< Job 38 >
1 Derefter svarede Herren Job ud af Stormen og sagde:
Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba. Ya ce,
2 Hvo er den, som formørker Guds Raad med Tale uden Forstand.
“Wane ne wannan da yake ɓata mini shawarata da surutan wofi?
3 Bind op om dine Lænder som en Mand, saa vil jeg spørge dig, og undervis du mig!
Ka sha ɗamara kamar namiji; zan yi maka tambaya, za ka kuwa amsa mini.
4 Hvor var du, der jeg grundfæstede Jorden? forkynd det, hvis du har Indsigt?
“Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya? Gaya mini, in ka sani.
5 Hvo har sat dens Maal? du ved det vel? eller hvo udstrakte Snoren over den?
Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani! Wane ne ya ja layin aunawa a kanta?
6 Hvorpaa ere dens Piller nedsænkede? eller hvo har lagt dens Hjørnesten?
A kan me aka kafa tushenta, ko kuma wa ya sa dutsen kan kusurwarta,
7 der Morgenstjerner sang til Hobe, og alle Guds Børn raabte af Glæde.
yayinda taurarin safe suke waƙa tare dukan mala’iku kuma suka yi sowa don farin ciki.
8 Og hvo lukkede for Havet med Døre, der det brød frem, gik ud af Moders Liv,
“Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi, lokacin da ya burtsatso daga cikin ciki.
9 der jeg gjorde Sky til dets Klædning og Mørke til dets Svøb,
Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
10 der jeg afstak for det min Grænse og satte Stang og Døre for det
sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
11 og sagde: Hertil skal du komme og ikke længere; og her skal være sat Grænse for dine stolte Bølger?
Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai, ga inda raƙuman ruwanka za su tsaya?
12 Har du i dine Dage givet Befaling til Morgenen? har du vist Morgenrøden dens Sted,
“Ko ka taɓa ba safiya umarni ko kuma ka sa asuba ta fito,
13 til at gribe Jorden ved dens Flige, saa at de ugudelige rystes bort fra den?
don ta kama gefen duniya ta kakkaɓe mugaye daga cikinta?
14 saa denne forvandler sig som Leret, hvori Seglet trykkes, og Tingene fremstille sig som i deres Klædebon,
Ƙasa ta sāke siffa kamar laka da aka yi wa hatimi; ta fito a fili kamar riga.
15 og de ugudelige unddrages deres Lys, og den opløftede Arm sønderbrydes?
An hana mugaye haskensu, hannun da suka ɗaga an karya shi.
16 Er du kommen til Havets Kilder? og har du vandret paa Dybets Bund?
“Ko ka taɓa tafiya zuwa maɓulɓulan teku, ko kuma ka taɓa zuwa cikin zurfin lungun teku?
17 Have Dødens Porte opladt sig for dig? eller saa du Dødens Skygges Porte?
Ko an taɓa nuna maka ƙofar mutuwa? Ko ka taɓa ganin ƙofar inuwar duhun mutuwa?
18 Har du overskuet Jordens Bredde? forkynd det, dersom du kender det alt sammen!
Ko ka gane fāɗin duniya? Gaya mini, in ka san wannan duka.
19 Hvor er Vejen did, hvor Lyset mon bo, og hvor er Mørkets Sted,
“Ina ne hanyar zuwa gidan haske? Kuma a ina duhu yake zama?
20 at du kunde bringe det til dets Landemærke, og at du kendte Stierne til dets Hus?
Ko za ka iya kai su wurarensu? Ka san hanyar zuwa wurin da suke zama?
21 Du ved det; thi den Gang blev du jo født, og dine Dages Tal er stort!
Ba shakka ka sani, gama an riga an haife ka a lokacin! Ka yi shekaru da yawa kana rayuwa.
22 Er du kommen til Forraadskamrene for Sneen, eller saa du Forraadskamrene for Hagelen,
“Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara ko ka taɓa ganin rumbunan ƙanƙara
23 hvilke jeg har sparet til Trængsels Tid, til Strids og Krigs Dag.
waɗanda nake ajiya domin lokacin wahala, domin kwanakin yaƙi da faɗa?
