< Job 34 >

1 Fremdeles svarede Elihu og sagde:
Sa’an nan Elihu ya ce,
2 Hører, I vise! min Tale, og I forstandige! vender eders Øren til mig;
“Ku ji maganata, ku masu hikima; ku saurare ni, ku masu ilimi.
3 thi Øret prøver Talen, og Ganen smager Maden.
Gama kunne yana rarrabe magana kamar yadda harshe yake ɗanɗana abinci.
4 Lader os vælge os det rette, lader os kende imellem os, hvad godt er.
Bari mu zaɓi abin da yake daidai, bari mu koyi abin da yake mai kyau tare.
5 Thi Job sagde: Jeg er retfærdig, men Gud har borttaget min Ret.
“Ayuba ya ce, ‘Ba ni da laifi, amma Allah ya hana mini hakkina.
6 Uagtet jeg har Ret, skal jeg staa som en Løgner; ulægelig har Pilen truffet mig, skønt der ikke er Overtrædelse hos mig.
Ko da yake ina da gaskiya, an ɗauke ni maƙaryaci; ko da yake ba ni da laifi, kibiyoyinsa sun ji mini ciwo wanda ba ya warkewa.’
7 Hvor er en Mand som Job, der inddrikker Gudsbespottelse som Vand
Wane mutum ne kamar Ayuba, wanda yake shan ba’a kamar ruwa?
8 og vandrer i Selskab med dem, som gøre Uret, og gaar med ugudelige Folk?
Yana abokantaka da masu aikata mugunta; yana cuɗanya da mugaye.
9 Thi han sagde: Det gavner ikke en Mand, om han har Behag i Gud.
Gama ya ce, ‘Ba ribar da mutum zai samu lokacin da yake ƙoƙari yă faranta wa Allah zuciya.’
10 Derfor, I Mænd af Forstand! hører paa mig: Det være langt fra Gud at være ugudelig, og fra den Almægtige at være uretfærdig.
“Saboda haka ku saurare ni, ku masu ganewa. Ko kaɗan Allah ba ya mugunta, Maɗaukaki ba ya kuskure.
11 Thi han betaler et Menneske efter dets Gerning og lader enhver faa efter hans Vej.
Yana biyan mutum bisa ga abin da ya yi; yana kawo masa abin da ayyukansa suka jawo.
12 Ja, sandelig, Gud handler ikke uretfærdigt, og den Almægtige forvender ikke Retten.
Ba zai yiwu Allah yă yi ba daidai ba, Maɗaukaki ba zai yi shari’a marar gaskiya ba.
13 Hvo har beskikket ham over Jorden? og hvo har grundet hele Jordens Kreds.
Wane ne ya ba shi iko yă lura da duniya? Wane ne ya ba shi iko kan dukan duniya?
14 Dersom han vilde agte paa sig selv alene, samlede han sin Aand og sin Aande til sig:
In nufinsa ne ya kuma janye ruhunsa da numfashinsa,
15 Da maatte alt Kød til Hobe opgive Aanden, og Mennesket blive til Støv igen.
’yan adam duka za su hallaka tare, mutum kuma zai koma ƙasa.
16 Dersom du har Forstand, saa hør dette, vend dine Øren til min Tales Røst!
“In kana da ganewa sai ka saurari wannan; ka saurari abin da zan ce.
17 Skulde vel den, som hader Ret, holde Styr? eller tør du sige den mægtige retfærdige at være uretfærdig?
Maƙiyin gaskiya zai iya yin mulki? Za ka iya ba mai gaskiya, Maɗaukaki laifi?
18 Tør nogen sige til en Konge: Du Belial! til de ædle: Du ugudelige!
Ba shi ne ya ce wa sarakuna, ‘Ba ku da amfani ba,’ ya ce wa manya ‘Ku mugaye ne,’
19 Han anser ikke Fyrsternes Personer og agter ikke den rige fremfor den ringe; thi de ere alle hans Hænders Gerning.
wanda ba ya nuna sonkai ga’ya’yan sarki kuma ba ya goyon bayan masu arziki a kan matalauta, gama dukansu shi ya yi su da hannuwansa.
20 De dø i et Øjeblik, og det midt om Natten: Folk rystes og forgaa; og de mægtige tages bort, men ikke ved Menneskehaand.
