< Jeremias 10 >
1 Israels Hus! hører det Ord, som Herren taler over eder.
Ku ji abin da Ubangiji yana ce muku, ya gidan Isra’ila.
2 Saa siger Herren: Vænner eder ej til Hedningernes Vej, og forfærdes ikke for Himmelens Tegn; thi Hedningerne forfærdes for dem.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada ku koyi hanyoyin al’ummai ko ku razana game da alamun sararin sama, ko da yake al’ummai sun razana saboda su.
3 Thi Hedningernes Skikke ere idel Forfængelighed; thi man afhugger dertil et Træ af Skoven, det udarbejdes af en Mesters Hænder med Øksen.
Gama al’adun mutane banza ne; sukan yanke itace daga kurmi, sai mai sassaƙa yă sassaƙa shi da gizago.
4 Man smykker det med Sølv og med Guld; man fæster det med Søm og med Hammer, at det ikke vakler.
Sukan yi masa ado da azurfa da kuma zinariya; sukan ɗauki guduma su kafa shi da ƙusoshi, don kada yă fāɗi.
5 Som et Palmetræ, af drevet Arbejde, staa de, men kunne ikke tale, de maa bæres, thi de kunne ikke gaa; I skulle ikke frygte for dem, thi de kunne ikke gøre ondt, og der er heller ingen Magt hos dem til at gøre godt.
Kamar dodon gona cikin gonar kabewa, haka gumakansu ba sa iya magana; dole a yi ta ɗaukansu domin ba za su iya tafiya ba. Kada ku ji tsoronsu; ba za su iya yi wa wani lahani ba ba sa iya yin wani abin kirki.”
6 Der er ingen som du, o Herre! du er stor, og dit Navn er stort med Styrke.
Babu wani kamar ka, ya Ubangiji; kai mai girma ne, kuma sunanka yana da girma da kuma iko.
7 Hvo skulde ikke frygte dig, du Hedningernes Konge? thi dig tilkommer det; thi iblandt alle Hedningernes vise og i alt deres Rige er ingen som du.
Wane ne ba zai girmama ka ba, Ya Sarkin al’ummai? Tsoronka wajibi ne. A cikin dukan masu hikima na al’ummai kuma cikin dukan mulkokinsu, babu kamar ka.
8 Men de ere ufornuftige og handle daarligt tillige, Afgudernes Lærdom, den er Træ;
Dukansu marasa azanci ne wawaye; gumakan itacen banza ne suke koya musu.
9 hamret Sølv, der føres fra Tharsis, og Guld fra Ufas, et Værk af Mesteren og af Guldsmedens Hænder! deres Klæder ere af blaat uldent og Purpur, et Værk af Kunstnere ere de alle.
An kawo ƙeraren azurfa daga Tarshish zinariya kuma daga Ufaz. Abin da gwani da maƙerin zinariya suka yi sa’an nan aka yi masa ado da mulufi da shunayya dukan aikin gwanaye.
10 Men Gud Herren er Sandhed, han er den levende Gud og en evig Konge; Jorden bæver for hans Vrede, og Hedningerne kunne ikke udholde hans Fortørnelse.
Amma Ubangiji shi ne Allah na gaskiya; shi ne Allah mai rai, madawwamin sarki. Sa’ad da ya yi fushi, ƙasa takan girgiza; al’ummai ba sa iya jure da hasalarsa.
11 Saaledes skulle I sige til dem: De Guder, som ikke have skabt Himmelen og Jorden, de skulle forsvinde fra Jorden og under Himlene.
“Ka faɗa musu wannan, ‘Waɗannan alloli, waɗanda ba su yi sammai da ƙasa ba, za su hallaka daga duniya da kuma daga ƙarƙashin sammai.’”
12 Han er den, som skabte Jorden ved sin Kraft og beredte Jorderige ved sin Visdom og udbredte Himlene ved sin Forstand.
Amma Allah ya yi duniya ta wurin ikonsa; ya kafa duniya ta wurin hikimarsa ya shimfiɗa sammai ta wurin fahiminsa.
13 Naar Røsten lyder, ved hvilken han lader Vandenes Mangfoldighed komme i Himmelen, da lader han Dunster opstige fra det yderste af Jorden; han gør Lynene til Regn og fører Vejret ud af sine Gemmer.
