< Jeremias 18 >
1 Det Ord, som kom til Jeremias fra Herren, saalydende:
Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji.
2 Staa op og gaa ned til Pottemagerens Hus, og der vil jeg lade dig høre mine Ord.
“Ka gangara zuwa gidan mai ginin tukwane, a can zan ba ka saƙona.”
3 Og jeg gik ned til Pottemagerens Hus, og se, han gjorde et Arbejde paa Skiven.
Sai na gangara zuwa gidan mai ginin tukwane, na gan shi yana aiki a na’urar ginin tukwanen.
4 Og naar det Kar, som han gjorde, mislykkedes, som det kan gaa med Leret i Pottemagerens Haand, saa begyndte han igen og gjorde et andet Kar deraf, saaledes som det var ret for Pottemagerens Øjne at gøre.
Amma tukunyar da yake ginawa ta lalace a hannuwansa, sai mai ginin tukwanen ya sāke gina wata tukunya dabam, yana gyara ta yadda ya ga dama.
5 Da kom Herrens Ord til mig saaledes:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
6 Mon jeg ikke kan gøre ved eder, Israels Hus, ligesom denne Pottemager? siger Herren; se, ligesom Leret er i Pottemagerens Haand, saaledes ere I, Israels Hus, i min Haand.
“Ya gidan Isra’ila, ashe, ba zan yi da ku yadda mai ginin tukwanen nan yake yi ba?” In ji Ubangiji. “Kamar yumɓu a hannun mai ginin tukwane, haka kuke a hannuna, ya gidan Isra’ila.
7 I eet Øjeblik taler jeg imod et Folk og imod et Rige, til at oprykke og til at ødelægge det;
A duk lokacin da na yi shela cewa za a tumɓuke, a kakkarya a kuma hallaka wata al’umma ko mulki,
8 men naar dette Folk, imod hvilket jeg har talt, omvender sig fra sin Ondskab, da skal jeg angre det onde, som jeg havde tænkt at gøre ved det.
in wannan al’ummar da na yi wa gargaɗi ta tuba daga muguntarta, sai in janye in kuma fasa kawo mata masifar da na yi niyya aukar mata.
9 Og i eet Øjeblik taler jeg om et Folk og om et Rige til at bygge og til at plante det;
In kuma wani lokaci na yi shela cewa za a gina wata al’umma ko mulki a kuma kafa ta,
10 men naar det gør, hvad der er ondt for mine Øjne, saa at det ikke hører min Røst, da skal jeg angre det gode, med hvilket jeg havde sagt at ville gøre vel imod det.
in ta yi mugunta a gabana ba tă kuwa yi mini biyayya ba, sai in janye alherin da na yi niyya in yi mata.
11 Og nu, sig dog til Judas Mænd og til Jerusalems Indbyggere: Saa siger Herren: Se, jeg bereder Ulykke over eder og udtænker et Anslag imod eder; vender dog om, hver fra sin onde Vej, og bedrer eders Veje og eders Idrætter!
“Yanzu fa, sai ka faɗa wa mutanen Yahuda da waɗanda suke zaune a Urushalima, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa ga shi! Ina shirya muku masifa ina ƙirƙiro dabara a kanku. Saboda haka ku juya daga mugayen hanyoyinku, kowannenku, ku canja hanyoyinku da kuma ayyukanku.’
12 Men de sige: Det er forgæves! thi vi ville vandre efter vore egne Tanker og gøre hver efter sit onde Hjertes Stivhed.
Amma za su amsa su ce, ‘Ba amfani. Za mu ci gaba da shirye-shiryenmu; kowannenmu zai bi taurin muguwar zuciyarsa.’”
13 Derfor, saa siger Herren: Spørger dog iblandt Hedningerne: „Hvo har hørt saadanne Ting?” Noget saare grueligt har Israels Jomfru begaaet.
Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku tattambaya a cikin al’ummai. Wa ya taɓa jin irin wannan abu? Budurwa Isra’ila ta yi mugun abu mafi banƙyama.
