< Jeremias 31 >

1 Paa den Tid, siger Herren, vil jeg være alle Israels Slægters Gud, og de skulle være mit Folk.
“A lokacin nan, zan zama Allah na dukan kabilan Isra’ila, za su kuma zama mutanena,” in ji Ubangiji.
2 Saa siger Herren: Et Folk, som er overblevet fra Sværd, har fundet Naade i Ørken; jeg gaar hen for at skaffe Israel Hvile.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Mutanen da suka tsere wa takobi za su sami tagomashi a hamada; zan zo don in ba da hutu ga Isra’ila.”
3 Herren har ladet sig se for mig fra det fjerne: Jeg har elsket dig med en evig Kærlighed, derfor har jeg bevaret dig Miskundhed.
Ubangiji ya bayyana mana a dā, yana cewa, “Na ƙaunace ku da madawwamiyar ƙauna; na janye ku da ƙauna marar iyaka.
4 Endnu vil jeg opbygge dig, og du skal bygges, du Israels Jomfru! endnu skal du pryde dig med Pauker og gaa ud i de legendes Dans.
Zan sāke gina ki za ki kuwa sāke ginuwa, ya Budurwar Isra’ila. Za ki kuma ɗauki ganganki ki fita don ki yi rawa da masu farin ciki.
5 Endnu skal du plante Vingaarde paa Samarias Bjerge; de, som plante, skulle plante dem og tage dem i Brug.
Za ki sāke dasa gonakin inabi a kan tussan Samariya; manoma za su yi shuka a kansu su kuma ji daɗin amfaninsu.
6 Thi der kommer en Dag, da Vægtere paa Efraims Bjerg skulle raabe: Staar op, og lader os gaa op til Zion, til Herren vor Gud.
Za a yi ranar da matsara za su tā da murya a kan tuddan Efraim su ce, ‘Ku zo, bari mu haura Sihiyona, zuwa wurin Ubangiji Allahnmu.’”
7 Thi saa siger Herren: Fryder eder over Jakob med Glæde, og jubler over det første af Folkene, lader det høres, priser og siger: Herre, frels dit Folk, det overblevne af Israel.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku rera don farin ciki wa Yaƙub; ku yi sowa don al’ummai da suke nesa. Ka sa a ji yabanku, ku kuma ce, ‘Ya Ubangiji ka ceci mutanenka, raguwar Isra’ila.’
8 Se, jeg fører dem fra Nordenland og vil samle dem fra det yderste af Jorden; iblandt dem skal der være blinde og halte, frugtsommelige og fødende til Hobe; de skulle komme hid tilbage som en stor Forsamling.
Ga shi, zan kawo su daga ƙasar arewa in tattara su daga iyakar duniya. A cikinsu makafi da guragu za su kasance, mata masu ciki da matan da suke naƙuda; jama’a mai yawan gaske za su komo.
9 De skulle komme med Graad, og under deres ydmyge Bønner vil jeg føre dem frem; jeg vil lede dem til Vandbække paa en jævn Vej, hvor de ikke skulle støde sig; thi jeg er bleven Israels Fader, og Efraim, han er min førstefødte Søn.
Za su zo da kuka; za su yi addu’a yayinda nake komo da su. Zan bishe su kusa da rafuffukan ruwa a miƙaƙƙiyar hanya inda ba za su yi tuntuɓe ba, domin ni ne mahaifin Isra’ila, Efraim kuma ɗan farina ne.
10 Hører, I Hedninger I Herrens Ord og kundgører det paa Øerne i det fjerne og siger: Den, som adspredte Israel, skal samle det og bevare det som en Hyrde sin Hjord.
“Ku ji maganar Ubangiji, ya al’ummai; ku yi shelarta a gaban teku masu nesa cewa, ‘Shi wanda ya watsar da Isra’ila zai tattara su zai kuma lura da garkensa kamar makiyayi.’
11 Thi Herren har løskøbt Jakob og igenløst ham af dens Haand, som var stærkere end han.
Gama Ubangiji zai fanshi Yaƙub zai cece su daga hannun waɗanda suka fi su ƙarfi.
12 Og de skulle komme og synge med Fryd paa Zions Høj og strømme til Herrens gode Gaver, til Korn og til Most og til Olie og til unge Faar og Øksne; og deres Sjæl skal være som en vandrig Have, og de skulle ikke herefter bedrøves mere.
Za su zo su yi sowa don farin ciki a ƙwanƙolin Sihiyona; za su yi farin ciki cikin yalwar Ubangiji hatsi, sabon ruwan inabi da mai,’ya’yan garken tumaki da na shanu. Za su zama kamar gonar da aka yi wa banruwa, ba za su ƙara yin baƙin ciki ba.
13 Da skal en Jomfru glæde sig i Dans, og unge og gamle til Hobe; og jeg vil vende deres Sorg til Glæde og trøste dem og glæde dem efter deres Bedrøvelse.
’Yan mata za su yi rawa su kuma yi murna, haka ma samari da tsofaffi. Zan mai da makokinsu farin ciki; zan ta’azantar da su in kuma sa su yi farin ciki a maimakon baƙin ciki.