Suna mutuwa nan take, a cikin tsakiyar dare; an girgiza mutanen amma sun wuce; an taɓa manya amma ba da hannun mutum ba.
21 Thi hans Øjne ere over hver Mands Veje, og han ser alle hans Skridt.
“Idanunsa suna kan al’amuran mutane; yana ganin tafiyarsu duka.
22 Der er intet Mørke og ingen Dødsskygge, hvori de som gøre Uret, kunne skjule sig.
Babu wuri mai duhu, babu inuwa mai duhu, inda masu aikata mugunta za su ɓoye.
23 Thi han behøver ikke at agte længe nogen, der skal stedes til Dom for Gud.
Allah ba ya bukata yă ci gaba da bincike mutane, har da za su zo gabansa don yă shari’anta su.
24 Han sønderslaar de mægtige uden at ransage, og han sætter andre i deres Sted.
Ba tare da tambaya ba yana ragargaza masu iko, yă kuma sa waɗansu a wurinsu.
25 Derfor kender han deres Gerninger og omkaster dem om Natten, at de blive knuste;
Gama yana sane da abubuwan da suke yi, yana hamɓarar da su da dare a kuma ragargaza su.
26 han slaar dem, hvor de ugudelige findes, paa det Sted, hvor Folk ser det.
Yana ba su horo, don muguntarsu, inda kowa zai gan su,
27 Thi derfor vege de fra ham og agtede ikke paa nogen af hans Veje,
domin sun juya daga binsa, kuma ba su kula da hanyoyinsa ba.
28 for at de kunde bringe den ringes Skrig ind for ham, og for at han maatte høre de elendiges Skrig.
Sun sa kukan matalauta ya kai wurinsa yadda ya kai ga jin kukan masu bukata.
29 Naar han skaffer Ro til Veje — hvo vil kalde ham uretfærdig? — og naar han skjuler sit Ansigt — hvo kan da beskue ham? — baade for et Folk og for et enkelt Menneske:
Amma in ya yi shiru, wa zai ba shi laifi? In ya ɓoye fuskarsa, wa zai gan shi? Duk da haka shi yake da iko kan mutum da al’umma duka,
30 Saa er det, for at en vanhellig ikke skal regere, og at der ikke skal være Snarer for Folket.
yana hana wanda bai san Allah ba yă yi mulki, ya hana shi sa wa mutane tarko.
31 Mon nogen har sagt til Gud: Jeg har faaet, hvad jeg ikke forskylder?
“A ce mutum ya ce wa Allah, ‘Na yi laifi, amma ba zan sāke saɓa wa wani ba.
32 Lær du mig ud over det, jeg kan se; dersom jeg har gjort Uret, da vil jeg ikke gøre det mere.
Ka koya mini abin da ba zan iya gani ba; in na yi ba daidai ba, ba zan sāke yi ba.’
33 Skal det være efter dit Skøn, at han skal gengælde? thi du har vraget, saa at du har at vælge, og ikke jeg? saa tal da, hvad du ved!
Ya kamata Allah yă yi maka bisa ga abin da ka ce ne, sa’ad da ka ƙi ka tuba? Dole kai ka zaɓa, ba ni ba; yanzu ka gaya mini abin da ka sani.
34 Folk af Forstand skulle sige til mig, og ligeledes den vise Mand, som hører mig:
“Mutane masu ganewa za su ce, masu hikima waɗanda suka ji ni za su ce mini,
35 „Job taler ikke med Forstand, og hans Ord ere ikke mere Klogskab”.
‘Ayuba ya yi magana cikin rashin sani; maganganunsa na marar hikima ne.’
36 O gid, at Job maatte prøves til fulde, fordi han har svaret som uretfærdige Mænd!
Kash, da za a gwada Ayuba har ƙarshe, domin yana ba da amsa kamar mugun mutum.
37 thi han lægger Overtrædelse til sin Synd, imellem os klapper han i Hænderne og gør mange Ord imod Gud.
Ya ƙara tawaye a kan zunubansa; ya tafa hannuwansa na reni a cikinmu ya kuma ƙara yawan maganganunsa ga Allah.”

< Job 34 >