< Jeremias 22 >
1 Saa sagde Herren: Gak ned til Judas Konges Hus, og tal der dette Ord,
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ka gangara zuwa fadan sarkin Yahuda ka yi shelar wannan saƙo a can ka ce,
2 og sig: Judas Konge, du, som sidder paa Davids Trone, hør Herrens Ord, du og dine Tjenere og dit Folk, som gaa ind ad disse Porte.
‘Ka ji maganar Ubangiji, ya sarkin Yahuda, kai da kake zaune kan gadon sarautar Dawuda, kai, da fadawanka da mutanenka waɗanda suke shiga ta waɗannan ƙofofi.
3 Saa siger Herren: Øver Ret og Retfærdighed, og redder den, som er bleven til Rov, af Voldsmandens Haand, og forfordeler ej den fremmede, den faderløse og Enken, og gører ikke Uret og udøser ikke uskyldigt Blod paa dette Sted!
Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka yi abin da yake gaskiya da kuma daidai. Ka kuɓutar da wannan da aka yi masa ƙwace daga hannun mai zaluntarsa. Kada ka yi abin da ba daidai ba ko ka cuci baƙo, maraya ko gwauruwa, kuma kada ka zub da jini marar laifi a wannan wuri.
4 Thi dersom I rettelig gøre efter dette Ord, da skal der ind ad dette Hus's Porte gaa Konger, som sidde i Davids Sted paa hans Trone, og som fare paa Vogne og paa Heste, han og hans Tjenere og hans Folk.
Gama in ka lura da bin waɗannan umarnai, to, sarakunan da suke zaune a gadon sarautar Dawuda za su shiga ta ƙofofin wannan fada, suna hawan kekunan yaƙi da dawakai, fadawansu da mutanensu suna musu rakiya.
5 Men dersom I ikke ville høre disse Ord, da har jeg svoret ved mig selv, siger Herren, at dette Hus skal blive til et øde Sted.
Amma in ba ku kiyaye waɗannan umarnai ba, in ji Ubangiji, na rantse da kaina cewa wannan fada za tă zama kufai.’”
6 Thi saa siger Herren om Judas Konges Hus: Du var mig som Gilead, som Libanons Top; men jeg skal sandelig gøre dig til en Ørk, til Stæder, som ikke bebos.
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da wannan fadar sarkin Yahuda, “Ko da yake kina kamar Gileyad a gare ni, kamar ƙwanƙolin Lebanon, tabbatacce zan maishe ki hamada, kamar garuruwan da ba mazauna.
7 Og jeg vil indvie Fordærvere, der skulle komme over dig, hver med sine Vaaben; og de skulle omhugge dine udvalgte Cedre og kaste dem paa Ilden.
Zan aika da mai hallakarwa a kanki, kowane mutum da makamansa, za su kuma yayyanka gumaguman al’ul na ki masu kyau su jefa su cikin wuta.
8 Og mange Hedninger skulle gaa forbi denne Stad, og de skulle sige hver til sin Næste: Hvorfor har Herren gjort saaledes ved denne store Stad?
“Mutane daga al’ummai da yawa za su ratsa cikin wannan birni su kuma tambayi juna suna cewa, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka da wannan babban birni?’
9 Og de skulle sige: Fordi de forlode Herrens, deres Guds, Pagt, og tilbade andre Guder og tjente dem.
Amsar kuwa za tă zama, ‘Domin sun keta alkawarin Ubangiji Allahnsu, suka yi sujada suka kuma bauta wa waɗansu alloli.’”
10 Græder ikke over den døde, og ynkes ikke over ham; græder bittert over den, som drager bort, thi han skal aldrig komme tilbage og se sit Fædreland.
Kada ku yi kuka domin sarkin da ya mutu ko ku yi makoki saboda rashinsa; a maimako, ku yi kuka mai zafi saboda wanda aka kai zaman bauta, domin ba zai ƙara dawowa ba ko ya ƙara ganin ƙasarsa ta haihuwa.
11 Thi saa har Herren sagt om Sallum, Judas Konge, Josias's Søn, som var Konge i Josias sin Faders Sted, og som drog ud fra dette Sted: Han skal ikke mere komme hid tilbage;
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da Shallum ɗan Yosiya, wanda ya gāji mahaifinsa a matsayin sarkin Yahuda amma bai bar wurin nan ba, “Ba zai ƙara dawowa ba.
12 men han skal dø paa det Sted, hvorhen de have bortført ham, og han skal ikke mere se dette Land.
Zai mutu a inda suka kai shi zaman bauta; ba zai ƙara ganin wannan ƙasa ba.”
13 Ve den, som bygger sit Hus med Uretfærdighed og sine Sale med Uret, ham, der lader sin Næste tjene for intet, og ikke giver ham hans Arbejdes Løn,
“Kaiton wanda ya gina gidansa ta hanyar rashin adalci, ɗakunansa na sama kuma ta hanyar rashin gaskiya, yana sa mutanen ƙasarsa suna aiki a banza ba ya biyansu wahalarsu.
14 ham, der siger: Jeg vil bygge mig et rummeligt Hus og luftige Sale; og som udhugger sig Vinduer og paneler det med Ceder og anstryger det med rødt.
Yana cewa, ‘Zan gina wa kaina babban fada da manyan ɗakuna.’ Ta haka sai ya yi musu manyan tagogi ya manne musu al’ul ya yi musu ado kuma da ruwan ja.
15 Skulde du være Konge, fordi du brammer med Ceder? har din Fader ikke spist og drukket og øvet Ret og Retfærdighed? da gik det ham vel.
