< Jeremias 29 >

1 Og disse ere Ordene i det Brev, som Profeten Jeremias sendte fra Jerusalem til de øvrige af de Ældste, som vare bortførte, og til Præsterne og til Profeterne og til alt Folket, som Nebukadnezar havde bortført fra Jerusalem til Babel,
Ga abin da yake cikin wasiƙar annabi Irmiya da ya aika daga Urushalima zuwa ga sauran dattawan da suka ragu a cikin masu zaman bauta da kuma zuwa ga firistoci, annabawa da kuma dukan sauran mutanen da Nebukadnezzar ya kwashe zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon.
2 — efter at Kong Jekonias og Herskerinden og Hofmændene, Judas og Jerusalems Fyrster, og Tømmermændene og Smedene vare gangne ud af Jerusalem, —
(Wannan ya faru bayan Sarki Yekoniya da mahaifiyar sarauniya, shugabannin fada da kuma dukan shugabannin Yahuda da Urushalima, gwanayen sana’a da masu sassaƙa suka tafi zaman bauta daga Urushalima.)
3 ved Eleasas, Safans Søns, og Gemarias, Hilkias Søns, Haand, hvilke Zedekias, Judas Konge, sendte til Babel til Nebukadnezar, Kongen i Babel; det lød saaledes:
Ya ba da wasiƙar ta hannun Eleyasa ɗan Shafan da Gemariya ɗan Hilkiya, waɗanda Zedekiya sarkin Yahuda ya aika wurin Sarki Nebukadnezzar a Babilon. Wasiƙar ta ce,
4 Saa siger den Herre Zebaoth, Israels Gud, til alle de bortførte, som jeg har ladet bortføre fra Jerusalem til Babel:
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ga dukan waɗanda aka kwashe zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon.
5 Bygger Huse og bosætter eder, og planter Haver og æder deres Frugt!
“Ku gina gidaje ku zauna; ku dasa gonaki ku kuma ci abin da suka haifar.
6 Tager Hustruer og avler Sønner og Døtre, og tager Hustruer til eders Sønner og giver eders Døtre Mænd, at de maa føde Sønner og Døtre; og formerer eder der, og mindsker eder ikke!
Ku yi aure ku kuma haifi’ya’ya maza da mata; ku nemi mata wa’ya’yanku maza, ku kuma ba da’ya’yanku mata ga aure, saboda su ma za su haifi’ya’ya maza da mata. Ku riɓaɓɓanya a can, kada ku ragu.
7 Og søger den Stads Bedste, til hvilken jeg bortførte eder, og beder for den til Herren, thi naar den har Fred, saa have og I Fred.
Haka kuma, ku nemi zaman salama da cin gaba a birnin da aka kai ku zaman bauta. Ku yi addu’a ga Ubangiji saboda birnin, domin in ya ci gaba, ku ma za ku ci gaba.”
8 Thi saa siger den Herre Zebaoth, Israels Gud: Lader ikke eders Profeter, som ere midt iblandt eder, og eders Spaamænd bedrage eder, og hører ikke paa eders Drømme, som I komme til at drømme.
I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Kada ku bar annabawa da masu sihiri a cikinku su ruɗe ku. Kada ku saurari mafarkan da dā kuke ƙarfafa su su yi.
9 Thi de spaa Løgn for eder i mit Navn; jeg har ikke sendt dem, siger Herren.
Suna muku annabcin ƙarya da sunana. Ban aike su ba,” in ji Ubangiji.
10 Thi saa siger Herren: Naar halvfjerdsindstyve Aar ere forløbne for Babel, da vil jeg besøge eder ogstadfæste over eder mit gode Ord om at føre eder tilbage til dette Sted.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Sa’ad da shekaru saba’in suka cika a Babilon, zan zo muku in cika alkawarin alherina don in komo da ku zuwa wannan wuri.
11 Thi jeg kender de Tanker, som jeg tænker angaaende eder, siger Herren, Tanker om Fred og ikke om Ulykke, for at give eder en Fremtid og et Haab.
