< Jeremias 30 >

1 Det Ord, som kom til Jeremias fra Herren, saalydende:
Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga Ubangiji.
2 Saa siger Herren, Israels Gud: Skriv dig alle de Ord, som jeg har talt til dig, i en Bog.
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Ka rubuta a cikin littafi dukan maganganun da na yi maka.
3 Thi se, de Dage komme, siger Herren, da vil jeg vende mit Folk Israels og Judas Fangenskab, siger Herren, og føre dem tilbage til det Land, som jeg har givet deres Fædre, at de skulle eje det.
Kwanaki suna zuwa,’ in ji Ubangiji, ‘sa’ad da zan komo da mutanena Isra’ila da Yahuda daga bauta in kuma maido da su ga ƙasar da na ba wa kakanninsu mallaka,’ in ji Ubangiji.”
4 Og disse ere Ordene, som Herren talte til Israel og Juda:
Ga kalmomin Ubangiji da ya yi game da Isra’ila da Yahuda,
5 Thi saa siger Herren: Forfærdelses Røst have vi hørt; der er Skræk og ikke Fred.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Ana jin kukan tsoro, razana, ba salama ba.
6 Spørger dog og ser, om en Mand føder? hvorfor saa jeg hver Mand med sine Hænder paa sine Lænder som hun, der føder, og at alle Ansigter ere omskiftede til Bleghed?
Ku tambaya ku ji. Namiji zai iya haifi’ya’ya? To, me ya sa kuke ganin kowane mai ƙarfi da hannuwansa a kwankwaso kamar mace mai naƙuda, kowace fuska ta koma fari?
7 Ve! thi stor er denne Dag, saa den er uden Lige; og det er en Trængsels Tid for Jakob; dog skal han blive frelst derfra.
Kaito, gama wannan rana za tă zama mai girma! Babu kamar ta. Zai zama lokacin wahala wa Yaƙub, amma za a cece shi daga cikinta.
8 Og det skal ske paa den Dag, siger den Herre Zebaoth, at jeg vil bryde hans Aag af din Hals og sønderrive dine Baand; og de fremmede skulle ikke ydermere bringe dem til at tjene sig.
“‘A wannan rana,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘Zan karya karkiya daga wuyansu zan kuma cire musu kangi; baƙi ba za su ƙara bautar da su ba.
9 Men de skulle tjene Herren deres Gud og David deres Konge, som jeg vil oprejse dem.
A maimakon haka, za su bauta wa Ubangiji Allahnsu Dawuda sarkinsu kuwa, wanda na tayar musu.
10 Frygt da ikke, du min Tjener Jakob! siger Herren, og vær ikke forfærdet, Israel! thi se, jeg frier dig ud fra et langt fraliggende Land og din Sæd ud fra deres Fangenskabs Land; og Jakob skal komme tilbage og bo rolig og tryg, og ingen skal forfærde ham.
“‘Saboda haka kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana; kada ka karai, ya Isra’ila,’ in ji Ubangiji. ‘Tabbatacce zan cece ka daga wuri mai nesa, zuriyarka daga ƙasar zaman bautansu. Yaƙub zai sami salama da zaman lafiya, kuma ba wanda zai sa ya ji tsoro.
11 Thi jeg er med dig, siger Herren, for at frelse dig, thi jeg vil lade det tage en Ende med alle de Folkeslag, iblandt hvilke jeg adspredte dig; kun med dig vil jeg ikke lade det tage Ende, men jeg vil tugte dig med Maade og ikke lade dig slippe aldeles fri.
Ina tare da kai zan kuma cece ka,’ in ji Ubangiji. ‘Ko da yake na hallakar da dukan al’umma gaba ɗaya a inda na warwatsa ku, ba zan hallaka ku gaba ɗaya ba. Zan hore ku amma da adalci kaɗai; ba zan ƙyale ku ku tafi gaba ɗaya ba hukunci ba.’
12 Thi saa siger Herren: Svart er dit Brud, ondartet dit Saar.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Mikinku marar warkewa ne, raunin da kuka ji ya sha ƙarfin warkarwa.
13 Ingen tager sig af din Sag til Helbredelse; der er ingen Lægedom, ingen Forbinding for dig.
Babu wanda zai yi roƙo saboda damuwarku, ba magani domin mikinku babu warkarwa dominku.
