< Job 16 >
1 Da svarede Job og sagde:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Jeg har hørt mange Ting som disse: I ere alle sammen besværlige Trøstere.
“Na ji abubuwa da yawa kamar waɗannan; dukanku ba ku iya ta’aziyya ba!
3 Bliver der Ende paa Ord, som kun ere Vind? eller hvad ægger dig, at du svarer?
Dogayen surutanku ba sa ƙare ne? Me yake sa kuke ta yin waɗannan surutai har kuke cin gaba da yin gardama?
4 Ogsaa jeg kunde tale som I, var kun eders Sjæl i min Sjæls Sted! jeg kunde sætte Ord sammen imod eder og ryste med Hovedet over eder.
Ni ma zan iya yin maganganu kamar yadda kuke yi in da kuna cikin halin da nake; zan iya faɗar duk abubuwan da kuke faɗi, in kaɗa muku kaina.
5 Jeg kunde styrke eder med min Mund, og mine Læbers Trøst kunde bringe Lindring.
Amma bakina zai ƙarfafa ku; ta’aziyyar da za tă fito daga bakina za tă kawar muku da ɓacin zuciyarku.
6 Vilde jeg tale, saa lindres min Smerte ikke; og vilde jeg lade være, hvad Lettelse finder jeg?
“Duk da haka in na yi magana, ba na samun sauƙi; in ma na yi shiru zafin ba ya tafiya.
7 Dog, nu har han gjort mig træt; du har ødelagt min hele Forsamling.
Ba shakka ya Allah ka gajiyar da ni; ka ɓata gidana gaba ɗaya.
8 Du har grebet mig, det blev et Vidne imod mig; og min Magerhed rejste sig imod mig, den taler imod mig.
Ka daure ni, ya kuma zama shaida; yadda na rame sai ƙasusuwa, wannan ya sa ake gani kamar don ni mai zunubi ne shi ya sa.
9 Hans Vrede har revet mig bort og forfulgte mig, han skar Tænder imod mig, som min Modstander stirrer han med sine Øjne imod mig.
Allah ya kai mini hari ya yi kaca-kaca da ni cikin fushinsa yana cizon haƙoransa don fushin da yake yi da ni; ya zura mini ido.
10 De opspilede deres Gab imod mig, de sloge mine Kinder med Forhaanelse, de flokkede sig til Hobe imod mig.
Mutane suka buɗe baki suka yi mini riyar reni; suka yi mini ba’a suka haɗu suka tayar mini.
11 Gud overantvordede mig til en uretfærdig og lod mig komme i de ugudeliges Hænder.
Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefa ni hannun mugaye.
12 Jeg var rolig; men han sønderrev mig og tog mig i Nakken og sønderslog mig og oprejste mig til en Skive for sig.
Dā ina zamana lafiya kome yana tafiya daidai; amma ya ragargaza ni; ya shaƙe ni a wuya; ya murƙushe ni na zama abin barata gare shi;
13 Hans Skytter omringe mig, han sønderskærer mine Nyrer og sparer ikke, han udgyder min Galde paa Jorden.
maharbansa sun kewaye ni. Ba tausayi, ya soke ni a ƙodata har jini ya zuba a ƙasa.
14 Han gennembryder mig med Stød paa Stød, han løber imod mig som en Krigshelt.
Ya ji mini rauni a kai a kai ya auko mini kamar mai yaƙi.
15 Jeg syede Sæk omkring min Hud og lagde mit Horn i Støvet.
“Ina makoki saye da tsummoki na ɓoye fuskata a cikin ƙura.
16 Mit Ansigt blusser af Graad, og Dødens Skygge hviler over mine Øjenlaage,
Fuskata ta yi ja don kuka idanuna sun kukumbura;
17 skønt ingen Uret er i mine Hænder, og min Bøn er ren.
duk da haka hannuwana ba su aikata ɓarna ba kuma addu’ata mai tsabta ce.
18 O Jord! skjul ikke mit Blod, og ingen Grænse være for mit Raab.
“Ya duniya, kada ki ɓoye jinina; bari yă yi kuka a madadina!
19 Alt nu, se, i Himmelen er mit Vidne, og min Talsmand er i det høje.
Ko yanzu haka shaidata tana sama; wanda zai tsaya mini yana sama.
20 Mine Venner ere blevne mine Bespottere, med Taarer vender mit Øje sig til Gud,
Shi mai yin roƙo a madadina abokina ne yayinda nake kuka ga Allah;
21 at han vilde skifte Ret mellem Manden og Gud, imellem Menneskets Barn og hans Næste.
a madadin mutum ya yi roƙo ga Allah kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.
22 Thi faa Aar skulle endnu komme, saa gaar jeg bort ad en Vej, ad hvilken jeg ikke kommer tilbage.
“Shekaru kaɗan suka rage in kama hanyar da ba a komawa.