Gama na san shirye-shiryen da na yi muku,” in ji Ubangiji, “shirye-shiryen cin gaba ba na cutarwa ba, shirye-shiryen ba ku sa zuciya da kuma na nan gaba.
12 Og I skulle paakalde mig og gaa hen og bede til mig, og jeg vil høre eder.
Sa’an nan za ku kira gare ni ku zo ku kuma yi addu’a gare ni, zan kuwa ji ku.
13 Og I skulle søge og finde mig; thi I ville søge mig af eders ganske Hjerte.
Za ku neme ni ku kuwa same ni sa’ad da kuka neme ni da dukan zuciyarku.
14 Og jeg skal lade mig finde af eder, siger Herren, og omvende eders Fangenskab og samle eder fra alle de Hedninger og fra alle de Steder, hvorhen jeg fordrev eder, siger Herren; og jeg skal lade eder komme tilbage til det Sted, hvorfra jeg bortførte eder.
Za ku same ni,” in ji Ubangiji, “zan kuma komo da ku daga bauta. Zan tattaro ku daga dukan al’ummai in sa ku inda na kore ku,” in ji Ubangiji, “zan kuma komo da ku zuwa wurin da na kwashe ku zuwa zaman bauta.”
15 Thi I have sagt: Herren har opvakt os Profeter i Babel;
Za ku iya ce, “Ubangiji ya tā da annabawa saboda mu a Babilon.”
16 men Herren har sagt saaledes om Kongen, som sidder paa Davids Trone, og om alt Folket, som bor i denne Stad, om eders Brødre, som ikke ere gangne ud med eder iblandt de bortførte,
Amma ga abin da Ubangiji yana cewa game da sarki, wanda yake zaune a kursiyin Dawuda da kuma dukan mutanen da suka ragu a wannan birni,’yan’uwanku waɗanda ba su tafi tare da ku zuwa zaman bauta ba.
17 ja, saaledes har den Herre Zebaoth sagt: Se, jeg sender Sværdet, Hungeren og Pesten over dem, og jeg vil gøre dem som de modbydelige Figener, der ikke kunde ædes, fordi de vare saa slette.
I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Zan aika da takobi, yunwa da annoba a kansu zan kuma sa su zama kamar ɓaure marar amfani da suka yi munin da ba a iya ci.
18 Og jeg vil forfølge dem med Sværdet, med Hungeren og med Pesten og gøre dem til en Gru for alle Riger paa Jorden, til Forbandelse og til Forfærdelse og til Spot og til Forhaanelse iblandt alle Hedningerne, hvorhen jeg har fordrevet dem;
Zan fafare su da takobi, yunwa da annoba zan kuma sa su zama abin ƙyama ga dukan mulkokin duniya da kuma abin la’ana da abin bantsoro, abin dariya da abin reni, a cikin dukan al’umman da aka kore su zuwa.
19 fordi de ikke hørte paa mine Ord, siger Herren, jeg, som sendte mine Tjenere, Profeterne, til dem tidligt og ideligt, uden at de hørte mig, siger Herren.
Gama ba su saurari maganata ba,” in ji Ubangiji, “maganar da na aika gare su sau da sau ta bayina annabawa. Ku kuma masu zaman bauta ba ku saurara ba,” in ji Ubangiji.
20 Men I, hører Herrens Ord, alle I bortførte, hvilke jeg sendte fra Jerusalem til Babel!
Saboda haka, ku ji maganar Ubangiji, dukanku masu zaman bauta waɗanda na aika daga Urushalima zuwa Babilon.
21 Saa siger den Herre Zebaoth, Israels Gud, om Akab, Kolajas Søn, og om Zedekias, Maasejas Søn, som spaa eder Løgn i mit Navn: Se, jeg giver dem i Nebukadnezar, Kongen af Babels Haand, og han skal dræbe dem for eders Øjne.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa game da Ahab ɗan Kolahiya da Zedekiya ɗan Ma’asehiya, waɗanda suke muku annabcin ƙarya da sunana. “Zan ba da su ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai kuwa kashe su a gaban idanunku.