Sa’ad da ya yi tsawa, ruwaye a cikin sammai sukan yi ƙugi; yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya. Yakan aiki walƙiya da ruwan sama ya fitar da iska daga gidajen ajiyarsa.
14 Hvert Menneske bliver ufornuftigt og uden Forstand, hver Guldsmed er beskæmmet for det udskaarne Billedes Skyld; thi hans støbte Billeder ere Bedrageri, og der er ikke Aand i dem.
Kowa marar azanci ne, marar ilimi; kowane maƙerin zinariya zai sha kunya saboda gumakansa. Siffofinsa ƙarya ne; ba su da numfashi a cikinsu.
15 De ere Forfængelighed, et bedragerisk Værk; til den Tid, naar de blive hjemsøgte, skulle de gaa til Grunde.
Su ba kome ba ne, aikin ruɗami ne; Sa’ad da hukuncinsu ya yi za su lalace.
16 Ikke som disse er Jakobs Del; thi han er den, som har dannet alle Ting, og Israel er hans Arvs Stamme; Herre Zebaoth er hans Navn.
Shi da yake Rabon Yaƙub ba kamar waɗannan yake ba, gama shi ne Mahaliccin abubuwa duka, har da Isra’ila, kabilar gādonsa Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
17 Sank dit Gods fra Landet, du, som bor i den belejrede Stad I
Ku tattara kayayyakinku don ku bar ƙasar, ku da kuke zaune a wurin da aka kewaye da yaƙi.
18 Thi saa siger Herren: Se, denne Gang vil jeg udslynge Landets Indbyggere, og jeg vil trænge dem, paa det de skulle finde det.
Gama haka Ubangiji ya faɗa, “A wannan lokaci zan jefar da waɗanda suke zaune a ƙasar; zan kawo damuwa a kansu domin a kama su.”
19 Ve mig for min Brøst! mit Saar er svart; men jeg siger: Dette er kun min Lidelse, og jeg vil bære den.
Tawa ta ƙare, saboda raunin da aka yi mini! Raunina ba mai warkewa ba ne! Duk da haka na ce wa kaina, “Wannan ciwona ne, dole kuma in jure da shi.”
20 Mit Paulun er ødelagt, og alle mine Teltsnore ere revne over; mine Børn ere udgangne fra mig, og de ere ikke mere til; ingen opslaar mere mit Paulun eller oprejser mit Telt.
An lalatar da tentina; dukan igiyoyinsa sun tsintsinke.’Ya’yana maza sun bar ni ba sa nan; ba wanda aka bari da zai kafa tentina ko ya kafa mini mafaka.
21 Thi Hyrderne ere ufornuftige og søge ikke Herren; derfor handle de ikke klogelig, og hele deres Hjord er adspredt.
Makiyaya marasa azanci ne kuma ba sa neman nufin Ubangiji; saboda haka ba sa nasara dukan garkensu kuwa ya watse.
22 Et Budskab høres, se, det kommer, og et stort Bulder fra Nordenland for at gøre Judas Stæder til en Ødelæggelse, til Dragers Bolig.
Ku saurara! Rahoto yana zuwa babban hargitsi daga ƙasar arewa! Zai mai da garuruwan Yahuda kufai, mazaunin diloli.
23 Jeg ved, Herre! at Menneskets Vej staar ikke til ham selv, at det ikke staar til ham, som vandrer, at han kan befæste sin Gang.
Na sani, ya Ubangiji, cewa ran mutum ba nasa ba ne; ba mutum ne yake kiyaye takawarsa ba.
24 Tugt mig, Herre! dog med Maade; ikke i din Vrede, at du ikke gør mig aldeles ringe.
Ka yi mini gyara, Ubangiji, amma fa da adalci kaɗai ba cikin fushinka ba, don kada ka wofinta ni.
25 Udøs din Harme over Hedninger, som ikke kende dig, og over Slægter, som ikke paakalde dit Navn; thi de have fortæret Jakob, ja, fortæret ham og tilintetgjort ham og ødelagt hans Bolig.
Ka zuba hasalarka a kan al’umman da ba su san ka ba, a kan mutanen da ba sa kira bisa sunanka. Gama sun cinye Yaƙub; sun cinye shi gaba ɗaya suka kuma lalace wurin zamansa.