“Wannan zai mai da kai sarki ne in kana da al’ul a kai a kai? Mahaifinka bai kasance da abinci da abin sha ba? Ya yi abin da yake gaskiya da kuma daidai saboda haka kome ya kasance da lafiya da shi.
16 Han antog sig den elendiges og den fattiges Sag, da gik det vel til; er dette ikke „at kende mig?‟ siger Herren.
Ya kāre muradin matalauta da mabukata, ta haka kome ya tafi masa daidai. Ba abin da ake nufi da ba san ni ke nan ba?” In ji Ubangiji.
17 Men dine Øjne og dit Hjerte ere ikke til andet end til din Vinding og til at udøse uskyldigt Blod og til at øve Vold og Undertrykkelse.
“Amma idanunka da zuciyarka sun kahu kawai a kan ƙazamar riba, da a kan zub da jinin marar laifi da kuma a kan danniya da zalunci.”
18 Derfor, saa siger Herren om Jojakim, Josias's Søn, Kongen i Juda: De skulle ikke sørge over ham, og sige: Ak, min Broder! og ak, Søster! de skulle ikke sørge over ham og sige: Ak, Herre! og ak, hans Herlighed!
Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa game da Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, “Ba za su yi kuka dominsa ba, ‘Kaito, ɗan’uwana! Kaito,’yar’uwata!’ Ba za su yi kuka dominsa ba, ‘Kaito, maigidana! Kaito, darajarsa!’
19 Han skal begraves som et Asen begraves; man skal slæbe ham bort og kaste ham hen, langt uden for Jerusalems Porte.
Za a binne shi kamar jaki za a ja shi a ƙasa a jefar a bayan ƙofofin Urushalima.”
20 Stig op paa Libanon og raab, og opløft din Røst i Basan og raab fra Abarim! thi alle dine Elskere ere knuste.
“Ka haura zuwa Lebanon ka yi kuka, bari a ji muryarka a Bashan, yi kuka daga Abarim, gama an murƙushe dukan abokanka.
21 Jeg talte til dig i din Tryghed, men du sagde: Jeg vil ikke høre; dette har været din Vej fra din Ungdom af, at du ikke har villet høre paa min Røst.
Na ja maka kunne sa’ad da kake zama lafiya, amma sai ka ce, ‘Ba zan saurara ba!’ Wannan halinka ne tun kana matashi; ba ka yi mini biyayya ba.
22 Alle dine Hyrder skal Vejret fortære, og dine Elskere skulle vandre i Fangenskab; thi da skal du beskæmmes og blive til Skamme for al din Ondskabs Skyld.
Iska za tă koro dukan makiyayanka abokanka kuma za su tafi zaman bauta. Sa’an nan za ka sha kunya a kuma walaƙanta ka saboda dukan muguntarka.
23 Du, som bor paa Libanon og bygger Rede i Cedrene, hvor vil du finde Medynk, naar Smerter komme paa dig, Pine som hendes, der føder?
Kai da kake zama a ‘Lebanon,’ kai da kake sheƙa a gine-ginen al’ul za ka yi nishi sa’ad da zafi ya auka maka, zafi kamar na mace mai naƙuda!
24 Saa sandt jeg lever, siger Herren, var end Konias, Jojakims, Judas Konges Søn, en Signetring paa min højre Haand, saa vilde jeg dog rive dig bort derfra.
“Muddin ina raye,” in ji Ubangiji, “ko kai, Yehohiyacin ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda, ka zama zoben hatimin dama a hannuna na dama, zan kwaɓe ka.
25 Og jeg vil give dig i deres Haand, som tragte efter dit Liv, og i deres Haand, for hvis Ansigt du gruer, og i Nebukadnezar, Kongen af Babels Haand og i Kaldæernes Haand.
Zan ba da kai ga waɗanda suke neman ranka, waɗanda kake tsoro, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da kuma ga Babiloniyawa.
26 Og jeg vil kaste dig og din Moder, som dig fødte, ud i et andet Land, hvor I ikke ere fødte, og der skulle I dø.
Zan jefar da kai da mahaifiyar da ta haife ka zuwa wata ƙasa, inda babu ɗayanku da aka haifa a wurin, a can kuma za ka mutu.
27 Men til det Land, hvorhen deres Sjæl længes efter at komme tilbage, derhen skulle de ikke komme tilbage.
Ba za ka ƙara dawo ƙasar da kake marmarin dawowa ba.”
28 Mon denne Mand, Konias, er et foragtet, sønderslaaet Billede? mon han er et Kar, som ingen har Lyst til? hvorfor ere de bortkastede, han og hans Sæd, ja, henkastede i et Land, som de ikke kende?
Wannan mutum Yehohiyacin ne da aka rena, fasasshen tukunya, abin da babu wanda yake so? Me ya sa za a jefar da shi da’ya’yansa a jefar da su a ƙasar da ba su sani ba?
29 Land! Land! Land! hør Herrens Ord!
Ya ke ƙasa, ƙasa, ƙasa, ki ji maganar Ubangiji!
30 Saa siger Herren: Indtegner denne Mand som barnløs som en Mand, der ikke skal have Lykke i sine Dage; thi ingen af hans Sæd skal have Lykke ved at sidde paa Davids Trone og herske fremdeles i Juda.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ka rabu da wannan mutum sai ka ce marar’ya’ya, mutumin da ba zai yi nasara a rayuwarsa ba, gama babu zuriyarsa da za tă yi nasara babu wani da zai zauna a kursiyin Dawuda ko ya ƙara yin mulkin Yahuda.”