bane, ko Iliya, ko annabin?”.
26 Johannes svarede dem og sagde: „Jeg døber med Vand; midt iblandt eder staar den, I ikke kende,
Yahaya ya amsa masu, cewa, “Ina baftisma ne da ruwa. Amma a cikinku akwai wani tsaye wanda ba ku sani ba,
27 han, som kommer efter mig, hvis Skotvinge jeg ikke er værdig at løse.‟
shi wanda ke zuwa bayana, wanda ko igiyar takalminsa ban isa in kwance ba.”
28 Dette skete i Bethania hinsides Jordan, hvor Johannes døbte.
Wadannan abubuwa sun faru ne a Baitanya, a dayan ketaren Urdun, a wurin da Yahaya ke Baftisma.
29 Den næste Dag ser han Jesus komme til sig, og han siger: „Se det Guds Lam, som bærer Verdens Synd!
Washegari, Yahaya ya ga Yesu yana zuwa wurinsa ya ce, “Duba, ga Dan Ragon Allah wanda ke dauke zunubin duniya!
30 Han er den, om hvem jeg sagde: Efter mig kommer en Mand, som er kommen foran mig; thi han var før mig.
Wannan shine wanda na fada maku cewa, “Shi wanda ke zuwa bayana ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'
31 Og jeg kendte ham ikke; men for at han skulde aabenbares for Israel, derfor er jeg kommen og døber med Vand.‟
Ban san shi ba, amma saboda a bayyana shi ga Isra'ila ne nazo ina baftisma da ruwa. “
32 Og Johannes vidnede og sagde: „Jeg har set Aanden dale ned som en Due fra Himmelen, og den blev over ham.
Yahaya ya shaida, cewa, “Na ga Ruhu yana saukowa kamar kurciya daga sama, ya kuma zauna a kansa.
33 Og jeg kendte ham ikke; men den, som sendte mig for at døbe med Vand, han sagde til mig: Den, som du ser Aanden dale ned over og blive over, han er den, som døber med den Helligaand.
Ban gane shi ba, amma shi wanda ya aiko ni in yi baftisma cikin ruwa ya fada mani cewa, 'duk wanda ka ga Ruhun ya sauka kuma ya zauna a kansa, shine wanda ke yin baftisma cikin Ruhu mai tsarki.'
34 Og jeg har set det og har vidnet, at denne er Guds Søn.‟
Na gani, na kuma shaida cewa wannan shine Dan Allah.”
35 Den næste Dag stod Johannes der atter og to af hans Disciple.
Kuma, washegari, da Yahaya na tsaye da biyu daga cikin almajiransa,
36 Og idet han saa paa Jesus, som gik der, siger han: „Se det Guds Lam!‟
suka ga Yesu na wucewa, sai Yahaya ya ce, “Duba, ga Dan rago na Allah!”
37 Og de to Disciple hørte ham tale, og de fulgte Jesus.
Sai almajiransa biyu suka ji ya fadi haka, suka kuwa bi Yesu.
38 Men Jesus vendte sig om, og da han saa dem følge sig, siger han til dem:
Da Yesu ya waiwaya ya gan su suna bin sa, sai ya ce masu, “Me kuke so?” Suka amsa, “Rabbi (wato 'Mallam'), ina kake da zama?”
39 „Hvad søge I efter?‟ Men de sagde til ham: „Rabbi! (hvilket udlagt betyder Mester) hvor opholder du dig?‟
Yace masu, “Zo ku gani.” Sai suka zo suka ga inda yake zama; suka zauna da shi ranan nan, gama wajen sa'a ta goma ne.
40 Han siger til dem: „Kommer og ser!‟ De kom da og saa, hvor han opholdt sig, og de bleve hos ham den Dag; det var ved den tiende Time.
Daya daga cikin wadanda suka ji maganar Yahaya suka kuma bi Yesu shine Andarawus, dan'uwan Siman Bitrus.
41 Den ene af de to, som havde hørt Johannes's Ord og havde fulgt ham, var Andreas, Simon Peters Broder.
Ya fara neman dan'uwansa Siman yace masa, “Mun sami Almasihu” (wanda ake kira 'Kristi').
42 Denne finder først sin egen Broder Simon og siger til ham: „Vi have fundet Messias‟ (hvilket er udlagt: Kristus).
Ya kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi yace, “Kai ne Siman dan Yahaya. Za a kira ka Kefas,” (ma'ana, 'Bitrus').
43 Og han førte ham til Jesus. Jesus saa paa ham og sagde: „Du er Simon, Johannes's Søn; du skal hedde Kefas‟ (det er udlagt: Petrus).
Washegari, da Yesu yana shirin tafiya zuwa Galili, sai ya sami Filibus, ya ce masa, “ka biyo ni.”
44 Den næste Dag vilde han drage derfra til Galilæa; og han finder Filip. Og Jesus siger til ham: „Følg mig!‟
Filibus dan asalin Baitsaida ne, garin Andarawus da Bitrus.
45 Men Filip var fra Bethsajda, fra Andreas's og Peters By.
Filibus ya sami Natana'ilu yace masa, “Mun same shi, shi wanda Musa ya rubuta shi a cikin attaura, da annabawa: Yesu Dan Yusufu, Ba-Nazarat.”
46 Filip finder Nathanael og siger til ham: „Vi have fundet ham, hvem Moses i Loven og ligesaa Profeterne have skrevet om, Jesus, Josefs Søn, fra Nazareth.‟
Natana'ilu ya ce masa, “za a iya samun wani abu nagari a Nazarat?” Filibus yace masa, “Zo ka gani.”
47 Og Nathanael sagde til ham: „Kan noget godt være fra Nazareth?‟ Filip siger til ham: „Kom og se!‟
Yesu ya ga Natana'ilu yana zuwa wurinsa sai yayi magana game da shi, “Duba, Ba-Isra'ile na hakika wanda babu yaudara a cikinsa.”
48 Jesus saa Nathanael komme til sig, og han siger om ham: „Se, det er sandelig en Israelit, i hvem der ikke er Svig.‟
Natana'ilu yace masa, “Ta yaya ka san ni?” Sai Yesu ya amsa masa yace, “Tun kafin Filibus ya kira ka, sa'adda kake a gindin baure, na gan ka.”
49 Nathanael siger til ham: „Hvorfra kender du mig?‟ Jesus svarede og sagde til ham: „Førend Filip kaldte dig, saa jeg dig, medens du var under Figentræet.‟
Natana'ilu ya amsa, “Rabbi, Kai Dan Allah ne! Kai Sarkin Isra'ila ne!”
50 Nathanael svarede ham: „Rabbi! du er Guds Søn, du er Israels Konge.‟
Yesu ya amsa masa yace, “Don na ce maka, 'Na gan ka a gindin Baure', ka gaskanta? Za ka ga abubuwa da suka fi wannan girma.”
51 Jesus svarede og sagde til ham: „Tror du, fordi jeg sagde dig, at jeg saa dig under Figentræet? Du skal se større Ting end disse.‟ Og han siger til ham: „Sandelig, sandelig, siger jeg eder, I skulle fra nu af se Himmelen aabnet og Guds Engle stige op og stige ned over Menneskesønnen.‟
Sai yace, 'Hakika, hakika ina gaya maka, zaka ga sammai a bude, mala'ikun Allah kuma suna hawa suna sauka akan Dan Mutum.”

< Johannes 1 >