24 Hvor er den Vej, hvor Lyset deler sig, hvor Østenvejret spreder sig over Jorden?
Ina ne hanyar zuwa wurin da ake samun walƙiya, ko kuma inda daga nan ne ake watsa iskar gabas zuwa ko’ina cikin duniya?
25 Hvo brød Render til Vandskyl og Vej til Lynet, som gaar foran Torden,
Wane ne ya yanka hanyar wucewar ruwa, da kuma hanyar walƙiyar tsawa
26 for at lade regne paa det Land, hvor ingen er, i Ørken, hvor intet Menneske er,
don ba da ruwa a ƙasar da ba kowa a wurin jeji inda ba mai zama ciki
27 for at mætte de øde og ødelagte Steder og bringe Græsbunden til at spire?
don a ƙosar da wurin da ya bushe a sa ciyawa ta tsiro a can?
28 Har Regnen vel en Fader? eller hvo har avlet Duggens Draaber?
Ruwan sama yana da mahaifi? Wa ya zama mahaifin raɓa?
29 Af hvis Moderliv er Frost udgangen? og hvo fødte Rimfrost under Himmelen?
Daga cikin wane ne aka haifi ƙanƙara? Wane ne ya haifi jaura daga sammai
30 Vandet skjuler sig, som var det en Sten, og Dybets Overflade slutter sig sammen.
lokacin da ruwa ya zama da ƙarfi kamar dutse, lokacin da saman ruwa ya daskare?
31 Kan du knytte Syvstjernens Baand, eller løse Orions Reb?
“Za ka iya daure kyakkyawar kaza da’ya’yanta? Ko za ka iya kunce igiyoyin mafarauci da kare da zomo?
32 Kan du lade Dyrekredsens Stjerner komme frem til deres Tid? eller føre Bjørnen med dens Unger frem?
Za ka iya tattara taurari bisa ga lokacinsu ko kuma ka bi da beyar da’ya’yanta zuwa waje?
33 Kender du Himmelens Love? eller kan du bestemme dens Herredømme over Jorden?
Ka san dokokin sammai? Ko za ka iya faɗar dangantakar Allah da duniya?
34 Kan du opløfte din Røst til Skyen, at Vands Mangfoldighed maa skjule dig?
“Za ka iya tsawata wa gizagizai ka kuma rufe kanka da ambaliyar ruwa?
35 Kan du udlade Lynene, at de fare frem, og at de sige til dig: Se, her ere vi?
Kai ne kake aika walƙiya da tsawa zuwa inda suke zuwa? Ko suna zuwa wurinka su ce, ‘Ga mu nan mun zo?’
36 Hvo lagde Visdom i Hjertets Inderste? eller hvo gav Forstand i Tanken?
Wane ne yake cika zuciya da hikima ko kuma yake ba zuciya ganewa?
37 Hvo kan tælle Skyerne med Visdom? og hvo kan udgyde Himmelens Vandbeholdere,
Wane ne yake da hikimar iya ƙirga gizagizai? Wane ne zai iya karkato bakunan tulunan sammai
38 idet Støv løber sammen til en Støbning, og Jordklumperne hænge ved hverandre?
sa’ad da ƙura ta yi yawa ta daskare a wuri ɗaya?
39 Kan du jage Rov til Løvinden og fylde de unge Løvers Graadighed,
“Za ka iya farauto wa zakanya nama, ka kuma kawar wa zakoki yunwarsu.
40 naar de lægge sig ned i deres Boliger og blive i Skjul for at lure?
Lokacin da suka kwanta cikin kogunansu, ko kuma lokacin da suke a wurin ɓuyansu?
41 Hvo skaffer Ravnen dens Føde, naar dens Unger skrige til Gud, naar de fare hid og did, fordi de intet have at æde?
Wane ne yake ba hankaka abinci lokacin da’ya’yansa suke kuka ga Allah, kuma suna yawo don rashin abinci?