< Job 21 >

1 Men Job svarede og sagde:
Sai Ayuba ya amsa,
2 hører, ja hører min Tale, og lader dette være den Trøst, I yde!
“Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
3 Fordrager mig, og jeg vil tale, og naar jeg har talt, da kan du spotte!
Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
4 Mon min Klage gælder Mennesker? og om saa er, hvorfor skulde ikke min Aand blive utaalmodig?
“A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
5 Vender eder til mig, og gruer og lægger Haanden paa Munden!
Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
6 Thi kommer jeg det i Hu, da forfærdes jeg, og Bævelse betager mit Kød.
Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
7 Hvorfor blive de ugudelige i Live, blive gamle, ja vældige i Kraft?
Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
8 Deres Sæd staar fast for deres Ansigt om dem og deres Afkom for deres Øjne.
Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
9 Deres Huse have Fred, uden Frygt, og Guds Ris er ikke over dem.
Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
10 Deres Tyr springer og ej forgæves; deres Ko kalver og er ikke ufrugtbar.
Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
11 De lade deres Børn løbe som en Faarehjord, og deres Drenge springe.
Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
12 De opløfte deres Røst til Tromme og Harpe og glæde sig ved Fløjtens Lyd.
Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
13 De slide deres Dage hen i Lykke, og i et Øjeblik synke de ned i de dødes Rige. (Sheol h7585)
Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
14 Og dog sagde de til Gud: Vig fra os! thi vi have ikke Lyst til Kundskab om dine Veje.
Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
15 Hvad er den Almægtige, at vi skulde tjene ham? eller hvad Gavn skulde vi have af at bønfalde ham?
Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
16 Se, deres Lykke hviler dog ikke i deres egen Haand! De ugudeliges Raad er langt fra mig.
Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
17 Hvor tit udslukkes vel de ugudeliges Lampe og kommer deres Ulykke over dem? hvor tit uddeler Gud Smerter til dem i sin Vrede?
“Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
18 Blive de som Straa for Vejr og som Avner, hvilke Hvirvelvind bortstjæler?
Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
19 „Gud gemmer hans Uret til hans Børn.” Han skulde betale ham selv, at han fornemmer det.
An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
20 Hans egne Øjne skulle se hans Fordærvelse, og han skulde drikke af den Almægtiges Vrede.
Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
21 Thi hvad bekymrer han sig om sit Hus efter sig, naar hans Maaneders Tal er ude?
Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
22 Mon nogen vil lære Gud Kundskab, ham, som dømmer de høje?
“Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
23 Den ene dør i sin fulde Styrke, ganske rolig og tryg;
Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
24 hans Kar vare fulde af Mælk, og Marven i hans Ben var vædskefuld.
jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
25 Men den anden maa dø med en beskelig bedrøvet Sjæl og har ikke nydt noget godt.
Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
26 De skulle ligge med hinanden i Støvet, og Ormene skulle bedække dem.
Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
27 Se, jeg kender eders Tanker, ja eders Rænker, med hvilke I gøre Vold imod mig;
“Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
28 thi I sige: Hvor er Voldsmandens Hus? og hvor er Teltet, hvor de ugudelige boede?
Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
29 Have I ikke adspurgt de vejfarende, og erkende I ikke deres Vidnesbyrd,
Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
30 at den onde skulde spares til Ulykkens Dag, skulde føres frem til Vredens Dag?
cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
31 „Hvo vil forholde ham hans Vej? naar han gør noget, hvo vil betale ham?
Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
32 Og han føres hen til Gravene, og ved Gravhøjen lever hans Minde.
Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
33 I Dalens Muld hviler han sødt, og han drager hvert Menneske efter sig, og paa dem foran ham er ikke Tal.”
Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
34 Hvorledes trøste I mig da med Forfængelighed? og hvad der bliver tilbage af eders Svar, er Troløshed.
“Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”

< Job 21 >