< Job 32 >
1 Da lode disse tre Mænd af at svare Job, efterdi han var retfærdig i sine egne Øjne.
Sai mutanen nan uku suka daina amsa wa Ayuba, domin a ganinsa shi mai adalci ne.
2 Men Vreden optændtes hos Elihu, Busiten, Barakels Søn, af Rams Slægt, hans Vrede optændtes imod Job, fordi han vilde holde sin Sjæl retfærdig over for Gud.
Amma Elihu ɗan Barakel mutumin Buz na iyalin Ram, ya ji haushi da Ayuba don yă nuna shi ne mai gaskiya ba Allah ba.
3 Hans Vrede optændtes ogsaa imod hans tre Venner, fordi de ikke fandt paa noget Svar og alligevel holdt Job for ugudelig.
Ya kuma ji haushin abokan nan guda uku, don sun kāsa amsa wa Ayuba ko da yake sun nuna Ayuba ne yake da laifi.
4 Men Elihu havde biet efter, at Job skulde ende sine Ord; thi hine vare ældre af Aar end han.
Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka.
5 Der Elihu saa, at der var intet Svar i de tre Mænds Mund, da optændtes hans Vrede.
Amma sa’ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da abin cewa, sai ya fusata.
6 Saa svarede Elihu, Busiten, Barakels Søn, og sagde: Jeg er ung af Aar, men I ere bedagede Mænd; derfor undsaa jeg mig og frygtede for at kundgøre eder min Kundskab.
Sai Elihu ɗan Barakel mutumin Buz ya ce, “Ni ƙarami ne a shekaru, ku kuma kun girme ni; shi ya sa na ji tsoro na kāsa gaya muku abin da na sani.
7 Jeg sagde: Lad Dagene tale, og Aars Mangfoldighed kundgøre Visdom!
Na ɗauka ya kamata ‘shekaru su yi magana; ya kamata yawan shekaru su koyar da hikima.’
8 Sandelig, det er Aanden i Mennesket og den Almægtiges Aande, som gør ham forstandig.
Amma ruhun da yake cikin mutum, numfashin Maɗaukaki shi ne yake ba shi ganewa.
9 De alderstegne ere ikke altid vise, ej heller forstaa de gamle altid Retten.
Ba tsofaffi ne kaɗai suke da hikima ba, ba masu yawan shekaru ne suke gane abin da yake daidai ba.
10 Derfor siger jeg: Hør paa mig; ogsaa jeg vil kundgøre min Kundskab.
“Saboda haka nake ce muku, ku saurare ni; ni ma zan gaya muku abin da na sani.
11 Se, jeg biede efter eders Ord, jeg vendte mine Øren til eders forstandige Tale, indtil I kunde faa udgrundet, hvad I vilde tale.
Na jira sa’ad da kuke magana, na ji muhawwararku lokacin da kuke neman abin da za ku faɗa,
12 Og jeg har agtet nøje paa eder, men se, der var ingen af eder, som gendrev Job, og som kunde svare paa hans Tale,
na saurare ku da kyau. Amma ba waninku da ya nuna Ayuba yana da laifi; ba ko ɗayanku da ya amsa muhawwararsa.
13 at I ikke skulde sige: Vi have fundet Visdom; Gud, men ikke et Menneske, kan fælde ham.
Kada ku ce, ‘Mun sami hikima; Allah ne kaɗai yake da ikon yin nasara da shi ba mutum ba.’
14 Men imod mig har han ikke stillet sin Tale, og med eders Ord vil jeg ikke give ham Svar.
Amma ba da ni Ayuba ya yi gardama ba kuma ba zan amsa masa da irin amsarku ba.
15 De ere blevne forskrækkede, de kunne ikke svare mere, borte ere Ordene for dem.
“Mamaki ya kama su kuma ba su da abin cewa; kalmomi sun kāsa musu.
16 Og jeg biede, thi de talte ikke; ja, de stode der, de svarede ikke mere.
Dole ne in jira yanzu da suka yi shiru, yanzu da suke tsaye a wurin ba su da amsa.
17 Nu vil jeg ogsaa svare for min Del, ogsaa jeg vil kundgøre min Kundskab.
Ni ma zan faɗi nawa; ni ma zan faɗi abin da na sani.
18 Thi jeg er fuld af Taler; Aanden i mit Indre trænger paa.
Gama ina cike da magana, kuma ruhun da yake cikina yana iza ni;
19 Se, mit Indre er som Vin, for hvilken der ikke er aabnet, det maa sprænges som nye Læderflasker.
a ciki ina kamar ruwan inabi wanda aka rufe a cikin kwalaba, kamar sabuwar salkar ruwan inabi mai shirin fashewa.
20 Jeg maa tale, at jeg kan faa Luft, jeg maa oplade mine Læber og svare.
Dole in yi magana in sami lafiya; dole in buɗe baki in ba da amsa.
21 Ikke vil jeg anse nogens Person, og jeg vil ikke smigre for noget Menneske;
Ba zan nuna wa wani sonkai ba, ko kuma in yi wa wani daɗin baki ba;
22 thi jeg forstaar ikke at smigre; lettelig vilde min Skaber rive mig bort.
gama da a ce na iya daɗin baki, da wanda ya yi ni ya ɗauke ni daga nan tuntuni.