< Jakob 2 >

1 Mine Brødre! Eders Tro paa vor Herre Jesus Kristus, den herliggjorte, være ikke forbunden med Persons Anseelse!
Ya ku 'yan'uwana, muddin kuna rike da bangaskiyar ku ga Ubangijinmu Yesu Almasihu, Ubangijin daukaka, kada ku nuna bambanci ga wadansu mutane.
2 Naar der nemlig kommer en Mand ind i eders Forsamling med Guldring paa Fingeren, i prægtig Klædning, men der ogsaa kommer en fattig ind i smudsig Klædning,
Idan wani mutum ya halarci taron ku da zobban zinariya da tufafi masu kyau, wani matalauci kuma ya shigo da tufafi marasa tsabta.
3 og I fæste Øjet paa den, som bærer den prægtige Klædning, og sige: Sæt du dig her paa den gode Plads, og I sige til den fattige: Staa du der eller sæt dig nede ved min Fodskammel:
Sa'adda kuka kula da mai tufafi masu kyau nan, har kuka ce masa, “Idan ka yarda ka zauna a nan wuri mai kyau,'' mataulacin nan kuwa kuka ce masa, “Kai ka tsaya daga can,” ko kuwa, “Zauna a nan kasa a gaba na,”
4 Ere I saa ikke komne i Strid med eder selv og blevne Dommere med slette Tanker?
Ashe ba kuna zartar da hukunci a tsakanin ku ba ke nan? Ba kun zama alkalai na mungayen tunani kenan ba?
5 Hører, mine elskede Brødre! Har Gud ikke udvalgt de for Verden fattige til at være rige i Tro og Arvinger til det Rige, som han har forjættet dem, der elske ham?
Ku saurara, ya 'yan'uwana kaunatattu, ashe, Allah bai zabi matalautan duniyar nan su zama mawadata cikin bangaskiya ba, su kuma zama magada a cikin mulkin nan da ya yi wa masu kaunar sa alkawari ba?
6 Men I have vanæret den fattige! Er det ikke de rige, som underkue eder, og er det ikke dem, som slæbe eder for Domstolene?
Amma, kun wulakanta matalauta! Ashe, ba masu arzikin ne suke matsa maku ba? Ba su ne kuwa suke jan ku zuwa gaban shari'a ba?
7 Er det ikke dem, som bespotte det skønne Navn, som er nævnet over eder?
Ba kuma sune ke sabon sunan nan mai girma da ake kiran ku da shi ba?
8 Ganske vist, dersom I opfylde den kongelige Lov efter Skriften: „Du skal elske din Næste som dig selv, ‟ gøre I ret;
Duk da haka, idan kuka cika muhimmiyar shari'ar da nassi ya ce, “Ka kaunaci makwabcin ka kamar kanka,” to, madalla.
9 men dersom I anse Personer, gøre I Synd og revses af Loven som Overtrædere.
Amma in kun nuna bambanci, kun yi zunubi kenan, shari'a ta same ku da laifin keta umarni.
10 Thi den, som holder hele Loven, men støder an i eet Stykke, er bleven skyldig i alle.
Duk wanda yake kiyaye dukan shari'a, amma ya yi tuntube a hanya daya kadai, ya sabi shari'a gaba daya ke nan.
11 Thi han, som sagde: „Du maa ikke bedrive Hor, ‟ sagde ogsaa: „Du maa ikke slaa ihjel.‟ Dersom du da ikke bedriver Hor, men slaar ihjel, da er du bleven en Lovens Overtræder.
Domin wanda ya ce, “Kada ka yi zina,” shi ne kuma ya ce, “Kada ka yi kisan kai.” Idan ba ka yi zina ba amma ka yi kisan kai, ai, ka zama mai taka shari'a kenan.
12 Taler saaledes og gører saaledes, som de, der skulle dømmes efter Frihedens Lov.
Saboda haka, ku yi magana ku kuma yi aiki kamar wadanda za a hukunta ta wurin 'yantacciyar shari'a.
13 Thi Dommen er ubarmhjertig imod den, som ikke har øvet Barmhjertighed; Barmhjertighed træder frimodigt op imod Dommen.
