< Jeremias 8 >
1 Paa den Tid, siger Herren, skulle de kaste Judas Kongers Ben og hans Fyrsters Ben og Præsternes Ben og Profeternes Ben og Jerusalems Indbyggeres Ben ud af deres Grave,
“‘A wancan lokaci, in ji Ubangiji, za a fitar da ƙasusuwan sarakuna da na shugabannin Yahuda, ƙasusuwan firistoci da na annabawa, da kuma ƙasusuwan mutanen Urushalima daga kaburbura.
2 og udsprede dem for Solen og for Maanen og for al Himmelens Hær, hvilke de elskede, og hvilke de tjente, og hvilke de vandrede efter, og hvilke de søgte, og hvilke de tilbade; de skulle ikke sankes op og ej begraves, men vorde til Møg oven paa Jorden.
Za a shimfiɗa su a rana da wata da kuma dukan taurarin sammai, waɗanda suka ƙaunata suka kuma bauta wa, waɗanda suka bi suka nemi shawarar suka kuma yi wa sujada. Ba za a tattara su ko a binne su ba, amma za su zama kamar juji a jibge a ƙasa.
3 Og Død skal foretrækkes for Liv af hver den, som er tilovers af de overblevne af denne onde Slægt; de, som ere overblevne i alle de Stæder, hvor jeg har drevet dem hen, siger den Herre Zebaoth.
Duk inda na kore su zuwa, dukan waɗanda suka ragu na wannan muguwar al’umma za su gwammaci mutuwa da rai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
4 Og du skal sige til dem: Saa siger Herren: Mon man falder og staar ikke op? mon man vender sig bort og vender ikke tilbage?
“Fada musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Sa’ad da mutane suka fāɗi, ba sa tashi ne? Sa’ad da mutum ya kauce, ba ya dawowa?
5 Hvorfor er dette Folk i Jerusalem da afveget med en evig Afvigelse? de holde fast ved Svig, de vægre sig ved at vende om.
To, me ya sa waɗannan mutane suka kauce? Me ya sa Urushalima kullum take kaucewa? Sun manne wa ƙarya; suka ƙi su dawo.
6 Jeg gav Agt og hørte til, de tale ikke Ret, der er ingen, som angrer sin Ondskab og siger: Hvad har jeg gjort? de have alle sammen vendt sig bort, hver til sit Løb, som en Hest, der render i Krigen.
Na saurara sosai, amma ba su faɗi wata maganar kirki ba. Ba wanda ya tuba daga muguntarsa, sai ma cewa yake, “Me na yi?” Kowa ta kai-ta-kai yake kamar dokin da ya kutsa kai a fagen fama.
7 Selv Storken under Himmelen kender sine bestemte Tider, og en Turteldue og en Trane og en Svale tage Vare paa den Tid, de skulle komme; men mit Folk, de kende ikke Herrens Ret.
Ko shamuwa ta sararin sama ma takan san lokutan da aka tsara mata, kurciya, mashirare da kuma zalɓe sukan lura da lokacin ƙauransu. Amma mutanena ba su san abubuwan da Ubangiji yake bukata ba.
8 Hvorledes kunne I sige: Vi ere vise, og Herrens Lov er hos os? men se, Skrivernes Løgnepen har arbejdet for Løgnen.
“‘Yaya za ku ce, “Muna da hikima, gama muna da dokar Ubangiji,” alhali alƙalamin ƙarya na magatakarda ya yi ƙarya?
9 De vise skulle blive til Skamme, forfærdes og besnæres; se, de have forkastet Herrens Ord, hvad for Visdom skulde de have?
Za a kunyatar da masu hikima; za su yi fargaba a kuma kama su. Da yake sun ƙi maganar Ubangiji, wace irin hikima kuka ce kuke da ita?
10 Derfor vil jeg give deres Hustruer til andre og deres Agre til dem, som skulle eje dem; thi fra den mindste til den største tragter enhver efter Vinding, fra Profet og indtil Præst lægge de alle Vind paa Løgn.
Saboda haka zan ba da matansu ga waɗansu gonakinsu kuma ga waɗansu da suka ci da yaƙi. Tun daga ƙarami har zuwa babba, kowannensu yana haɗamar cin muguwar riba; har da annabawa da firistoci ma, kowannensu yana ƙarya.
