< Jeremias 17 >

1 Judas Synd er skreven med en Jerngriffel, med Æggen af en Demant; den er indgravet paa deres Hjertes Tavle og paa deres Altres Horn,
“An rubuta zunubin Yahuda da alƙalamin ƙarfe, an rubuta da tsinin dutse, a kan allunan zukatansu da kuma a kan ƙahonin bagadansu.
2 ligesom deres Børn ihukomme deres Altre og deres Astartebilleder, ved de grønne Træer, ved Højenes Toppe.
Har’ya’yansu ma sun tuna bagadansu da ginshiƙan Asheransu kusa da itatuwa masu duhuwa da kuma a kan tuddai masu tsayi.
3 Mit Bjerg paa Marken, dit Gods, ja, alt dit Liggendefæ vil jeg give hen til Rov, ja, dine Høje for Synden inden alle dine Landemærker.
Dutsena a ƙasar da dukiyarku na ƙasar da dukan arzikinku za a ba da su ganima, tare da masujadanku na kan tuddai, saboda zunubi ko’ina a ƙasarku.
4 Og du skal drage ud, og det ved din egen Skyld, fra din Arv, som jeg gav dig, og jeg vil gøre, at du skal tjene dine Fjender i et Land, som du ikke kender; thi I have optændt en Ild i min Vrede, den skal brænde evindelig.
Saboda laifinku za ku rasa gādon da na ba ku. Zan bautar da ku ga abokan gābanku a ƙasar da ba ku sani ba, domin kun husata ni, zai kuwa ci har abada.”
5 Saa siger Herren: Forbandet er den Mand, som forlader sig paa Mennesket og holder Kød for sin Arm, og hvis Hjerte viger fra Herren.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “La’ananne ne mutumin da yake dogara ga mutum, wanda ya dogara ga jiki don ƙarfi wanda kuma zuciyarsa ta juya wa Ubangiji baya.
6 Og han skal være som den enlige paa den øde Mark og skal ikke se, at der kommer godt; men han skal bo paa de forbrændte Steder i Ørken, i et Saltland, som ikke kan bebos.
Zai zama kamar ɗan kurmi a ƙasar da take kango; ba za su ga arziki sa’ad da ya zo ba. Za su zauna a busassun wuraren hamada, a cikin ƙasar gishiri inda ba kowa.
7 Velsignet den Mand, som forlader sig paa Herren, og hvis Tillid Herren er!
“Amma mai albarka ne mutumin da yake dogara ga Ubangiji, wanda ƙarfin halinsa yana daga Ubangiji.
8 Thi han skal være ligesom et Træ, plantet ved Vand, og som udskyder sine Rødder ved Bækken, og som ikke frygter, naar der kommer Hede, og hvis Blad skal være grønt, og som ikke hænger mat, naar et tørt Aar kommer, og ikke lader af at bære Frugt.
Za su zama kamar itacen da aka dasa kusa da ruwa wanda ya miƙa saiwoyinsa zuwa cikin rafi. Ba ya jin tsoro sa’ad da zafi ya zo; ganyayensa kullum kore suke. Ba shi da damuwa a shekarar fări ba ya taɓa fasa ba da’ya’ya.”
9 Hjertet er bedrageligt, mere end alle Ting, og det er sygt; hvo kan kende det?
Zuciya ta fi kome ruɗu ta fi ƙarfin warkewa. Wa zai iya gane ta?
10 Jeg Herren er den, som ransager Hjertet og prøver Nyrer, og det for at give hver efter sine Veje, efter sine Idrætters Frugt.
“Ni Ubangiji nakan bincike zuciya in gwada tunani, don in sāka wa kowane mutum bisa ga halinsa, bisa ga ayyukansa.”
11 Som en Agerhøne, der samler Æg, som den ikke selv har lagt, saaledes er den, som forhverver sig Rigdom, men ikke med Ret; han skal forlade den midt i sine Dage og være en Daare paa sit sidste.
Kamar makwarwar da ta kwanta a kan ƙwan da ba ita ta zuba ba haka yake da mutumin da ya sami arziki a hanyar da ba daidai ba. A tsakiyar rayuwarsa za su rabu da shi, a ƙarshe kuma zai zama wawa.
12 Herlighedens Trone, Højheden af Begyndelsen, var vor Helligdoms Sted.
Kursiyi mai daraja, da aka ɗaukaka tun daga farko, shi ne wuri mai tsarkinmu.
13 Israels Forhaabning, Herre! Alle, som forlade dig, skulle beskæmmes; de, som affalde fra dig, skulle skrives i Jorden, thi de forlode Herren, de levende Vandes Kilde.
Ya Ubangiji, sa zuciyar Isra’ila, duk waɗanda suka rabu da kai za su sha kunya. Waɗanda suka juya maka baya za a rubuta su a ƙura domin sun yashe Ubangiji, maɓulɓular ruwan rai.
14 Herre! læg mig, saa læges jeg; frels mig, saa frelses jeg; thi du er min Ros.
Ka warkar da ni, ya Ubangiji, zan kuwa warke; ka cece ni zan kuwa cetu, gama kai ne nake yabo.
15 Se, de sige til mig: Hvor er Herrens Ord? lad det dog komme!
Sun riƙa ce mini, “Ina maganar Ubangiji take? Bari tă cika yanzu!”