14 Og jeg vil vederkvæge Præsternes Sjæl med det fede, og mit Folk, de skulle mættes med mine Gaver, siger Herren.
Zan ƙosar da firistoci da yalwa, mutanena kuma za su cika da yalwa,” in ji Ubangiji.
15 Saa siger Herren: Der er hørt en Røst i Rama, en Klage, en bitter Graad, Rakel græder over sine Børn; hun vægrer sig ved at lade sig trøste over sine Børn, thi de ere ikke mere til.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “An ji murya daga Rama, makoki da kuka mai zafi, Rahila tana kuka domin’ya’yanta ta kuma ƙi a ta’azantar da ita domin’ya’yanta ba su.”
16 Saa siger Herren: Hold din Røst fra Graad og dine Øjne fra Taarer; thi der er Løn for dit Arbejde, siger Herren; og de skulle komme tilbage fra Fjendens Land.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Hana muryarki kuka da kuma idanunki hawaye, gama za a sāka wa aikinki,” in ji Ubangiji. “Za su komo daga ƙasar abokin gāba.
17 Og der er Haab for din sidste Tid, siger Herren; og Børnene skulle komme igen til deres Landemærker.
Saboda haka akwai sa zuciya domin nan gaba,” in ji Ubangiji. “’Ya’yanki za su komo ƙasarsu.
18 Jeg har hørt Efraim ynkeligt klage: Du har tugtet mig, og jeg er tugtet som en Kalv, der ikke er tæmmet; omvend mig, og jeg vil omvende mig; thi du er Herren min Gud.
“Tabbatacce na ji gurnanin Efraim yana cewa, ‘Ka hore ni kamar ɗan maraƙi mai ƙin ji, na kuwa horu. Ka mayar da ni, zan kuwa dawo, domin kai ne Ubangiji Allahna.
19 Thi efter at jeg havde vendt mig bort, angrede jeg det, og efter at jeg var kommen til at erkende det, slog jeg mig paa Hoften; jeg var beskæmmet og skammede mig, thi jeg maatte bære min Ungdoms Skændsel.
Bayan na kauce, sai na tuba; bayan na gane, sai na sunkuyar da kaina. Na ji kunya da ƙasƙanci domin ina ɗauke da kunyar ƙuruciyata.’
20 Er da Efraim mig en dyrebar Søn? eller er han mit Yndlingsbarn? thi saa ofte jeg end har talt imod ham, kommer jeg ham dog endnu flittigt i Hu; derfor bruser mit Indre for ham, jeg vil forbarme mig over ham, siger Herren.
Efraim ba ƙaunataccen ɗana ba ne, ɗan da nake jin daɗinsa? Ko da yake sau da dama ina maganar gāba a kansa, duk da haka nakan tuna da shi. Saboda haka zuciyata tana marmarinsa; ina da jinƙai mai girma dominsa,” in ji Ubangiji.
21 Oprejs dig Vejvisere, sæt dig Mærkestene, agt vel paa Stien, den Vej, ad hvilken du gik bort; vend tilbage, du Israels Jomfru, vend tilbage til disse dine Steder.
“Ki kafa alamun hanya; ki sa shaidun bishewa. Ki lura da babbar hanya da kyau, hanyar da kika bi. Ki komo, ya Budurwar Isra’ila, ki komo zuwa garuruwanki.
22 Hvor længe vil du fare omkring, du frafaldne Datter; thi Herren skaber nyt paa Jorden: Kvinde skal omgive Manden.
Har yaushe za ki yi ta yawo, Ya’ya marar aminci? Ubangiji zai ƙirƙiro sabon abu a duniya mace za tă kewaye namiji.”
23 Saa siger den Herre Zebaoth, Israels Gud: Endnu skulle de sige dette Ord i Judas Land og i hans Stæder, naar jeg omvender deres Fangenskab: Herren velsigne dig, du Retfærdigheds Bolig! du hellige Bjerg!
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Sa’ad da na komo da su daga bauta mutane a ƙasar Yahuda da cikin garuruwanta za su sāke yi amfani da waɗannan kalmomi. ‘Ubangiji ya albarkace ka, ya mazauni mai adalci, ya tsarkakan dutse.’
24 Og Juda og alle hans Stæder skulle bo derudi til Hobe, de, som dyrke Ageren, og de, som drage om med Hjorden.
Mutane za su zauna tare a Yahuda da dukan garuruwansa, manoma da waɗanda suke yawo da garkunansu.
25 Thi jeg vederkvæger den trætte Sjæl og mætter hver vansmægtet Sjæl.
Zan wartsake waɗanda suka gaji in kuma ƙosar da waɗanda ransu ya yi yaushi.”
26 Derfor vaagnede jeg op og saa, og min Søvn var mig sød.
A kan wannan na farka na duba kewaye. Barcina ya yi mini daɗi.
27 Se, de Dage komme, siger Herren, da jeg vil besaa Israels Hus og Judas Hus med en Sæd af Folk og med en Sæd af Kvæg.
“Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan kafa gidan Isra’ila da gidan Yahuda da’ya’yan mutane da na dabbobi.