11 Og de lægede mit Folks Datters Brøst, som om det var en let Sag, idet de sagde: Fred! Fred! dog der var ikke Fred.
Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, “Lafiya, Lafiya,” alhali kuwa ba lafiya.
12 De ere blevne til Skamme; thi de gjorde Vederstyggelighed; dog skamme de sig aldeles ikke og vide ikke at være skamfulde; derfor skulle de falde iblandt dem, som falde; i den Tid, naar de hjemsøges skulle de snuble, siger Herren.
Sukan ji kunyar halin banƙyamarsu kuwa? Sam, ba su da kunya ko kaɗan; ba su ma san yadda za su ji kunya ba. Saboda haka sukan fāɗi tare da fāɗaɗɗu; za su fāɗi sa’ad da aka hukunta su, in ji Ubangiji.
13 Jeg vil helt rive dem bort, siger Herren; der er ikke Druer paa Vintræet og ej Figen paa Figentræet, og Bladene ere visne, og jeg gav dem til Pris for dem, der drage hen over dem.
“‘Zan ƙwace girbinsu, in ji Ubangiji. Ba a za sami inabi a kuringa ba. Ba za a sami’ya’ya a itacen ɓaure ba, ganyayensu kuwa za su bushe. Abin da na ba su za a ƙwace.’”
14 Hvorfor sidde vi stiller samler eder, og lader os gaa ind i de faste Stæder og omkomme der; thi Herren vor Gud har ladet os omkomme og givet os besk Vand at drikke; thi vi have syndet imod Herren.
Me ya sa muke zama a nan? Mu tattaru! Mu gudu zuwa birane masu katanga mu mutu a can! Gama Ubangiji Allahnmu ya ƙaddara mana mutuwa ya kuma ba mu ruwan dafi mu sha, domin mun yi masa zunubi.
15 Man venter paa Fred, og det bliver ikke godt; paa Lægedoms Tid, og se, Forfærdelse kommer.
Mun sa zuciya ga salama amma ba lafiya, mun sa zuciya ga lokacin warkarwa amma sai ga razana.
16 Fra Dan høres hans Hestes Fnysen, for Lyden af hans vældige Hestes Vrinsken ryster det ganske Land; og de komme og fortære Landet og dets Fylde, Staden og Indbyggerne derudi.
Daga Dan ana jin tirjin dawakan abokin gāba; da jin haniniyar ingarmunsu dukan ƙasar ta girgiza. Sun zo su cinye ƙasar da kome da yake cikinta, birni da dukan mazaunanta.
17 Thi se, jeg sender iblandt eder Slanger, Basilisker, som ikke lade sig besværge, og de skulle bide eder, siger Herren.
“Duba, zan aika macizai masu dafi a cikinku, kāsā, waɗanda ba su da maƙari, za su kuwa sassare ku,” in ji Ubangiji.
18 Hvor finder jeg Vederkvægelse for Sorgen! mit Hjerte er sygt i mig.
Ya mai ta’aziyyata a cikin baƙin ciki, zuciyata ta ɓaci ƙwarai.
19 Se, mit Folks Datters Raab lyder fra et langt bortliggende Land: Er da Herren ikke i Zion? eller er dets Konge ikke der? Hvorfor have de fortørnet mig med deres udskaarne Billeder, med et fremmed Folks Afguder?
Ka saurari kukan mutanena daga ƙasa mai nisa suna cewa, “Ubangiji ba ya a Sihiyona ne? Sarkinta ba ya can ne kuma?” “Me ya sa suka tsokane ni da gumakansu har na yi fushi, da baƙin gumakansu marasa amfani?”
20 Høsten er forbi, Sommeren er til Ende, og vi ere ikke frelste.
“Girbi ya wuce, damuna ta ƙare, ba a kuwa cece mu ba.”
21 Jeg er sønderknust over mit Folks Datters Sønderknuselse, jeg gaar i Sørgeklæder, Forskrækkelse har betaget mig.
Da yake an ragargazar da mutanena, an ragargaza ni ke nan; na yi kuka, tsoro ya kama ni.
22 Er der da ingen Balsam i Gilead? eller er der ingen Læge der? thi hvorfor er der ikke lagt Forbinding paa mit Folks Datter?
Ba magani ne a Gileyad? Ba likita ne a can? To, me ya sa ba warkarwa wa raunin mutanena?