< Jeremias 33 >
1 Og Herrens Ord kom til Jeremias anden Gang, medens han endnu var indelukket i Fængselets Forgaard; det lød:
Yayinda Irmiya yana a tsare a sansanin matsara, sai maganar Ubangiji ta zo masa sau na biyu cewa,
2 Saa siger Herren, som gør det, Herren, som beslutter det, saa at han udfører det, Herren er hans Navn:
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicci duniya, Ubangiji wanda ya siffanta ta ya kuma kafa ta, Ubangiji ne sunansa.
3 Raab til mig, og jeg vil svare dig, og jeg vil tilkendegive dig store og velforvarede Ting, som du ikke ved.
‘Kira gare ni zan kuwa amsa maka in kuma faɗa maka manyan abubuwan da ba a iya kaiwa, da ba ka sani ba.’
4 Thi saa siger Herren, Israels Gud, om denne Stads Huse og om Judas Kongers Huse, som ere slaaede ned formedelst Belejringsvoldene og formedelst Sværdet,
Gama ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa game da gidaje a wannan birni da fadodin Yahuda da aka rurrushe domin a yi amfani da su a kan mahaurai da kuma takobi
5 og om dem, som kom ind for at stride imod Kaldæerne og for at fylde op med døde Kroppe af Mennesker, hvilke jeg slog i min Vrede og i min Harme, og idet jeg skjulte mit Ansigt for denne Stad for al deres Ondskabs Skyld:
a yaƙi da Babiloniyawa. ‘Za su cika da gawawwakin mutane waɗanda na kashe da fushina da hasalata. Zan ɓoye fuskata wa wannan birni saboda dukan muguntarsu.
6 Se, jeg vil lade dens Helbredelse og Lægedom tage til og læge dem, og jeg vil oplade dem en Rigdom af Fred og Sandhed.
“‘Duk da haka, zan kawo lafiya da warkarwa gare ta; zan warkar da mutanena in kuma wadata su da salama da zama lafiya.
7 Og jeg vil omvende Judas Fangenskab og Israels Fangenskab, og jeg vil bygge dem som i Begyndelsen.
Zan komo da Yahuda da Isra’ila daga bauta zan kuma sāke gina su kamar yadda suke a dā.
8 Og jeg vil rense dem fra al deres Misgerning, med hvilken de syndede imod mig, og forlade dem alle deres Misgerninger, med hvilke de have syndet imod mig, og med hvilke de have forbrudt sig imod mig.
Zan tsarkake su daga dukan zunubin da suka yi mini zan kuma gafarta musu dukan zunubansu na yin mini tawaye.
9 Og det skal være mig til et glædeligt Navn, til Lov og til Ære for alle Jordens Folkeslag, som høre alt det gode, jeg gør dem; og de skulle forfærdes og skælve over alt det gode og over al den Fred, som jeg vil give dem.
Sa’an nan birnin nan za tă sa in zama sananne, farin ciki, yabo da girma a gaban dukan al’ummai a duniya da suka ji abubuwa masu kyau da na yi mata; za su kuma yi mamaki su kuma yi rawan jiki saboda yalwar wadata da salamar da na ba ta.’
10 Saa siger Herren: Endnu skal der paa dette Sted, om hvilket I sige: Det er øde, uden Folk og uden Fæ, i Judas Stæder og paa Jerusalems Gader, som ere ødelagte, uden Folk og uden Indbyggere og uden Fæ, høres
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Kuna cewa game da wannan wuri, “Kango ne, babu mutane ko dabbobi.” Duk da haka a cikin garuruwan Yahuda da titunan Urushalima da aka yashe, inda ba mutane ko dabbobi, za a sāke jin
11 Fryds Røst og Glædes Røst, Brudgoms Røst og Bruds Røst, deres Røst, som sige: Takker den Herre Zebaoth, thi Herren er god, thi hans Miskundhed er evindelig, og deres, som bringe Takoffer til Herrens Hus; thi jeg vil omvende Landets Fangenskab som i Begyndelsen, sagde Herren.
sowa ta farin ciki da murna, muryoyin amarya da na ango, da muryoyin waɗanda suka kawo hadayun salama a gidan Ubangiji suna cewa, “‘“Ku yi godiya ga Ubangiji Maɗaukaki, gama Ubangiji mai alheri ne; ƙaunarsa za tă dawwama har abada.” Gama zan mayar da wadatar ƙasar kamar yadda suke a dā,’ in ji Ubangiji.
12 Saa siger den Herre Zebaoth: Endnu skal der være paa dette Sted, som er øde uden Folk og uden Fæ, og i alle dets Stæder Bolig for Hyrder, som lade Hjorden hvile.
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, ‘A wannan wuri, kango da babu mutane ko dabbobi, cikin dukan garuruwansa za a sāke kasance da wurin kiwo don makiyaya su hutar da garkunansu.