28 Og det skal ske, at ligesom jeg var aarvaagen over dem til at oprykke og til at nedrive og til at nedbryde og til at ødelægge og til at handle ilde med dem: Saaledes vil jeg være aarvaagen over dem til at bygge og til at plante, siger Herren.
Kamar yadda na lura da su don su tumɓuke su kuma rusar, su lalatar, su hallaka su kuma kawo masifa, haka zan lura da su don su gina su kuma dasa,” in ji Ubangiji.
29 I de Dage skulle de ikke mere sige: Fædrene aade sure Druer, og Børnenes Tænder bleve ømme;
“A waɗannan kwanaki mutane ba za su ƙara ce, “‘Ubanni suka ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoran’ya’ya suka mutu ba.’
30 men enhver skal dø for sin egen Misgernings Skyld, hvert Menneske, som æder de sure Druer, hans Tænder skulle blive ømme.
A maimako, kowa zai mutu saboda zunubinsa; duk wanda ya ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoransa ne za su mutu.
31 Se, de Dage komme, siger Herren, da jeg vil slutte en ny Pagt med Israels Hus og med Judas Hus;
“Lokaci yana zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan yi sabon alkawari da gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda.
32 ikke efter den Pagt, som jeg sluttede med deres Fædre, der jeg tog dem ved Haanden for at udføre dem af Ægyptens Land, hvilken Pagt med mig de brøde, endskønt jeg var deres Ægtemand, siger Herren;
Ba zai zama kamar alkawarin da na yi da kakanni kakanninsu ba sa’ad da na kama su da hannu na bishe su daga Masar, domin sun take alkawarina, ko da yake na zama miji a gare su,” in ji Ubangiji.
33 men dette er Pagten, som jeg vil slutte med Israels Hus, efter disse Dage, siger Herren: Jeg giver min Lov i deres Indre og skriver den i deres Hjerte, og jeg vil være deres Gud, og de skulle være mit Folk.
“Ga alkawarin da zan yi da gidan Isra’ila bayan wannan lokaci,” in ji Ubangiji. “Zan sa dokata a tunaninsu in kuma rubuta ta a zukatansu. Zan zama Allahnsu, za su kuma zama mutanena.
34 Og de skulle ikke mere lære nogen sin Næste eller nogen sin Broder, sigende: Kender Herren; thi de skulle alle kende mig, baade de smaa og de store iblandt dem, siger Herren; thi jeg vil forlade dem deres Skyld og ikke ydermere komme deres Synd i Hu.
Mutum ba zai ƙara koya wa maƙwabci ba, ko ya koya wa ɗan’uwansa cewa, ‘Ka san Ubangiji,’ domin duk za su san ni, daga ƙaraminsu har zuwa babba,” in ji Ubangiji. “Gama zan gafarta muguntarsu ba zan kuwa ƙara tuna da zunubansu ba.”
35 Saa siger Herren, som sætter Solen til Lys om Dagen, Maanens og Stjernernes Love til Lys om Natten, han, som oprører Havet, at dets Bølger bruse, Herre Zebaoth er hans Navn:
Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya kafa rana don tă yi haske a yini shi da ya sa wata da taurari su yi haske da dare, shi da yake dama teku don raƙuman ruwansa su yi ruri Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
36 Dersom disse Love vige for mit Ansigt, siger Herren, da skal og Israels Sæd ophøre med at være et Folk for mit Ansigt alle Dage.
“In dai wannan kafaffiyar ƙa’ida ta daina aiki a gabana,” in ji Ubangiji, “to, sai zuriyar Isra’ila ta daina zama al’umma a gabana.”
37 Saa siger Herren: Dersom Himlene heroventil kunne maales, og Jordens Grundvold hernedentil kan udforskes, saa vil jeg og forkaste al Israels Sæd for alt det, som de have gjort, siger Herren.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “In a iya auna sammai a kuma bincike tushen duniya a ƙarƙas to, sai in ƙi dukan zuriyar Isra’ila ke nan saboda dukan abin da suka yi,” in ji Ubangiji.
38 Se, de Dage komme, siger Herren, da Staden skal bygges for Herren, fra Hananeels Taarn indtil Hjørneporten.
“Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da za a sāke gina wannan birni domina daga Hasumiyar Hananel zuwa Ƙofar Kusurwa.
39 Og over for den skal Maalesnoren gaa videre over Garebs Høj og vende sig om imod Goat.
Ma’auni zai miƙe daga can ya nausa kai tsaye zuwa tudun Gareb sa’an nan ya juya zuwa Gowa.
40 Og den hele Dal med Aadslerne og Asken og alle Markerne indtil Kedrons Bæk, indtil Hesteportens Hjørne imod Østen skal være Herren en Helligdom; den skal ikke forstyrres og ikke nedbrydes mere evindelig.
Dukan kwarin da ake zubar da toka da kuma gawawwaki, da dukan lambatun da suke can har zuwa Kwarin Kidron a gabas zuwa kusurwar Ƙofar Doki, za su zama mai tsarki ga Ubangiji. Ba za a ƙara tumɓuke birnin ko a rushe shi ba.”

< Jeremias 31 >