< Esajas 6 >
1 Idet Aar, der Kong Usias døde, da saa jeg Herren sidde paa en høj og ophøjet Trone, og Slæbet af hans Klædebon fyldte Templet.
A shekarar da Sarki Uzziya ya mutu, na ga Ubangiji zaune a kan kujerar sarauta a sama cike da ɗaukaka, zatinsa ya cika haikali.
2 Seraferne stode over ham, hver af dem havde seks Vinger; med to skjulte hver sit Ansigt, og med to skjulte hver sine Fødder, og med to fløj de.
A bisansa akwai serafofi, kowanne yana da fikafikai shida. Fikafikai biyu sun rufe fuskokinsu, da biyu suka rufe ƙafafunsu, biyu kuma da su suke tashi.
3 Og den ene raabte til den anden og sagde: Hellig, hellig, hellig er den Herre Zebaoth; al Jorden er fuld af hans Ære.
Suna kiran juna, “Mai Tsarki, Mai Tsarki, Mai Tsarki! Ubangiji Maɗaukaki ne; duniya ta cika da ɗaukakarsa.”
4 Og Dørposterne med Dørtærsklerne bævede for den raabendes Røst, og Huset blev fuldt af Røg.
Da jin ƙarar muryoyinsu madogarai da madogaran ƙofa suka girgiza, haikali kuma ya cika da hayaƙi.
5 Da sagde jeg: Ve mig! thi jeg forgaar; thi jeg har urene Læber og bor midt iblandt et Folk, som har urene Læber; thi mine Øjne have set Kongen, den Herre Zebaoth.
Sai na tā da murya na ce, “Kaitona! Na shiga uku! Gama ni mutum ne mai leɓuna marar tsarki, kuma ina raye a cikin mutane masu leɓuna marasa tsarki, idanuna kuma sun ga Sarki, Ubangiji Maɗaukaki.”
6 Da fløj en af Seraferne til mig og havde i sin Haand en Glød, som han havde taget fra Alteret med en Tang.
Sai ɗaya daga cikin serafofin ya yi firiya zuwa wurina tare da garwashi mai wuta a hannunsa, wanda ya ɗiba da arautaki daga bagade.
7 Og han lod den røre ved min Mund og sagde: Se, denne har rørt ved dine Læber, og din Misgerning er bortvegen, og din Synd skal sones.
Da shi ne ya taɓa bakina ya ce, “Duba, wannan ya taɓa leɓunanka, yanzu fa an kawar da laifofinka, an kuma gafarta maka zunubanka.”
8 Og jeg hørte Herrens Røst, som sagde: Hvem skal jeg sende? og hvo vil gaa for os? da sagde jeg: Se, her er jeg, send mig!
Sa’an nan na ji muryar Ubangiji tana cewa, “Wa zan aika? Wa zai tafi mana?” Sai na ce, “Ga ni! Ka aike ni!”
9 Og han sagde: Gak hen, og du skal sige til dette Folk: Hører og hører, men forstaar ej! ser og ser, men indser ej!
Ya ce, “Je ka ka faɗa wa wannan mutane, “‘Kome yawan kasa kunne da za ku yi, ba za ku fahimta ba; Kome yawan dubar da za ku yi, ba za ku san abin da yake faruwa ba.’
10 Gør dette Folks Hjerte fedt, og gør deres Øren tunghørige, og tilstryg deres Øjne, at det ikke ser med sine Øjne og hører med sine Øren og forstaar med sit Hjerte, saa at det omvender sig og vorder lægt.
Ka sa zuciyar mutanen nan ta dushe; kunnuwansu su kurunce, idanunsu kuma su makance. In ba haka ba za su iya gani da idanunsu, su ji da kunnuwansu, su fahimta da zuciyarsu, su kuma juyo a kuma warkar da su.”
11 Men jeg sagde: Hvor længe, Herre? og han sagde: Indtil Stæderne blive øde, uden Indbyggere, og Husene uden Folk, og Landet aldeles ødelægges.
Sa’an nan na ce, “Har yaushe, ya Ubangiji?” Ya kuma amsa, “Sai an lalatar da biranen ba kowa a ciki, sai an mai da gidaje kangwaye ƙasa kuma ta zama kango ba amfani,
12 Og Herren har ført Folket langt bort, og Tomheden er bleven stor i Landet.
sai lokacin da Ubangiji ya kori kowa aka kuma yashe ƙasar gaba ɗaya.
13 Og bliver en Tiendepart endnu tilbage deri, saa skal denne atter være til at ødelægges; men ligesom der af Terebinten og Stenegen bliver en Stub tilbage, naar de ere fældede, saaledes skal denne Stub være en hellig Sæd.
Ko da yake kashi ɗaya bisa goma zai ragu a ƙasar, za tă sāke zama kango. Amma kamar yadda katambiri da itacen oak sukan bar kututturai sa’ad da aka yanke su, haka iri mai tsarkin nan zai zama kututture a ƙasar mai tsarki.”