22 Og der skal fra dem optages en Forbandelse iblandt alle de bortførte af Juda, som ere i Babel, idet man skal sige: Herren gøre dig som Zedekias og som Akab! hvilke Kongen af Babel stegte ved Ild,
Saboda su, dukan masu zaman bauta daga Yahuda waɗanda suke a Babilon za su yi amfani da wannan la’ana cewa, ‘Ubangiji ka yi da mu kamar Zedekiya da Ahab waɗanda sarkin Babilon ya ƙone da wuta.’
23 fordi de gjorde en Daarskab i Israel og bedreve Hor med deres Næstes Hustruer og i mit Navn talte løgnagtige Ord, hvilke jeg ikke havde befalet dem; jeg ved det og vidner det, siger Herren.
Gama sun aikata munanan abubuwa a Isra’ila; sun yi zina da matan maƙwabtansu kuma da sunana suka yi ƙarya, waɗanda ban faɗa musu su yi ba. Na san wannan kuma ni shaida ne ga haka,” in ji Ubangiji.
24 Og om Semaja, Nekelamiten, skal du sige saaledes:
Faɗa wa Shemahiya mutumin Nehelam,
25 Saa siger den Herre Zebaoth, Israels Gud: Fordi du sendte Breve i dit Navn til alt Folket, som er i Jerusalem, og til Præsten Zefanja, Maasejas Søn, og til alle Præsterne saa lydende:
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka aika da wasiƙu da sunanka ga dukan mutane a Urushalima, zuwa ga Zefaniya ɗan Ma’asehiya firist da kuma ga sauran firistoci. Ka ce wa Zefaniya,
26 Herren har sat dig til Præst i Præsten Jojadas Sted, for at der maa være Opsynsmænd i Herrens Hus over hver Mand, som raser, og som spaar, at du kan lægge dem i Blok og Baand:
‘Ubangiji ya naɗa ka firist a wurin Yehohiyada don ka lura da gidan Ubangiji; ya kamata ka sa kowane mahaukaci wanda yake yi kamar annabi cikin turu da kuma a kangi.
27 Hvorfor har du da nu ikke truet Jeremias fra Anathoth, som spaar for eder?
To, me ya sa ba ka tsawata wa Irmiya daga Anatot, wanda yana ɗauka kansa annabi a cikinku ba?
28 thi derfor har han sendt Bud til os til Babel og sagt: Det vil vare længe; bygger Huse og bosætter eder, og planter Haver og æder deres Frugt — —
Ya aiko mana da saƙonsa a Babilon cewa zai ɗauki lokaci ƙwarai. Saboda haka ku gina gidaje ku zauna; ku dasa gonaki ku kuma ci abin da suka haifar.’”
29 Og Præsten Zefanja læste dette Brev for Profeten Jeremias's Øren.
Zefaniya firist kuwa, ya karanta wasiƙar annabi Irmiya.
30 Og Herrens Ord kom til Jeremias saalunde:
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
31 Send Bud til alle de bortførte, og sig: Saa siger Herren om Nekelamiten Semaja: Fordi Semaja har spaaet for eder, skønt jeg ikke har sendt ham, og han har bragt eder til at forlade eder paa Løgn:
“Ka aika da wannan saƙo zuwa ga dukan masu zaman bauta cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa game da Shemahiya, mutumin Nehelam. Domin Shemahiya ya yi muku annabci, ko da yake ban aike shi ba, ya kuma sa kuka gaskata ƙarya,
32 Derfor, saa siger Herren: Se, jeg vil hjemsøge Nekelamiten Semaja og hans Afkom; han skal ikke have nogen, som skal bo midt iblandt dette Folk, og han skal ikke se det gode, som jeg vil gøre imod mit Folk, siger Herren; thi han har prædiket Frafald fra Herren.
ga abin da Ubangiji yana cewa, tabbatacce zan hukunta Shemahiya mutumin Nehelam da zuriyarsa. Ba zai kasance da wani da ya rage a cikin wannan mutane ba, ba kuwa zai ga abubuwa alherin da zan yi wa mutanena ba, in ji Ubangiji, domin ya yi wa’azin tawaye a kaina.’”

< Jeremias 29 >