13 I Stæderne paa Bjerget, i Stæderne i Lavlandet og i Stæderne imod Sønden og i Benjamins Land og trindt omkring Jerusalem og i Judas Stæder skulle Hjordene endnu gaa forbi Tællerens Hænder, siger Herren.
A cikin garuruwan ƙasar tudu, garuruwan yammancin gindin dutse da na Negeb, a yankin Benyamin, a cikin ƙauyuka kewayen Urushalima da kuma a cikin garuruwan Yahuda, garkuna za su sāke bi a ƙarƙashin hannun mai ƙidayawa,’ in ji Ubangiji.
14 Se, de Dage komme, siger Herren, da jeg vil stadfæste det gode Ord, hvilket jeg har talt til Israels Hus og om Judas Hus.
“‘Kwanaki suna zuwa,’ in ji Ubangiji, ‘sa’ad da zan cika alkawarin alheri da na yi wa gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda.
15 I de Dage og paa den Tid vil jeg lade for David en Retfærdigheds Vækst opvokse; og han skal øve Ret og Retfærdighed paa Jorden.
“‘A waɗannan kwanaki da kuma a wannan lokaci zan tā da Reshe mai adalci daga zuriyar Dawuda; zai yi abin da yake daidai da kuma gaskiya a ƙasar.
16 I de Dage skal Juda frelses og Jerusalem bo tryggelig; og dette er Navnet, man skal give den: Herren vor Retfærdighed.
A kwanakin nan zan ceci Yahuda Urushalima kuma za tă zauna lafiya. Sunan da za a kira ta shi ne, Ubangiji Adalcinmu.’
17 Thi saa siger Herren: Der skal ikke fattes for David en Mand, som skal sidde paa Israels Hus's Trone.
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Dawuda ba zai taɓa rasa mutumin da zai zauna a gadon sarautar Isra’ila ba,
18 Og der skal ikke fattes for Præsterne, Leviterne, en Mand til at staa for mit Ansigt, som skal ofre Brændoffer og antænde Madoffer og lave Slagtoffer alle Dagene.
ba kuwa firistoci waɗanda suke Lawiyawa za su rasa mutumin da zai ci gaba da tsaya a gabana don miƙa hadayun ƙonawa, ya ƙona hadayun hatsi ya kuma miƙa sadakoki ba.’”
19 Og Herrens Ord kom til Jeremias, saaledes:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
20 Saa siger Herren: Dersom I kunne bryde min Pagt med Dagen og min Pagt med Natten, saa at der ikke bliver Dag og Nat, naar Tiden er:
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘In ka tā da alkawarina na rana da kuma alkawarina na dare, har dare da rana ba za su ƙara bayyana a ƙayyadaddun lokutansu ba,
21 Da skal ogsaa min Pagt med David, min Tjener, brydes, at han ikke skal have en Søn til at være Konge paa hans Trone, og med Leviterne, Præsterne, mine Tjenere.
to, sai a tā da alkawarina da Dawuda bawana da alkawarina da Lawiyawan da suke firistoci masu hidima a gabana, Dawuda kuma ba zai ƙara kasance da zuriyar da za tă yi mulki.
22 Thi ligesom Himmelens Hær ikke kan tælles og Havets Sand ikke maales, saaledes vil jeg formere Davids, min Tjeners, Sæd og Leviterne, som tjene mig.
Zan sa zuriyar Dawuda bawana da kuma Lawiyawan da suke hidima a gabana su yi yawa kamar taurarin sararin sama da kuma yashin bakin tekun da ba a iya ƙidaya.’”
23 Og Herrens Ord kom til Jeremias, saalunde:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
24 Har du ikke set, hvad dette Folk har talt, idet det siger: De to Slægter, som Herren havde udvalgt, dem har han forkastet? og de foragte mit Folk, saa at det ikke mere er et Folk for deres Ansigt.
“Ba ka lura ba cewa waɗannan mutane suna cewa, ‘Ubangiji ya ƙi masarautai biyu da ya zaɓa’? Saboda haka suka rena mutanena ba sa ƙara ɗaukansu a matsayin al’umma.
25 Saa siger Herren: Dersom jeg ikke har fastsat min Pagt med Dag og Nat, Himmelens og Jordens Skikke,
Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘In ban kafa alkawarina game da rana da kuma game da dare ba in kuma gyara dokokin sama da duniya ba,
26 da vil jeg ogsaa forkaste Jakobs og Davids, min Tjeners, Sæd, saa at jeg ikke af hans Sæd tager dem, som skulle herske over Abrahams, Isaks og Jakobs Sæd; thi jeg vil omvende deres Fangenskab og forbarme mig over dem.
to zan ƙi zuriyar Yaƙub da na Dawuda bawana ba zan kuma zaɓi ɗaya daga cikin’ya’yansa maza ya yi mulki a kan zuriyar Ibrahim, Ishaku da Yaƙub ba. Gama zan mayar da wadatarsu in kuma yi musu jinƙai.’”