< Esajas 9 >
1 Thi der skal ej være Mørke for det Land, hvor der nu er Trængsel; som han i den første Tid bragte Vanære over Sebulons Land og Nafthalis Land, saa skal han gøre det herligt paa det sidste, Landet ad Vejen ved Havet, paa hin Side Jordan, Hedningernes Galilæa.
Duk da haka, babu sauran baƙin ciki ga waɗanda suke shan azaba. Dā ya ƙasƙantar da ƙasar kabilan Zebulun da ƙasar Naftali, amma nan gaba zai girmama Galili na Al’ummai, ta hanyar teku wadda take ta Urdun.
2 Det Folk, som vandrede i Mørket, ser et stort Lys; over dem, som boede i Dødens Skygges Land, skinner et Lys.
Mutanen da suke tafiya cikin duhu sun ga babban haske; a kan waɗanda suke zama a ƙasar inuwar mutuwa haske ya haskaka.
3 Du formerer Folket, hvis Glæde du ikke havde gjort stor; de glæde sig for dit Ansigt, ligesom Glæden er om Høsten, ligesom man fryder sig, naar man uddeler Bytte.
Ka fadada al’umma ka kuma ƙara farin cikinsu; suna farin ciki a gabanka yadda mutane sukan yi murna a lokacin girbi, kamar yadda mutane sukan yi farin ciki sa’ad da suke raba ganima.
4 Thi dets Byrdes Aag og Kæppen over dets Ryg, dets Drivers Stav, har du sønderbrudt som paa Midians Dag;
Gama kamar yadda yake a kwanakin da aka ci Midiyan da yaƙi, kuka ji tsoro nauyin da ya nawaita musu, sandar da yake a kafaɗunsu, sandar masu zaluncinsu.
5 thi hver Krigsstøvle, som blev baaren i Stridstummelen, og Klæderne, som vare sølede i Blod, skulle opbrændes og blive Ildens Næring.
Kowane takalmin jarumin da aka yi amfani da shi a yaƙi da kuma kowane rigar da ka naɗe cikin jini zai kasance an ƙone shi zai kuma zama abin hura wuta.
6 Thi et Barn er os født, en Søn er os given, og Fyrstendømmet skal være paa hans Skulder, og hans Navn kaldes Under, Raadgiver, vældige Gud, Evigheds Fader, Fredsfyrste;
Gama a gare mu an haifa mana yaro, a gare mu an ba da ɗa, gwamnati za tă kasance a kafaɗarsa. Za a ce da shi Mashawarci Mai Banmamaki, Allah Maɗaukaki Uban Madawwami, Sarkin Salama.
7 for at Fyrstendømmet maa blive stort, og at der maa blive Fred uden Ende over Davids Trone og over hans Rige til at befæste det og til at opholde det ved Ret og Retfærdighed fra nu og indtil evig Tid; den Herre Zebaoths Nidkærhed skal gøre dette.
Game da girmar gwamnatinsa da salama babu iyaka. Zai gāji sarki Dawuda, yă yi mulki a matsayinsa, zai kafa mulkinsa a kan adalci da gaskiya, tun daga yanzu har zuwa ƙarshen zamani. Ubangiji Maɗaukaki ne ya yi niyyar aikata wannan duka.
8 Herren har sendt et Ord i Jakob, og det er faldet i Israel.
Ubangiji ya aika da saƙon gāba da Yaƙub; zai auka wa Isra’ila.
9 Og det hele Folk skal fornemme det, Efraim og Indbyggerne i Samaria, med deres Hovmodighed og Hjerters Stolthed; de sige:
Dukan mutane za su san shi, Efraim da mazaunan Samariya, waɗanda suke magana da fariya suna kuma ɗaga kai,
10 Teglstenene ere faldne, men vi ville bygge med hugne Sten; Morbærtræerne ere afhugne, men vi ville sætte Cedertræer i Stedet.
“Tubalai sun zube a ƙasa, amma za mu sāke gina su da dutse; an sassare itatuwan ɓaure, amma za mu maya su da al’ul.”
11 Og Herren skal ophøje Rezins Modstandere over ham, og han vil væbne hans Fjender.
Amma Ubangiji ya ƙarfafa maƙiyan Rezin gāba da su ya kuma ingiza abokan gāba.
12 Syrerne forfra og Filisterne bagfra fortærede Israel med fuld Mund. Med alt dette har hans Vrede ikke lagt sig, men hans Haand er endnu udrakt.
Arameyawa daga gabas da Filistiyawa daga yamma sun cinye Isra’ila da buɗaɗɗen baki. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
13 Og Folket har ikke omvendt sig til den, som slog det, og har ikke søgt den Herre Zebaoth.
Amma mutanen ba su juyo wurin wanda ya buge su ba, balle su nemi Ubangiji Maɗaukaki.
14 Derfor vil Herren afhugge af Israel Hoved og Hale, Palmegren og Siv, paa een Dag.
Saboda haka Ubangiji zai yanke Isra’ila kai da wutsiya, da reshen dabino da iwa a rana guda;
15 Den gamle og den ansete, han er Hovedet; men en Profet, som lærer Løgn, han er Halen.
dattawa da manyan mutane su ne kai, annabawa waɗanda suke koyar da ƙarairayi su ne wutsiya.
16 Og dette Folks Førere forføre det, og de iblandt det, som lade sig føre, opsluges.
Waɗanda suke jagorar wannan mutane suna ɓad da su, su ne waɗanda ake jagora aka sa suka kauce.
17 Derfor kan Herren ikke glæde sig over dets unge Karle og ej forbarme sig over dets faderløse og over dets Enker; thi hver af dem er vanhellig og handler ondt, og hver Mund taler Daarskab. Med alt dette har hans Vrede ikke lagt sig, men hans Haand er endnu udrakt.
Saboda haka Ubangiji ba zai ji daɗin matasa ba, ba kuwa zai ji tausayin marayu da gwauraye ba, gama kowa marar sanin Allah ne da kuma mugu, kowane baki yana faɗin mugayen maganganu. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
18 Thi Ugudelighed brænder som en Ild, der fortærer Torn og Tidsler og sætter Ild paa Skovens Tykninger, og de skulle hvirvle højt op i Røg.
Tabbatacce mugunta tana ƙuna kamar wuta; tana cin ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya, ta sa wuta a jeji mai itatuwa masu yawa, don yă yi murtuke hayaƙi har zuwa sama.
19 Landet er sat i Brand i den Herre Zebaoths Vrede; og Folket er som det, der fortæres af Ild, de spare ikke den ene den anden.
Ta wurin fushin Ubangiji Maɗaukaki ƙasar za tă ci wuta mutane kuma za su zama abin hura wutar, babu wanda zai ji tausayin ɗan’uwansa.
20 Og man snapper til højre og hungrer endda, og man æder om sig til venstre og mættes ej; de fortære hver sin Arms Kød:
A dama za su ci, amma su ci gaba da jin yunwa; a hagu za su ci, amma ba za su ƙoshi ba. Kowa zai mai da naman’ya’yansa abinci.
21 Manasse er imod Efraim og Efraim imod Manasse, begge med hverandre imod Juda. Med alt dette har hans Vrede ikke lagt sig, men hans Haand er endnu udrakt.
Manasse zai mai da Efraim abinci, Efraim kuma yă cinye Manasse; tare za su yi gāba da Yahuda. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.