< Job 31 >
1 Jeg gjorde en Pagt med mine Øjne, og hvad skulde jeg agte paa en Jomfru?
“Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
2 Og hvad for en Lod vilde Gud have givet ovenfra og hvad for en Arv den Almægtige fra det høje?
Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
3 Mon ikke Ulykke er beredt for den uretfærdige og Undergang for dem, som gøre Uret?
Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
4 Mon han ikke ser mine Veje og tæller alle mine Skridt?
Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
5 Dersom jeg har vandret med Falskhed, og min Fod har hastet til Svig,
“In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
6 — han veje mig paa Retfærdigheds Vægtskaaler, og Gud kende min Uskyldighed —
Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
7 dersom min Gang har bøjet af fra Vejen, og mit Hjerte er gaaet efter mine Øjne, og en Plet har klæbet ved mine Hænder:
In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
8 Da gid jeg maa saa, men en anden æde, og mit Afkom maa oprykkes med Rod.
bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
9 Dersom mit Hjerte er forlokket til en Kvinde, og jeg har luret ved min Næstes Dør:
“In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
10 Da gid min Hustru maa male for en anden, og andre bøje sig over hende.
sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
11 Thi det var en Skændselsgerning, og det var en Misgerning, som hørte hen for Dommerne;
Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
12 thi det var en Ild, som fortærede indtil Afgrunden, og som skulde have oprykket al min Afgrøde med Rode.
Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
13 Dersom jeg havde foragtet min Tjeners eller min Tjenestepiges Ret, naar de trættede med mig;
“In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
14 — og hvad vilde jeg gøre, naar Gud vilde opstaa? og naar han vilde hjemsøge, hvad skulde jeg svare ham?
me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
15 har ikke han, som skabte mig i Moders Liv, skabt ham? og har ikke en og den samme beredt os i Moderskød? —
Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
16 dersom jeg har nægtet de ringe deres Begæring og ladet Enkens Øjne vansmægte,
“In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
17 og jeg har ædt min Mundbid for mig alene, saa at den faderløse ikke aad deraf;
in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
18 — tværtimod, han er opvokset hos mig som hos en Fader fra min Ungdom af, og hende ledede jeg, fra min Moders Liv af —
amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
19 dersom jeg har set en forkommen, uden Klæder, og at den fattige intet Dække havde;
In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
20 dersom hans Lænder ikke have velsignet mig, medens han varmede sig ved Ulden af mine Faar;
kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
21 dersom jeg har løftet min Haand imod den faderløse, fordi jeg saa Hjælp for mig i Porten:
in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
22 Da gid min Skulder maa falde fra Skulderbladet, og min Arm brydes fra Armpiben!
bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
23 Thi en Rædsel vilde være kommen over mig, en Ulykke fra Gud, og imod hans Højhed formaaede jeg intet.
Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
24 Dersom jeg har sat Guld til mit Haab eller sagt til det kostelige Guld: Du er min Tillid;
“In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
25 dersom jeg har glædet mig, at mit Gods var meget, og at min Haand havde forhvervet mangfoldigt;
in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
26 dersom jeg har set til Sollyset, naar det skinnede, eller til Maanen, naar den gaar herlig,
In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
27 og mit Hjerte har ladet sig forlokke i Løndom, saa at min Mund kyssede min Haand:
zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
28 — Ogsaa dette havde været en Misgerning, som hørte hen under Dommerne; thi jeg havde hyklet for Gud i det høje —!
Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
29 dersom jeg har glædet mig over min Fjendes Undergang og jublet, naar Ulykken ramte ham;
“In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
30 — men jeg tilstedede ikke min Gane at synde, saa at jeg under Forbandelse begærede hans Sjæl —
ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
31 dersom ikke Mændene i mit Telt have sagt: Hvor finder man nogen, som ikke er bleven mæt af hans Kød?
in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
32 — den fremmede maatte ikke ligge udenfor om Natten, jeg lod mine Døre op for vejfarende —
Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
33 dersom jeg har skjult mine Overtrædelser som Adam og dulgt min Misgerning i min Barm,
in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
34 fordi jeg frygtede den store Hob, og Slægters Foragt kunde have forfærdet mig, saa at jeg tav og ikke gik ud af en Dør —
domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
35 Havde jeg dog den, som vilde høre paa mig! se her min Underskrift — den Almægtige svare mig — og her den Klage, min Modpart har opsat;
(“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
36 sandelig, jeg skulde tage den paa min Skulder, jeg skulde binde den omkring mig som et Hovedsmykke!
Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
37 Jeg vil tilkendegive ham ethvert af mine Skridt, som en Fyrste vil jeg nærme mig ham.
Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
38 Dersom min Ager raaber imod mig, og alle dens Furer græde;
“In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
39 dersom jeg har fortæret dens Grøde uden at have betalt den og udblæst Sjælen fra dens Ejermand:
in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
40 Gid da vokse Tjørn i Stedet for Hvede, og Ukrudt i Stedet for Byg; — Jobs Ord have Ende.
bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.