14 Mon Libanons Sne gaar bort fra Klippen paa Marken? eller mon de fremtrængende, friske, rindende Vande standse?
Dusar ƙanƙarar Lebanon ta taɓa rabuwa da kan duwatsun Lebanon? Ruwan mai sanyinsa daga rafuffukansa masu nesa sun taɓa daina gudu?
15 Dog mit Folk har glemt mig, de gøre Røgelse for, hvad der er Forfængelighed, og de bragtes til at snuble paa deres Veje og de evige Baner, saa at de gik ind paa Stier, paa en Vej, som ikke var banet,
Duk da haka mutanena sun manta da ni; sun ƙone turare wa gumaka marasa amfani, waɗanda suka sa su tuntuɓe a al’amuransu a hanyoyin dā. Sun sa suka yi tafiya a ɓarayin hanyoyi a hanyoyin da ba a gina ba.
16 til at gøre deres Land til en Gru, til en evig Spot; hver som gaar derover, gruer og ryster med sit Hoved.
Ƙasarsu za tă zama kufai, abin reni har abada; dukan waɗanda suka wuce za su yi mamaki su kaɗa kai.
17 Som Østenvejret vil jeg adsprede dem for Fjendens Ansigt; jeg vil vende Ryggen og ikke Ansigtet til dem paa deres Trængsels Dag.
Kamar iska daga gabas zan warwatsa su a gaban abokan gābansu; zan juya musu bayana, ba zan nuna musu fuskata ba a ranar masifarsu.”
18 Men de sagde: Kommer og lader os optænke Anslag imod Jeremias; thi Loven gaar ikke tabt for Præsten, eller Raadet for den vise, eller Ordet for Profeten; kommer og lader os slaa ham med Tungen, og lader os ikke give Agt paa noget af hans Ord!
Suka ce, “Zo mu shirya wa Irmiya maƙarƙashiya; gama koyarwar doka da firist ya yi ba za tă ɓace ba, haka ma shawara daga mai hikima da kuma magana daga annabawa. Saboda haka ku zo, mu fāɗa masa da harsunanmu kada mu saurari wani abin da zai faɗa.”
19 Herre! giv Agt paa mig, og hør deres Røst, som trætte imod mig.
Ka saurare ni, ya Ubangiji ka ji abin da masu zargina suke cewa!
20 Mon man skulde betale ondt for godt? thi de have gravet en Grav for min Sjæl; kom i Hu, hvorledes jeg har staaet for dit Ansigt for at tale godt for dem, for at bortvende din Vrede fra dem.
Ya kamata a sāka wa alheri da mugunta? Duk da haka sun haƙa mini rami. Ka tuna cewa na tsaya a gabanka na kuma yi magana a madadinsu don ka janye fushinka daga gare su.
21 Derfor giv deres Børn hen til Hungeren, og overlad dem i Sværdets Vold, og lad deres Hustruer blive barnløse og Enker og deres Mænd ihjelslagne ved Døden; lad deres unge Karle blive dræbte med Sværd i Krigen!
Saboda haka ka kawo wa’ya’yansu yunwa; ka miƙa su ga ikon takobi. Bari matansu su zama marasa’ya’ya da gwauraye; bari a kashe mazansu, a kuma kashe samarinsu da takobi a yaƙi.
22 Lad der høres Skrig fra deres Huse, naar du lader en Trop pludselig komme over dem; thi de grove en Grav for at fange mig og skjulte Snarer for mine Fødder.
Bari a ji kuka daga gidajensu sa’ad da ka kawo masu hari a kansu farat ɗaya, gama sun haƙa rami don su kama ni suka kuma kafa tarko wa ƙafafuna.
23 Men du, Herre! du ved alt deres Raad imod mig til Døden, son ikke deres Misgerning, og udslet ikke deres Synd for dit Ansigt; lad dem være nedstyrtede for dit Ansigt, handle med dem i din Vredes Tid!
Amma Ya Ubangiji, ka san duk maƙarƙashiyarsu, na neman su kashe ni. Kada ka gafarta musu laifofinsu ko ka shafe zunubansu daga gabanka. Bari a tumɓuke su a gabanka; ka yi da su sa’ad da kake fushi.