< Jeremias 43 >

1 Og det skete, der Jeremias var færdig med at tale til alt Folket alle Herren deres Guds Ord, med hvilke Herren deres Gud havde sendt ham til dem, alle hine Ord,
Sa’ad da Irmiya ya gama faɗa wa mutane dukan maganar Ubangiji Allahnsu, duk abin da Ubangiji ya aike shi ya faɗa musu,
2 da sagde Asaria, Hosajas Søn, og Johanan, Kareaks Søn, og alle de hovmodige Mænd til Jeremias: Du taler Løgn, Herren var Gud har ikke sendt dig og sagt: I skulle ikke drage til Ægypten for at være der som fremmede.
Azariya ɗan Hoshahiya da Yohanan ɗan Kareya da dukan masu ɗaga kai suka ce wa Irmiya, “Kana ƙarya ne! Ubangiji Allahnmu bai aike ka ka ce, ‘Kada ku tafi Masar don ku zauna a can.’
3 Men Baruk, Nerias Søn, ophidser dig imod os, for at give os i Kaldæernes Haand, at de kunne dræbe os eller bortføre os til Babel.
Amma Baruk ɗan Neriya yana zuga ka a kanmu don ka ba da mu ga Babiloniyawa, don su kashe mu ko su kai mu zaman bauta a Babilon.”
4 Saa hørte Johanan, Kareaks Søn, og alle Høvedsmændene for Hæren og alt Folket ikke Herrens Røst om at blive boende i Judas Land.
Saboda haka Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji da dukan mutane suka yi rashin biyayya ga umarnin Ubangiji da su zauna a ƙasar Yahuda.
5 Men Johanan, Kareaks Søn, og alle Høvedsmændene for Hæren toge alle de overblevne af Juda, og dem, som vare komne tilbage fra alle de Folkeslag, hvorhen de havde været fordrevne, for at bo i Judas Land:
A maimako, Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji suka kwashe raguwar Yahuda waɗanda suka dawo su zauna a ƙasar Yahuda daga dukan al’umman inda aka kora su.
6 Mændene og Kvinderne og de smaa Børn og Kongens Døtre og hver Sjæl, som Nebusar-Adan, den øverste for Livvagten, havde ladet blive hos Gedalia, Ahikams Søn, Safans Sønnesøn, samt Profeten Jeremias, og Baruk, Nerias Søn;
Suka kuma kwashe dukan maza, mata da yara da’ya’yan sarki mata waɗanda Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya bari tare da Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, da Irmiya annabi da kuma Baruk ɗan Neriya.
7 og de kom til Ægyptens Land, thi de havde ikke hørt Herrens Røst; og de kom lige til Thakpankes.
Saboda haka suka shiga Masar cikin rashin biyayya ga Ubangiji suka tafi har can Tafanes.
8 Og Herrens Ord kom til Jeremias i Thakpankes, saa lydende:
A Tafanes maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
9 Tag store Stene i din Haand, og skjul dem i Leret ved Teglovnen, som er ved Indgangen til Faraos Hus i Thakpankes for Judas Mænds Øjne;
“Yayinda Yahudawa suna kallo, ka ɗauki waɗansu manyan duwatsu tare da kai ka kuma binne su cikin yumɓu a tubalin dakalin ƙofar shiga fadar Fir’auna a Tafanes.
10 og sig til dem: Saa siger den Herre Zebaoth, Israels Gud: Se, jeg sender Bud og henter Nebukadnezar, Kongen af Babel, min Tjener, og jeg vil sætte hans Trone oven over disse Stene, som jeg har skjult, og han skal udbrede sit kostelige Tæppe over dem.
Sa’an nan ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, zan aika wa bawana Nebukadnezzar sarkin Babilon, zan kuma sa kursiyinsa a kan waɗannan duwatsun da na binne a nan; zai fadada bukkar mulkinsa a bisansu.
11 Og han skal komme og slaa Ægyptens Land: De, som ere bestemte til Døden, blive Dødens, de, som ere bestemte til Fangenskabet, blive Fangenskabets, de, som ere bestemte til Sværdet, blive Sværdets.
Zai zo ya yaƙi Masar, ya kawo mutuwa ga waɗanda aka ƙaddara musu mutuwa, zaman bauta ga waɗanda aka ƙaddara musu zaman bauta, da kuma takobi ga waɗanda aka ƙaddara su mutu ta takobi.
12 Og jeg vil stikke Ild paa Ægyptens Guders Huse, og han skal opbrænde disse og bortføre hine, og han skal svøbe Ægyptens Land om sig, ligesom en Hyrde svøber sit Klædebon om sig, og drage ud derfra med Fred.
Zai sa wuta wa haikalan allolin Masar; zai ƙone haikalansu yă kuma kwashe allolinsu bayi. Kamar yadda makiyayi yakan yafa mayafinsa kewaye da shi, haka zai yafa Masar kewaye da kansa ya kuma tashi a wurin babu abin da ya same shi.
13 Og han skal sønderbryde Billedstøtterne i Beth-Semes, som er i Ægyptens Land, og opbrænde Ægyptens Guders Huse med Ild.
A can cikin haikalin rana a Masar zai rushe al’amudan duwatsu yă kuma ƙone haikalan allolin Masar.’”

< Jeremias 43 >