Gama hukunci yana zuwa ba tare da jinkai ba ga wadanda ba su nuna jinkai. Jinkai ya yi nasara a kan hukunci.
14 Hvad gavner det, mine Brødre! om nogen siger, han har Tro, men ikke har Gerninger? mon Troen kan frelse ham?
Ina amfanin haka, 'yan'uwana, idan wani ya ce yana da bangaskiya, kuma ba shi da ayyuka? Wannan bangaskiyar ba za ta cece shi ba, ko za ta iya?
15 Dersom en Broder eller Søster er nøgen og fattes den daglige Føde,
Misali, idan wani dan'uwa ko 'yar'uwa ba su da tufa mai kyau ko suna rashin abincin yini.
16 og en af eder siger til dem: Gaar bort i Fred, varmer eder og mætter eder, men I ikke give dem det, som hører til Legemets Nødtørft, hvad gavner det?
Misali, idan waninku kuma ya ce masu, “Ku tafi cikin salama, ku kasance da dumi ku koshi.” Idan baku ba su abubuwan da jiki ke bukata ba, ina amfanin wannnan?
17 Ligesaa er ogsaa Troen, dersom den ikke har Gerninger, død i sig selv.
Haka ma, bangaskiya ita kadai, ba tare da aikin da ya nuna ta ba, matacciya ce.
18 Men man vil sige: Du har Tro, Og jeg har Gerninger. Vis mig din Tro uden Gerningerne, og jeg vil af mine Gerninger vise dig Troen.
To, wani zai ce, “Ai, kai kana da bangaskiya, ni kuwa ina da ayyuka.” Nuna mani bangaskiyar ka ba tare da ayyuka ba, ni kuma in nuna maka bangaskiya ta ta wurin ayyuka na.
19 Du tror, at Gud er een; deri gør du ret; ogsaa de onde Aander tro det og skælve.
Ka gaskanta cewa Allah daya ne; ka yi daidai. Amma ko aljannu ma sun gaskata, kuma suna rawar jiki.
20 Men vil du vide, du tomme Menneske! at Troen uden Gerninger er unyttig?
Kana so ka sani, kai marar azanci, cewa bangaskiya ba tare da ayyuka ba banza ce?
21 Blev ikke vor Fader Abraham retfærdiggjort af Gerninger, da han ofrede sin Søn Isak paa Alteret?
Ba an baratar da Ibrahim mahaifinmu ta wurin ayyuka ba, sa'adda ya mika Ishaku dansa a bisa bagadi?
22 Du ser, at Troen virkede sammen med hans Gerninger, og ved Gerningerne blev Troen fuldkommet,
Ka gani, ashe, bangaskiyar sa ta yi aiki da ayyukan sa, kuma da cewa ta wurin ayyuka bangaskiyar sa ta ginu sosai.
23 og Skriften blev opfyldt, som siger: „Abraham troede Gud, og det blev regnet ham til Retfærdighed, ‟ og han blev kaldet Guds Ven.
Nassi kuma ya cika da ya ce, “Ibrahim ya gaskata Allah, aka kuma lisafta masa ita a matsayin adalci.” Aka kuma kira shi abokin Allah.
24 I se, at et Menneske retfærdiggøres af Gerninger, og ikke af Tro alene.
Kun ga, ta wurin ayyuka ne mutum yake samu baratarwa ba ta wurin bangaskiya kadai ba.
25 Ligesaa Skøgen Rahab, blev ikke ogsaa hun retfærdiggjort af Gerninger, da hun tog imod Sendebudene og lod dem slippe bort ad en anden Vej?
Ta wannan hanyar kuma, ba Rahab karuwar nan ta samu baratarwa ta wurin ayyuka, da ta marabci masu leken asirin nan ta fitar da su ta wata hanya dabam ba?
26 Thi ligesom Legemet er dødt uden Aand, saaledes er ogsaa Troen død uden Gerninger.
Kamar yadda jiki idan ba tare da ruhu ba matacce ne, haka kuma, bangaskiya ba tare da ayyuka ba matacciya ce.

< Jakob 2 >