< Esajas 8 >

1 Og Herren sagde til mig: Tag dig en stor Tavle og skriv derpaa med Menneskers Griffel: „Hurtigt Rov, hastigt Bytte”.
Ubangiji ya ce mini, “Ka ɗauki naɗaɗɗen littafi mai girma ka yi rubutu a kai da alƙalami kurum, Maher-Shalal-Hash-Baz.
2 Og jeg vil tage mig tilforladelige Vidner: Præsten Uria og Sakarias, Jeberekias Søn.
Zan kuma kira Uriya firist da Zakariya ɗan Yeberekiya su zama mini amintattun shaidu.”
3 Og jeg nærmede mig til Profetinden, og hun undfangede og fødte en Søn; og Herren sagde til mig: Kald hans Navn: Maher-Sjalal Kasj-Bas.
Sa’an nan na tafi na yi jima’i da annabiya, ta kuwa yi ciki ta haifi ɗa. Ubangiji kuma ya ce mini, “Raɗa masa suna, Maher-Shalal-Hash-Baz.
4 Thi førend Barnet forstaar at raabe: Min Fader og min Moder! skal man bortføre Damaskus's Gods og Samarias Bytte hen foran Kongen af Assyriens Ansigt.
Kafin yaron yă san yadda zai ce ‘Babana’ ko ‘Mamana,’ sarkin Assuriya zai kwashe arzikin Damaskus da ganimar Samariya.”
5 Og Herren blev endnu ved at tale til mig, sigende:
Ubangiji ya sāke yi mini magana ya ce,
6 Fordi dette Folk foragtede Siloas sagte rindende Vande, og der er Glæde over Rezin og Remalias Søn;
“Domin wannan jama’a ta ƙi natsattsen ruwan rafin Shilowa suka yi ta farin ciki a kan Rezin ɗan Remaliya,
7 se, derfor skal Herren lade Flodens mægtige og mange Vande, Kongen af Assyrien og al hans Herlighed komme over dem; og den skal stige over alle sine Strømme og gaa over alle sine Bredder.
saboda haka Ubangiji yana shirin yă kawo musu rigyawar ruwan Kogi, wato, sarkin Assuriya da dukan sojojinsa. Zai cika dukan gaɓoɓinsa, yă kuma malala har zuwa bakin kogi.
8 Og den skal bryde ind i Juda, skylle over og strømme over og naa til Halsen; og hans udbredte Vinger skulle fylde dit Land, o Immanuel! saa vidt, som det er.
Yă yi ta malala har zuwa cikin Yahuda, yă shafe ta, yana ratsa ta ciki har yă kai kafaɗa. Fikafikansa da ya buɗe za su rufe fāɗin ƙasarka, Ya Immanuwel!”
9 Slaar kun ned, I Folkefærd! I skulle dog sønderknuses; mærker med eders Øren, alle I, som ere i langt fraliggende Lande! omgjorder eder, I skulle dog blive sønderknuste, omgjorder eder, I skulle dog blive sønderknuste.
Ku yi kururuwar yaƙi, ku ƙasashe, ku kuma ji tsoro! Ku saurara, dukanku manisantan ƙasashe. Ku shirya don yaƙi, ku kuma ji tsoro!
10 Beslutter et Raad, det skal blive til intet; taler et Ord, det skal ikke bestaa; thi med os er Gud.
Ku ƙirƙiro dabarunku, amma ba za su yi nasara ba; ku ƙulla shirye-shiryenku, amma ba za su yi amfani ba, gama Allah yana tare da mu.
11 Thi saa sagde Herren til mig, der hans Haand greb mig, og han underviste mig, at jeg ikke skulde vandre paa dette Folks Vej, og sagde:
Ubangiji ya yi mini magana da hannunsa mai ƙarfi a kaina, yana yi mini gargaɗi kada in bi hanyar waɗannan mutane. Ya ce,
12 Kalder ikke Sammensværgelse, hvad dette Folk kalder Sammensværgelse, og frygter ikke, hvad det frygter, og forfærdes ikke!
“Kada ka kira wani abu makirci game da kome da waɗannan mutane suke kira makirci; kada ji tsoron abin da suke tsoro, kada kuma ka firgita game da shi.
13 Den Herre Zebaoth, han skal være eder hellig; og han skal være eders Frygt, og han skal være eders Forfærdelse.
Ubangiji Maɗaukaki shi ne za ka ɗauka a matsayi mai tsarki, shi ne wanda za ka ji tsoro, shi ne za ka yi rawar jiki a gabansa,
14 Og han skal være til en Helligdom, men og til en Anstødssten og til en Forargelsesklippe for Israels tvende Huse, til en Snare og til en Strikke for Jerusalems Indbyggere.
zai kuwa kasance a wuri mai tsarki; amma ga dukan gidajen Isra’ila zai zama dutsen da zai sa mutane su yi tuntuɓe dutse kuma da zai sa su fāɗi. Ga dukan mutanen Urushalima kuma zai zama tarko da raga.
15 Og mange skulle støde sig paa dem og falde og sønderbrydes og omsnæres og fanges.
Yawancinsu za su yi tuntuɓe; za su fāɗi a kuwa ragargaza su, za a sa musu tarko a kuma kama su.”
16 Bind Vidnesbyrdet til, forsegl Loven hos mine Disciple!
Ɗaura shaidar nan ta gargadi ka kuma yimƙe umarnin Allah a cikin almajiraina.
17 Og jeg vil bie efter Herren, han, som har skjult sit Ansigt for Jakobs Hus, og jeg vil forvente ham.
Zan saurari Ubangiji, wanda ya ɓoye fuskarsa daga gidan Yaƙub. Zan dogara gare shi.
18 Se, her er jeg og de Børn, som Herren har givet mig, til Tegn og Forbilleder i Israel fra den Herre Zebaoth, som bor paa Zions Bjerg.
Ga ni, da yaran da Ubangiji ya ba ni. Mu alamu ne da shaidu a cikin Isra’ila daga Ubangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a Dutsen Sihiyona.
19 Og naar de ville sige til eder: Søger til Spaakvinderne og til Tegnsudlæggerne, som hviske og mumle, da siger: Skal ikke et Folk søge til sin Gud? skal man søge til de døde for de levendes Skyld?
Sa’ad da mutane suka ce muku ku nemi shawarar’yan bori da masu sihiri, waɗanda suke shaƙe murya har ba a jin abin da suke faɗi, bai kamata mutane su nemi shawara daga Allahnsu ba? Me zai sa ku nemi shawara daga matattu a madadin masu rai?
20 „Til Loven og til Vidnesbyrdet!” — dersom de ikke tale saaledes, naar der ingen Morgenrøde er for dem,
Nemi umarnin Allah da kuma shaidar jan kunne. Duk wanda bai yi magana bisa ga wannan kalma ba, ba su da amfani.
21 da skulle de drage igennem Landet, haardt plagede og hungrige; og naar en hungrer, da skal han blive vred og bande sin Konge og sin Gud og vende sit Ansigt imod det høje;
Cikin matsuwa da yunwa, za su yi ta kai komo ko’ina a ƙasar; sa’ad da suka ji yunwa, za su yi fushi su tā da idanu sama, su zagi sarkinsu da Allahnsu.
22 og han skal se til Jorden, men se, der skal være Angest og Mørke, Trængsels Mørke, og i Mulm er han udstødt.
Sa’an nan za su zura wa ƙasa idanu, abin da za su gani kawai shi ne matsuwa da duhu da kuma abin banrazana, za a kuma jefa su cikin baƙin duhu.

< Esajas 8 >