< Job 18 >
1 Da svarede Bildad, Sukiten, og sagde:
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 Naar ville I gøre Ende paa Ord? forstaar først, og derefter ville vi tale.
“Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
3 Hvorfor blive vi agtede som Fæ og ere blevne urene for eders Øjne?
Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
4 O du, som sønderslider din Sjæl i din Vrede, mon Jorden skal ligge forladt for din Skyld og en Klippe flyttes fra sit Sted?
Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
5 Ja den ugudeliges Lys skal udslukkes, og hans Ilds Lue skal ikke skinne.
“An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
6 Lyset skal blive mørkt i hans Telt, og hans Lampe over ham skal udslukkes.
Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
7 Hans Krafts Skridt skulle indsnævres, og hans eget Raad skal styrte ham.
Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
8 Thi han føres i Garnet ved sine egne Fødder, og han vandrer over et Net;
Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
9 Snaren holder ham om Hælen, Strikken snører sig fast om ham;
Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
10 Garnet for ham ligger skjult paa Jorden, og Fælden for ham ved Stien;
An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
11 Rædsler forfærde ham trindt omkring, og de drive ham hid og did, hvor han gaar;
Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
12 hans Kraft vansmægter af Hunger, og Ulykke er beredt til hans Side.
Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
13 Lemmerne under hans Hud skal Dødens førstefødte fortære, ja hans Lemmer skal den fortære.
Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
14 Han rives op fra sit Telt, som var hans Tillid, og han føres frem til Rædslernes Konge.
An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
15 Der skal bo i hans Telt, hvad der ikke hører ham til; Svovl skal strøs over hans Bolig.
Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
16 Hans Rødder skulle tørres nedentil, og oventil skal hans Gren afskæres.
Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
17 Hans Ihukommelse skal udslettes af Landet, og han skal intet Navn have paa Gaderne.
An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
18 De skulle udstøde ham fra Lyset til Mørket og bortjage ham fra Jorderige.
An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
19 Han skal ikke have en Søn og ej en Sønnesøn iblandt sit Folk, og der skal ingen blive tilovers i hans Boliger.
Ba shi da’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
20 Efterkommerne skulle forskrækkes over hans Dag, og de gamle skulle betages af Forfærdelse.
Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
21 Visselig, saadanne ere den uretfærdiges Boliger og saadant dens Sted, som ikke kender Gud.
Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”