< Job 29 >
1 Og Job blev ved at fremføre sit Billedsprog og sagde:
Ayuba ya ci gaba da jawabinsa,
2 Gid jeg var som i de forrige Maaneder, som i de Dage, da Gud bevarede mig,
“Da ma ina nan lokacin da ya wuce baya can, kwanakin da Allah yake lura da ni,
3 da hans Lampe lyste over mit Hoved, da jeg gik igennem Mørket ved hans Lys;
lokacin da fitilarsa take haske a kaina na yi tafiya cikin duhu tare da haskensa.
4 som det var med mig i min Høsts Dage, der Guds Fortrolighed var over mit Telt;
Kwanakin da nake tasowa, lokacin da abokantakar Allah ta sa wa gidana albarka,
5 da den Almægtige endnu var med mig, da mine Drenge vare omkring mig;
lokacin da Maɗaukaki yana tare da ni, kuma’ya’yana suna kewaye da ni,
6 da mine Trin badede sig i Mælk, og Klippen hos mig udgød Oliebække;
lokacin da ake zuba madara a inda nake takawa, duwatsu kuma suna ɓulɓulo mini man zaitun.
7 da jeg gik ud til Porten op til Staden, da jeg lod berede mit Sæde paa Torvet.
“Sa’ad da na je ƙofar birni na zauna a bainin jama’a,
8 De unge saa mig og trak sig tilbage, og de gamle stode op og bleve staaende.
matasan da suka gan ni sukan ja gefe tsofaffi kuma suka tashi tsaye;
9 De Øverste holdt op at tale, og de lagde Haanden paa deres Mund.
sarakuna suka yi shiru suka rufe bakunansu da hannuwansu;
10 Fyrsternes Røst forstummede, og deres Tunge hang ved deres Gane.
Muryar manya ta yi tsit harshensu ya manne a rufin bakunansu.
11 Thi det Øre, som hørte, priste mig salig, og det Øje, som saa mig, gav mig Vidnesbyrd.
Duk wanda ya ji ni ya yaba mini waɗanda suka gan ni kuma sun amince da ni,
12 Thi jeg reddede den fattige, som skreg, og den faderløse, som ingen Hjælper havde.
domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
13 Dens Velsignelse, som ellers maatte omkommet, kom over mig, og jeg frydede Enkens Hjerte.
Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
14 Jeg iførte mig Retfærdighed, og den klædte sig i mig; min Dom var mig som en Kappe og et Hovedsmykke.
Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
15 Jeg var den blindes Øje, og jeg var den lammes Fod.
Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
16 Jeg var de fattiges Fader, og den mig ubekendtes Retssag undersøgte jeg.
Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
17 Og jeg sønderbrød den uretfærdiges Kindtænder, og jeg gjorde, at han maatte slippe Rovet af sine Tænder.
Na karya ƙarfin mugaye na ƙwato waɗanda suke riƙe da haƙoransu.
18 Og jeg sagde: I min Rede vil jeg opgive Aanden og have Dage mangfoldige som Sand.
“Na yi tunani cewa, ‘Zan mutu a cikin gidana, kwanakina da yawa kamar turɓayar ƙasa.
19 Min Rod skal aabne sig for Vandet, og Duggen skal blive om Natten paa mine Grene.
Jijiyoyina za su kai cikin ruwa, kuma raɓa za tă kwanta a rassana dukan dare.
20 Min Herlighed skal blive ny hos mig, og min Bue skal forynges i min Haand.
Ɗaukakata za tă kasance tare da ni garau, bakana koyaushe sabo ne a hannuna.’
21 De hørte paa mig og ventede, og de tav til mit Raad.
“Mutane suna mai da hankali su saurare ni, suna yin shiru don su ji shawarata.
22 Havde jeg talt, toge de ikke igen til Orde, og min Tale faldt som Draaber over dem;
Bayan da na yi magana, ba su ƙara ce kome ba. Maganata ta shige su.
23 de ventede paa mig som paa en Regn, og de aabnede Munden vidt som efter den sildige Regn.
Sukan jira ni kamar yadda ake jiran ruwan sama. Sukan sha daga cikin maganganuna kamar mai shan ruwan bazara.
24 Jeg smilte til dem, der vare mistrøstige; og de bragte ikke mit Ansigts Lys til at svinde.
Sa’ad da na yi musu murmushi da ƙyar sukan yarda; hasken fuskata yana da daraja a gare su.
25 Jeg udvalgte deres Vej og sad øverst, og jeg boede som en Konge iblandt Hærskaren, som den, der trøster de sørgende.
Na zaɓar masu inda za su bi na kuma zauna kamar sarkinsu; na zauna kamar sarki a cikin rundunansu; ina nan kamar mai yi wa masu makoki ta’aziyya.