< Job 13 >
1 Se, det har mit Øje set alt sammen; mit Øre har hørt og forstaaet sig derpaa.
“Idanuna sun ga waɗannan duka, kunnuwana sun ji sun kuma gane.
2 Hvad I vide, det ved jeg, ogsaa jeg, jeg falder ikke igennem for eder.
Abin da kuka sani, ni ma na sani; ba ku fi ni ba.
3 Dog vilde jeg gerne tale til den Almægtige, og jeg havde Lyst til at gaa i Rette med Gud.
Amma ina so in yi magana da Maɗaukaki, in kai kukana wurin Allah kai tsaye.
4 Men I sammensy Løgn: I ere alle sammen unyttige Læger.
Ku kuma kun ishe ni da ƙarairayi; ku likitocin wofi ne, dukanku!
5 Gid I vilde tie, saa skulde det regnes eder til Visdom!
In da za ku yi shiru gaba ɗaya! Zai zama muku hikima.
6 Kære, hører min Bevisning og mærker paa det, som jeg strider for med mine Læber.
Ku ji gardamata yanzu; ku ji roƙon da zai fito daga bakina.
7 Ville I forsvare Gud med Uret og forsvare ham med Svig?
Za ku iya yin muguwar magana a madadin Allah? Ko za ku yi ƙarya a madadinsa?
8 Ville I anse hans Person eller føre Sag for Gud?
Ko za ku nuna masa sonkai? Ko za ku yi gardama a madadinsa?
9 Vil det gaa godt, naar han undersøger eder? ville I bedrage ham, ligesom man bedrager et Menneske?
In ya bincike ku zai tarar ba ku da laifi? Ko za ku iya ruɗe shi yadda za ku ruɗi mutane?
10 Han skal visselig straffe eder, om I anse Personer i Løndom.
Ba shakka zai kwaɓe ku in kun nuna sonkai a ɓoye.
11 Skulde ikke hans Højhed forfærde eder og Rædsel for ham falde over eder?
Ko ikonsa ba ya ba ku tsoro? Tsoronsa ba zai auka muku ba?
12 Eders Tankesprog ere at ligne ved Aske, eders Borge ere Lerborge.
Duk surutanku kamar toka suke; kāriyarku na yimɓu ne.
13 Tier for mig, at jeg kan tale, og lad saa overgaa mig, hvad der vil!
“Ku yi shiru zan yi magana; sa’an nan abin da zai same ni yă same ni.
14 Hvorfor skulde jeg føre mit Kød bort i mine Tænder? jeg vil derimod sætte mit Liv i min Haand.
Don me na sa kaina cikin hatsari na yi kasada da raina?
15 Se, han slaar mig ihjel, jeg har intet Haab; kunde jeg blot retfærdiggøre mine Veje for hans Ansigt!
Ko da zai kashe ni ne, begena a cikinsa zai kasance; ba shakka zan kāre kaina a gabansa
16 Ogsaa dette skulde være mig en Frelse; thi der skal ingen vanhellig komme for hans Ansigt!
lalle wannan zai kawo mini kuɓuta gama ba wani marar tsoron Allah da zai iya zuwa wurinsa!
17 Hører flittig min Tale og det, jeg kundgør for eders Øren.
Ku saurara da kyau ku ji abin da zan faɗa; bari kunnuwanku su ji abin da zan ce.
18 Se, kære, jeg har indledet Sagen, jeg ved, at jeg skal kendes retfærdig.
Yanzu da na shirya ƙarata, na san za a ce ba ni da laifi.
19 Hvo er den, som kan trætte med mig? thi da maatte jeg tie og opgive Aanden.
Ko wani zai ce ga laifin da na yi? In an same ni da laifi, zan yi shiru in mutu.
20 Dog, gør ikke to Ting imod mig, da vil jeg ikke skjule mig for dit Ansigt:
“Kai dai biya mini waɗannan bukatu biyu kawai ya Allah, ba zan kuwa ɓoye daga gare ka ba;
21 Lad din Haand være langt fra mig og Rædsel for dig ikke forfærde mig!
Ka janye hannunka nesa da ni, ka daina ba ni tsoro da bantsoronka.
22 Kald saa, og jeg vil svare, eller jeg vil tale, og giv saa du mig Svar igen!
Sa’an nan ka kira ni, zan kuwa amsa, ko kuma ka bar ni in yi magana sai ka amsa mini.
23 Hvor mange ere mine Misgerninger og Synder? lad mig vide min Overtrædelse og min Synd!
Abubuwa nawa na yi waɗanda ba daidai ba, kuma zunubi ne? Ka nuna mini laifina da zunubina.
24 Hvorfor skjuler du dit Ansigt og holder mig for din Fjende?
Don me ka ɓoye mini fuskarka; ka kuma sa na zama kamar maƙiyinka?
25 Vil du jage det henvejrede Blad op og forfølge det tørre Straa?
Ko za a wahalar da ganye wanda iska take hurawa? Ko za ka bi busasshiyar ciyawa?
26 Thi du skriver Bitterheder op imod mig og lader mig faa min Ungdoms Synder til Arv.
Gama ka rubuta abubuwa marasa daɗi game da ni; ka sa na yi gādon zunuban ƙuruciyata.
27 Og du lægger mine Fødder i Stokken og tager Vare paa alle mine Stier; du afstikker Grænser for mine Fødders Saaler,
Ka daure ƙafafuna da sarƙa; kana kallon duk inda na taka ta wurin sa shaida a tafin ƙafafuna.
28 skønt jeg er en Mand, der bliver gammel som Trøske, som et Klæde, der ædes op af Møl.
“Haka mutum yake lalacewa kamar ruɓaɓɓen abu, kamar rigar da asu ya cinye.