14 Alle dine Elskere have glemt dig, de søge dig ikke; thi jeg har slaget dig, ligesom man slaar en Fjende, med en svar Tugtelse, fordi dine Misgerninger ere mangfoldige, fordi dine Synder ere talrige.
Dukan abokanku sun manta da ku; ba su ƙara kulawa da ku. Na buge ku kamar yadda abokin gāba zai yi na kuma hukunta ku yadda mai mugunta zai yi, domin laifinku da girma yake zunubanku kuma da yawa suke.
15 Hvorfor raaber du over dit Brud, at din Pine er saa svar? fordi dine Misgerninger ere mangfoldige, fordi dine Synder ere talrige, har jeg gjort disse Ting ved dig.
Me ya sa kuke kuka a kan mikinku, wahalarku da ba ta da magani? Domin laifinku da girma yake da kuma zunubanku masu yawa na yi muku waɗannan abubuwa.
16 Derfor skulle alle, som fortære dig, blive fortærede, og alle dine Modstandere skulle alle sammen gaa i Fangenskab; og de, som udplyndrede dig, skulle udplyndres, og alle dem, som berøvede dig, vil jeg give hen til Rov.
“‘Amma duk wanda ya cinye ku za a cinye shi; dukan abokan gābanku za su tafi zaman bauta. Waɗanda suka washe ku su ma za a washe su; dukan waɗanda suka mai da ku ganima su ma zan mai da su ganima.
17 Thi jeg vil lade din Helbredelse tage til og læge dig for dine Saar, siger Herren; thi de kaldte dig den fordrevne, de sagde: Det er Zion, ingen spørger efter hende.
Amma zan mayar muku da lafiya in kuma warkar da mikinku,’ in ji Ubangiji, ‘domin ana ce da ku yasassu, Sihiyona wadda ba wanda ya kula da ita.’
18 Saa siger Herren: Se, jeg vil omvende Fangenskabet for Jakobs Telte og forbarme mig over hans Boliger; og Staden skal bygges paa sin Høj, og der skal blive Palads efter sin Vis.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Zan mayar da wadatar tentin Yaƙub in kuma ji tausayin wuraren zamansa; za a sāke gina birnin a kufansa, fadar kuwa za tă tsaya a wurin da ya dace da ita.
19 Og Taksigelse og de legendes Røst skal udgaa fra dem; thi jeg vil formere dem, og de skulle ikke formindskes, og jeg vil ære dem, og de skulle ikke blive ringe.
Daga gare su waƙoƙi za su fito na godiya da kuma sowa ta farin ciki. Zan riɓaɓɓanya su, ba za su kuwa ragu ba; zan kawo musu ɗaukaka, ba kuwa za a ƙasƙanta su ba.
20 Og hans Sønner skulle vorde som fordum, og hans Menighed skal befæstes for mit Ansigt, og jeg vil hjemsøge alle dem, som fortrykke ham.
’Ya’yansu za su kasance kamar a kwanakin dā jama’arsu kuma za su kahu a gabana; zan hukunta duk wanda ya zalunce su.
21 Og hans Fyrste skal nedstamme fra ham selv, og hans Hersker skal udgaa fra hans Midte, og ham vil jeg lade nærme sig, og han skal komme nær til mig; thi hvo er ellers den, som har sat sit Hjerte i Borgen for at komme nær til mig? siger Herren.
Shugabansu zai zama ɗaya daga cikinsu; mai mulkinsu zai taso daga cikinsu. Zan kawo shi kusa zai kuma zo kusa da ni, gama wane ne zai miƙa kansa don yă yi kusa da ni?’ In ji Ubangiji.
22 Og I skulle være mit Folk, og jeg vil være eders Gud.
‘Saboda haka za ku zama mutanena, ni kuwa in zama Allahnku.’”
23 Se, en Herrens Storm, Fortørnelse, farer ud, og en hvirvlende Storm, den skal hvirvle over de ugudeliges Hoved.
Ga shi, hadarin Ubangiji zai fasu cikin hasala, iskar guguwa mai hurawa a kan kawunan mugaye.
24 Herrens brændende Vrede skal ikke vende om, førend han har udført, og førend han har fuldkommet sit Hjertes Tanker; i de sidste Dage skulle I faa Forstand derpaa.
Fushi mai zafi na Ubangiji ba zai kawu ba sai ya cika manufofin zuciyarsa gaba ɗaya. A kwanaki masu zuwa za ku gane wannan.

< Jeremias 30 >