16 Men jeg søgte ikke at unddrage mig fra som Hyrde at følge dig, jeg har heller ikke begæret den smertelige Dag, du ved det; hvad der er udgaaet af mine Læber, det er for dit Ansigt.
Ban gudu zaman mai yin maka kiwo ba; ka sani ban marmarin ranan nan ta masifa ba. Abin da ya fito daga leɓunana kuwa, a bayyane suke gare ka.
17 Vær mig ikke til Forfærdelse; du er min Tilflugt paa Ulykkens Dag.
Kada ka zama mini abin razana; kai ne mafakata a ranar masifa.
18 Lad dem, som forfølge mig, beskæmmes, men lad ikke mig beskæmmes; lad dem forfærdes, men lad ikke mig forfærdes; lad Ulykkens Dag komme over dem, og slaa dem ned med et dobbelt Slag!
Bari masu tsananta mini su sha kunya, amma ka kiyaye ni daga shan kunya; bari su tsorata, amma ka kiyaye ni da razana. Ka kawo musu ranar masifa; ka hallaka su da hallaka riɓi biyu.
19 Saa sagde Herren til mig: Gak, og stil dig i Folkets Børns Port, igennem hvilken Judas Konger komme ind, og igennem hvilke de gaa ud, og i alle Jerusalems Porte!
Ga abin da Ubangiji ya ce mini, “Ka je ka tsaya a ƙofar mutane, inda sarakunan Yahuda sukan shiga su fita; ka tsaya kuma a dukan sauran ƙofofin Urushalima.
20 Og du skal sige til dem: Hører Herrens Ord, I Judas Konger og al Juda og alle Indbyggere i Jerusalem, I, som gaa ind ad disse Porte.
Ka ce musu, ‘Ku ji maganar Ubangiji, ku sarakunan Yahuda, da dukan mutanen Yahuda da dukan mazaunan Urushalima waɗanda suke bi ta waɗannan ƙofofi.
21 Saa siger Herren: Tager eder i Vare for eders Sjæles Skyld; og bærer ingen Byrde paa Sabbatens Dag, og fører den ikke ind ad Jerusalems Porte.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, ku yi hankali kada ku ɗauki kaya a ranar Asabbaci ko ku shigar da shi ta ƙofofin Urushalima.
22 Og I skulle ingen Byrde føre ud af eders Huse paa Sabbatens Dag, og I skulle intet Arbejde gøre; men I skulle helligholde Sabbatens Dag, som jeg bød eders Fædre.
Kada ku fitar da kayan gidajenku ko ku yi wani aiki a ranar Asabbaci mai tsarki, yadda na umarci kakanni-kakanninku.
23 Men de hørte ikke og laante ikke Øre, men forhærdede deres Nakke for ikke at høre og for ej at annamme Lære.
Duk da haka ba su saurara ba, ba su kuwa mai da hankali ba; suka taurare ba su kuwa saurara ko su karɓi horo ba.
24 Og det skal ske, dersom I høre mig, siger. Herren, saa I ikke føre nogen Byrde ind ad denne Stads Porte paa Sabbatens Dag, men derimod holde Sabbatens Dag hellig og ikke gøre noget Arbejde paa den:
Amma in kuka yi hankali kuka yi mini biyayya, in ji Ubangiji, ba ku kuwa shigar da kaya ta ƙofofi a ranar Asabbaci ba, amma kuka kiyaye ranar Asabbaci da tsarki ba tare da yin wani aiki a cikinta ba,
25 Da skal der ind ad denne Stads Porte komme Konger og Fyrster, som sidde paa Davids Trone, og som fare paa Vogne og paa Heste, de og deres Fyrster, Judas Mænd og Indbyggerne i Jerusalem; og denne Stad skal blive evindelig.
sa’an nan sarakuna da suke zama a kursiyin Dawuda za su shiga ta ƙofofin wannan birni tare da fadawansu. Su da fadawansu za su shiga a kan kekunan yaƙi da kuma a kan dawakai, mutanen Yahuda suna musu rakiya tare da waɗanda suke zaune a Urushalima, wannan birni kuwa za tă kasance da mazauna har abada.
26 Og de skulle komme fra Judas Stæder og fra Jerusalems Omegn og fra Benjamins Land og fra Lavlandet og fra Bjergene og fra Sydlandet, de, som bringe Brændoffer og Slagtoffer og Madoffer og Virak, og som bringe Takoffer frem til Herrens Hus.
Mutane za su zo daga garuruwan Yahuda da ƙauyukan kewaye da Urushalima, daga iyakar Benyamin da gindin tuddan yamma, daga ƙasar tudu da kuma Negeb, suna kawo hadayun ƙonawa da hadayun gari, sadakokin turare da na godiya zuwa gidan Ubangiji.
27 Men dersom I ikke høre mig om at helligholde Sabbatens Dag og om ikke at bære Byrder og gaa ind ad Portene i Jerusalem paa Sabbatens Dag, da vil jeg antænde en Ild i dens Porte, og den skal fortære Jerusalems Paladser og ikke udslukkes.
Amma in ba ku yi mini biyayya ba, ba ku kiyaye ranar Asabbaci da tsarki ba, kuka ɗauki wani kaya yayinda kuke shiga ƙofofin Urushalima a ranar Asabbaci, to, sai in cinna wa ƙofofin Urushalima wutar da ba a iya kashewa, tă cinye kagaranta.’”

< Jeremias 17 >